Anka24 Tv Channel

Anka24 Tv Channel Anka24 Tv Domin Nishadantarwa fada Karwa da Ilmantarwa

JAM’IYAR PDP RESHEN KARAMAR HUKUMAR MULKI TA ANKA TA GUDANAR DA TARON KADDAMAR DA SHUWAGABANNIN PARTY MATAKIN GUNDUMA A ...
30/04/2026

JAM’IYAR PDP RESHEN KARAMAR HUKUMAR MULKI TA ANKA TA GUDANAR DA TARON KADDAMAR DA SHUWAGABANNIN PARTY MATAKIN GUNDUMA A YAU ALHAMIS 20/APRIL/2026

16/04/2026

GAMAYYAR KUNGIYOYIN GIDAN ZANNAN BUNGUDU DAKE GARIN ANKA SUNYI MUBA'AYI GA MAIGIRMA GWAMNA DAUDA LAWAL DARE.

ABI DOKA A ZAUNA LAFIYA HRH Dr Attahiru Muhammad Ahmad CON Emir of Zamfara
15/04/2026

ABI DOKA A ZAUNA LAFIYA
HRH Dr Attahiru Muhammad Ahmad CON Emir of Zamfara

ZANNAN SUPPORT GROUP ANKAGAMAYYAR KUNGIYOYIN GIDAN ZANNAN BUNGUDU DAKE GARIN ANKA SUNYI MUBA'AYI GA MAIGIRMA GWAMNA DAUD...
15/04/2026

ZANNAN SUPPORT GROUP ANKA

GAMAYYAR KUNGIYOYIN GIDAN ZANNAN BUNGUDU DAKE GARIN ANKA SUNYI MUBA'AYI GA MAIGIRMA GWAMNA DAUDA LAWAL DARE.

A wani mataki na tabbatar da umarnin Maigirma HON Dr Abdulmalik Zubairu Zannan Bungudu ga daukacin kungiyoyi da magoya bayansa dake kananan hukumomi goma-sha hudu na jihar Zamfara, gamayyar manyan kungiyoyin gidan Zannah guda (6) da s**a hada da:

1.Zannah Support Group.
2.Zannah Like-maind.
3.Zannah Solidarity.
4.Zannah Muke Fata.
5.Zannah Connect.
6.Zannah Trust.

Sun jaddada umarnin His-Excellency Hon.Dr. Abdulmalik Zubairu Bungudu na goyon bayan Maigirma Gwamna Dr. Dauda Lawal karo na biyu ta hannun wakilin Maigirma Gwamna Shugaban karamar hukumar mulkin Anka Hon bello tungar kuda kuku a dacin taro dake cikin sakatariyar karamar hukumar mulkin Anka

Da yake gabatar da jawabi amadadin dukkanin shuwagabannin kungiyoyin Hon. Shafii musa sarkin yamman anka da Malan Abdullahi Garba Anka sun bayyana cewa, daga yau duk wata hidima da ta shafi nasarar Maigirma Gwamna Dr Dauda lawal dare ashirye wadannan gamayyar kungiyoyi suke domin bada gudunmuwar su bisa umarnin mai girma Hon Dr Abdulmalik Zubairu Zannan Bungudu.

Shima da yake maida jawabi a wurin taron, Maigirma Mukaddashin Shugaban karamar hukumar mulki ta ank Hon bello tungar kuda kuku ya bayyana jindaɗinsa bisa wannan muba'ayi, tare da bayyana Zannan Bungudu amatsayin dan siyasa mai matukar anfanar da al-ummar jihar Zamfara, inda ya bada tabbacin yin aiki kafaɗa-da-kafaɗa da mutanen Zannah dake Karamar hukumar mulki ta anka

Taron ya samu halartar dukkanin shuwagabannin kungiyoyin da mambobin su, Wakilan Jam'iyyar APC, Dattawa, da sauran yan Jam'iyya Maza da mata, Allah (SWT) ya kara karfafa wannan tafiya ta Zannah, Allah ya taimaki Gwamnatin Zamfara da al-ummar Zamfara baki daya Allahumma Amin.

