Kabawan Kanta Fm Radio

Kabawan Kanta Fm Radio Kabawan Kanta Fm Radio Na Maraba Da Kowa Domin Kawo Muku Labarai Fadakarwa, Ilmantarwa,Nishadantarwa

CONGRATULATIONSALLAH YA KARO ILMI MAI YAWA DA ALBARKA MALAM MUDASSIR AMEEN.
12/08/2026

CONGRATULATIONS
ALLAH YA KARO ILMI MAI YAWA DA ALBARKA MALAM MUDASSIR AMEEN.

Alhamdulillah TINUBU KAURA HOUSE ARGUNGU Yau 21/7/2026 an kaddamar da shuwagabannin Tinubu Kaura House wato gamayyar kun...
22/07/2026

Alhamdulillah

TINUBU KAURA HOUSE ARGUNGU

Yau 21/7/2026 an kaddamar da shuwagabannin Tinubu Kaura House wato gamayyar kungiyoyi magoya bayan APC na karamar hukumar mulki ta Argungu a karkahsin jagororin Alh. Abubakar Salihu Gulma Garkuwan matasan Gulma.

Muna rokon Allah ya baiwa APC nasara daga sama har kasa

🌙 Happy Muharram 1448 AH 🌙Allah Ya sa wannan sabuwar shekarar Hijira ta kasance cike da alkhairi, albarka, zaman lafiya ...
16/06/2026

🌙 Happy Muharram 1448 AH 🌙
Allah Ya sa wannan sabuwar shekarar Hijira ta kasance cike da alkhairi, albarka, zaman lafiya da ci gaba gare mu baki ɗaya.
Allah Ya sa mu dace da dukkan alheran da ke cikinta, Ya kare mu daga dukkan fitintinu, sharri da musibu da ke tattare da ita.
Ya Ubangiji, Ka ba mu lafiya, arziki mai albarka, zaman lafiya a ƙasarmu, da kyakkyawan ƙarshe.
Barka da Sabuwar Shekarar Musulunci. Happy Muharram!
🤲 Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya sa mu kasance cikin bayinsa na gari.
— Yarima Muhammad Kmsk Argungu

HAPPY BIRTHDAY TO COMRADE ZAKARIYA'U Comrade-Zakari Y Adamu Kontagora A wannan rana ta musamman, muna miƙa saƙon taya mu...
12/06/2026

HAPPY BIRTHDAY TO COMRADE ZAKARIYA'U Comrade-Zakari Y Adamu Kontagora
A wannan rana ta musamman, muna miƙa saƙon taya murna da fatan alkhairi ga fitaccen ɗan jarida, mai fafutukar zaman lafiya da tsaro, kuma jajirtaccen mai kare gaskiya da adalci, Comrade Zakariya'u Adamu Kontagora, yayin da yake bikin cika wani sabon shekaru na rayuwa.
Rayuwarka ta kasance abar koyi ga matasa da al'umma baki ɗaya. Jajircewarka wajen yaɗa gaskiya, inganta zaman lafiya, da ƙarfafa haɗin kan al'umma ya sanya ka zama abin alfahari ga jama'a da ƙasa baki ɗaya.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara maka lafiya, hikima, nisan kwana, da albarka a rayuwarka. Ya ci gaba da ba ka ƙarfin guiwa da basirar ci gaba da hidimtawa al'umma cikin gaskiya da riƙon amana.
Allah Ya sa wannan sabuwar shekarar ta zo maka da nasarori masu yawa, farin ciki mara iyaka, da cikar burin rayuwa.
🎂 Happy Birthday Comrade Zakari y Adamu Kontagora
Allah Ya ƙara shekaru masu albarka, Ya sa rayuwarka ta kasance mai amfani ga addini, al'umma da ƙasa baki ɗaya. Amin Ya Rabbal Alameen. 🤲🎉🎊
Yarima Muhammad Kmsk Argungu
12/06/2026

