Zinariya

Zinariya A kafafen sada zumunta gidan talabijin ɗin
Zinariya TV ya ke gabatar da ayyukan shi. Zinariya TV, Farin Cikin Al'umma
(1)

Sayyadi Ibrahim Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi kenan yake ɗawafin ban kwana a garin Makkah
29/05/2026

Sayyadi Ibrahim Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi kenan yake ɗawafin ban kwana a garin Makkah

Bello El-Rufa'i ya ziyarci Atiku Abubakar
29/05/2026

Bello El-Rufa'i ya ziyarci Atiku Abubakar

ZA'A FAFATA: Garkuwan Chindo ya rattaɓa hannu a kan Damben 200k Shida Ali kanin Bello a yau Juma'a za'a fafata Wa kuke f...
29/05/2026

ZA'A FAFATA: Garkuwan Chindo ya rattaɓa hannu a kan Damben 200k Shida Ali kanin Bello a yau Juma'a za'a fafata

Wa kuke fata ya samu nasara?

28/05/2026

Dunbun Al’ummah daga cikin ƙananan hukumomin Jos ta Arewa da Bassa sun kai wa Hon. Abubakar to Sadik Plaza, ɗan takarar kujerar Majalisar Tarayya ta Najeriya mai wakiltar mazabar Bassa/Jos ta Arewa, gaisuwar Babbar Sallah.

“Kefiano Ba Zai Samu Kashi 1% Na Ƙuri’u A Bassa/Jos North Ba” - Pasali Jigo a jam’iyyar APC a Jihar Filato, Hon. Khalifa...
28/05/2026

“Kefiano Ba Zai Samu Kashi 1% Na Ƙuri’u A Bassa/Jos North Ba” - Pasali

Jigo a jam’iyyar APC a Jihar Filato, Hon. Khalifa Pasali, ya bayyana cewa Kefas Wusgak Rotshik Kefiano ba zai iya samun ko kashi 1% na ƙuri’un al’umma a mazabar Bassa/Jos North ba, yana mai cewa mutane da dama a yankin ma ba su san jam’iyyar PDP ba.

Pasali ya bayyana haka ne yayin da yake magana kan siyasar Jihar Filato, inda ya ce al’ummar jihar har yanzu suna tsayin daka wajen goyon bayan Gwamna Caleb Mutfwang. Ya ƙara da cewa, da yardar Allah, gwamnan zai ci gaba da mulki har zuwa shekarar 2031.

Ya kuma bayyana cewa “Caleb daga Little Rayfield zuwa Presidential Villa,” yana nuna cikakken yakinin sa game da makomar siyasar gwamnan jihar.

Hakazalika, Pasali ya yi kira ga al’ummar Jihar Filato da su ci gaba da addu’o’i domin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jihar, musamman a wannan lokaci na bukukuwan Sallah.

Wani matashi mai basira a harkar zane mai suna Baba Na Kowa ya kai ziyara ga Hon. Ibrahim Mohammed Baba (IMBA), ɗan taka...
28/05/2026

Wani matashi mai basira a harkar zane mai suna Baba Na Kowa ya kai ziyara ga Hon. Ibrahim Mohammed Baba (IMBA), ɗan takarar Sanatan Bauchi ta Arewa na APC a 2027, tare da gabatar masa da hoton da ya zana domin nuna girmamawa da goyon baya.

Haske No Shaking

Madugun adawar siyasar Najeriya, Alh Atiku Abubakar ya ziyarci Rotimi Ameachi domin rarrashin shi bayan kayi da ya sha a...
28/05/2026

Madugun adawar siyasar Najeriya, Alh Atiku Abubakar ya ziyarci Rotimi Ameachi domin rarrashin shi bayan kayi da ya sha a zaɓen fidda gwani na jam'iyyar ADC

28/05/2026

Shirin “Zare da Abawa” tare da Hon. Anas Shehu Baba kan ayi Hakuri ayi Hon. Adamu Aliyu A Zabe mai zuwa na 2027 a Jam’iyyar APC a kujerar Majalisar Dokokin Jihar Plateau, mai wakiltar mazabar Jos North North.

DA ƊUMI-ƊUMI: Atiku ya lashe zaben fidda gwani na takarar shugaban Najeriya a jam'iyyar ADC.Wannan nasara ta tabbatar da...
27/05/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Atiku ya lashe zaben fidda gwani na takarar shugaban Najeriya a jam'iyyar ADC.

Wannan nasara ta tabbatar da cewa tsohon shugaban kasar Nigeriya Atiku Abubakar zai fafata da shugaba Tinubu a zaben Shekarar 2027.

Wa kuje fatan ya lashe zaben?

Bayan idar da Sallar Idi, Abba Kabir Yusuf ya ziyarci kabarin mahaifinsa domin yi mishi addu'a
27/05/2026

Bayan idar da Sallar Idi, Abba Kabir Yusuf ya ziyarci kabarin mahaifinsa domin yi mishi addu'a

Shamsudeen Bala Mohammed Ya Tallafawa Matasan Bauchi Da Miliyoyin Kuɗi Da Kuma Shanu Domin SallahƊan Gwamnan Jihar Bauch...
27/05/2026

Shamsudeen Bala Mohammed Ya Tallafawa Matasan Bauchi Da Miliyoyin Kuɗi Da Kuma Shanu Domin Sallah

Ɗan Gwamnan Jihar Bauchi, Shamsudeen Bala Mohammed, ya ci gaba da jawo yabo daga al’ummar jihar sakamakon irin tallafin da yake bai wa matasa da marasa ƙarfi musamman a wannan lokaci na bukukuwan Eid-el-Kabir.
A cikin kwanaki uku kacal, Shamsudeen Bala Mohammed ya rabawa matasa kuɗaɗe har naira miliyan hamsin da biyu domin tallafa musu wajen gudanar da harkokinsu da rage musu raɗaɗin matsin tattalin arziƙi.

Haka kuma, a yau ya ƙaddamar da rabon manyan shanu sama da ashirin da huɗu domin faranta ran matasa da sauran al’ummar Jihar Bauchi yayin shagulgulan Sallah, lamarin da ya kara nuna jajircewarsa wajen taimakon jama’a.

Wasu daga cikin matasan da s**a amfana da tallafin sun bayyana jin daɗinsu tare da yabawa wannan ƙoƙari, inda s**a ce irin wannan taimako na ƙara ƙarfafa musu guiwa da samar da walwala ga al’umma.

Al’umma da dama sun bayyana cewa wannan aiki abin a yaba ne kuma abin ƙarfafa guiwa ga masu hannu da shuni da sauran masu taimakon jama’a, tare da addu’ar Allah Ya ci gaba da yi wa Shamsudeen Bala Mohammed jagora da albarka a rayuwarsa.

Address

Abuja
Anglo Jos
80073

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zinariya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share