13/04/2026

Daga Fadar Mai Martaba Sarkin Zamfara Yayinda Dan Takarar Dan Majalisar Anka Da Kewaye Yakai Ziyarar Bangirma Tare Da Neman Addu’a Da Saka Albarka Daga Bakin Mai Martaba

SANARWA GA MANEMA LABARU ICPC Ta Gurfanar da El-Rufai Kan Zarge-zarge Guda Tara, Ta Raba Shari’ar sa da ta Abokin Karar ...
13/04/2026

SANARWA GA MANEMA LABARU

ICPC Ta Gurfanar da El-Rufai Kan Zarge-zarge Guda Tara, Ta Raba Shari’ar sa da ta Abokin Karar sa

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Sauran Laifuka Masu Alaka (ICPC) ta gurfanar da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir Ahmad El-Rufai, a gaban Mai Shari’a Darius Khobo na Babbar Kotun Jihar Kaduna mai lamba 5, kan zarge-zarge guda tara da s**a shafi damfara da kuma karkatar da kudade.

Gurfanarwar, wadda aka yi a ranar Litinin, ta biyo bayan gyaran da lauyan mai gabatar da kara na Hukumar, Dr. Osuobeni Ekoi Akponimisingha, ya yi wa tuhumar tun farko, inda ya raba shari’ar Mallam El-Rufai da ta abokin karar sa, Amadu Sule.

Wannan gyara ya zama dole ne saboda rashin halartar wanda ake kara na biyu, Amadu Sule, wanda aka bayar da rahoton cewa ba zai iya zuwa kotu ba saboda matsalar rashin lafiya.

Bayan faruwar hakan, kotun ta amince da bukatar yin gyaran, wanda hakan ya bai wa masu gabatar da kara damar ci gaba da gurfanar da Mallam El-Rufai shi kadai ba tare da wanda ake kara na biyun ba.

Daga bisani aka karantawa Mallam El-Rufai sabbin tuhume-tuhume guda tara wadanda s**a yi zargin karya dokoki daban-daban karkashin Dokar ICPC ta shekarar 2000, Dokar Damfara da Sauran Laifuka Masu Alaka ta shekarar 2006, Kundin Dokar Hukunta Masu Laifi na Jihar Kaduna na shekarar 2017, da kuma Dokar Sayen Kayayyaki ta Jihar Kaduna ta shekarar 2017.

Bayan an karanta masa tuhume-tuhumen, tsohon gwamnan na Jihar Kaduna ya bayyana cewa ba shi da laifi a dukkan zarge-zarge guda taran.

Lauyan masu gabatar da kara ya bukaci kotun da ta sanya ranar fara shari’a, sannan ta ba da umarnin da zai tabbatar da cewa wanda ake karar ya halarci zaman kotun a kowane lokaci.

Lauyan kariya, a nasa martanin, ya sanar da kotun cewa akwai wata bukata da s**a shigar, kuma ya nemi kotun da ta ba da belin wanda ake karar kan wasu sharuda masu sauki.

Bayan sauraron bangarorin biyu, kotun ta dage zaman zuwa ranar Talata, 14 ga watan Afrilu, 2026, domin yanke hukunci kan bukatar neman belin, sannan ta bayar da umarnin cewa Mallam El-Rufai ya ci gaba da kasancewa a hannun hukumar ICPC.

J. Okor Odey
Shugaban Sashen Yada Labarai da Sadarwa, ICPC.

Zaku Iya Gasgata Wannan Magana Ta Chairman Anka Hon Bashar Katuka
13/04/2026

Zaku Iya Gasgata Wannan Magana Ta Chairman Anka Hon Bashar Katuka

Address

Anka, Magaji Ward
Anka

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Anka24 Tv Channel posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Anka24 Tv Channel:

Share