13/04/2026
SANARWA GA MANEMA LABARU
ICPC Ta Gurfanar da El-Rufai Kan Zarge-zarge Guda Tara, Ta Raba Shari’ar sa da ta Abokin Karar sa
Hukumar Yaki da Cin Hanci da Sauran Laifuka Masu Alaka (ICPC) ta gurfanar da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir Ahmad El-Rufai, a gaban Mai Shari’a Darius Khobo na Babbar Kotun Jihar Kaduna mai lamba 5, kan zarge-zarge guda tara da s**a shafi damfara da kuma karkatar da kudade.
Gurfanarwar, wadda aka yi a ranar Litinin, ta biyo bayan gyaran da lauyan mai gabatar da kara na Hukumar, Dr. Osuobeni Ekoi Akponimisingha, ya yi wa tuhumar tun farko, inda ya raba shari’ar Mallam El-Rufai da ta abokin karar sa, Amadu Sule.
Wannan gyara ya zama dole ne saboda rashin halartar wanda ake kara na biyu, Amadu Sule, wanda aka bayar da rahoton cewa ba zai iya zuwa kotu ba saboda matsalar rashin lafiya.
Bayan faruwar hakan, kotun ta amince da bukatar yin gyaran, wanda hakan ya bai wa masu gabatar da kara damar ci gaba da gurfanar da Mallam El-Rufai shi kadai ba tare da wanda ake kara na biyun ba.
Daga bisani aka karantawa Mallam El-Rufai sabbin tuhume-tuhume guda tara wadanda s**a yi zargin karya dokoki daban-daban karkashin Dokar ICPC ta shekarar 2000, Dokar Damfara da Sauran Laifuka Masu Alaka ta shekarar 2006, Kundin Dokar Hukunta Masu Laifi na Jihar Kaduna na shekarar 2017, da kuma Dokar Sayen Kayayyaki ta Jihar Kaduna ta shekarar 2017.
Bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, tsohon gwamnan na Jihar Kaduna ya bayyana cewa ba shi da laifi a dukkan zarge-zarge guda taran.
Lauyan masu gabatar da kara ya bukaci kotun da ta sanya ranar fara shari’a, sannan ta ba da umarnin da zai tabbatar da cewa wanda ake karar ya halarci zaman kotun a kowane lokaci.
Lauyan kariya, a nasa martanin, ya sanar da kotun cewa akwai wata bukata da s**a shigar, kuma ya nemi kotun da ta ba da belin wanda ake karar kan wasu sharuda masu sauki.
Bayan sauraron bangarorin biyu, kotun ta dage zaman zuwa ranar Talata, 14 ga watan Afrilu, 2026, domin yanke hukunci kan bukatar neman belin, sannan ta bayar da umarnin cewa Mallam El-Rufai ya ci gaba da kasancewa a hannun hukumar ICPC.
J. Okor Odey
Shugaban Sashen Yada Labarai da Sadarwa, ICPC.