Innalillahi Wainna Ilaihin Raju'u Allah Ya Yiwa Sakina Lawali Jariri Rasuwa Bayan Gajeruwar Rashin Lafiya Sakina Wadda M...
09/06/2026

Innalillahi Wainna Ilaihin Raju'u Allah Ya Yiwa Sakina Lawali Jariri Rasuwa Bayan Gajeruwar Rashin Lafiya

Sakina Wadda Matar Alh Lawali Jariri Ce Ta Rasu Yau Attanin Da Misalin Karfe 12 Na Daren Attanin

Za,ayj Jana'izarta Yau Talata 9 06 2026 a Masallacin Idi Na Garin Argungu Da Misalin Karfe 10 Na Safe

Allah Ka Gafartawa Sakina Lawali Jariri Ka Raya Abinda Ta Bari Ka Baiwa Mai Gidanta Hakuri

Kakakin Cikin Gida 🎤 📢

ADC Is Working!A yau Lahadi, 07/06/2026, babbar ƙungiyar ATIKU/KULIYAN GWANDU (AKG) ta gudanar da zamanta na farko cikin...
08/06/2026

ADC Is Working!
A yau Lahadi, 07/06/2026, babbar ƙungiyar ATIKU/KULIYAN GWANDU (AKG) ta gudanar da zamanta na farko cikin nasara, domin ƙarfafa tubalin shugabanci nagari da kuma tsara ingantattun hanyoyin gudanar da ayyukanta cikin haɗin kai, tsari da manufa ɗaya.
Taron ya mayar da hankali ne kan tsara dabarun siyasa, wayar da kan al’umma, da ƙarfafa gwiwar magoya baya domin tabbatar da nasarar Atiku Abubakar a matsayin Shugaban Ƙasar Najeriya, tare da Abubakar Malami a matsayin Gwamnan Jihar Kebbi a zaɓen 2027.
Ƙungiyar na aiki ne ƙarƙashin jagorancin Dr. Nazifi Ladan, inda ta kuduri aniyar haɗa kan mambobi, ƙarfafa gwiwar magoya baya, da gina ingantaccen tsari mai ɗorewa wanda zai zama ginshiƙin cimma manufofin siyasa da ci gaban al’umma.
Da yardar Allah, wannan tafiya ta AKG za ta kasance mai albarka, cike da nasara, haɗin kai da ci gaba ga al’ummar Jihar Kebbi da Najeriya baki ɗaya.
AKG! AKG!! AKG!!!
Atiku for President 2027
Malami for Governor 2027
Haɗin kai, jajircewa da aiki tukuru su ne mabuɗin nasara. 💪🇳🇬
Yarima Muhammad Kmsk Argungu
07/06/2026

🚨 SAKON KIRA NA GAUGAWA NA TAIMAKO GA AL'UMMAR ARGUNGU 🚨Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuhu.A sakamakon ...
06/06/2026

🚨 SAKON KIRA NA GAUGAWA NA TAIMAKO GA AL'UMMAR ARGUNGU 🚨
Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta'ala Wabarakatuhu.
A sakamakon mummunar iska mai ƙarfi da ruwan sama da aka samu a daren Juma'a, al'ummar Argungu sun fuskanci babbar jarabawa wadda ta yi sanadiyyar lalacewar gidaje, rugujewar muhalli, da asarar dukiyoyi masu yawa ga iyalai da dama.
Wannan lamari ya jefa wasu daga cikin 'yan uwanmu cikin halin ƙunci da buƙatar taimakon gaggawa. Saboda haka, muna yin kira ga gwamnati, shugabanni, 'yan siyasa, masu hannu da shuni, ƙungiyoyi masu zaman kansu, da dukkan masu kishin al'umma da su gaggauta miƙa hannun taimako ga waɗanda wannan ibtila'i ya shafa.
A yau, abin da waɗannan bayin Allah ke buƙata shi ne goyon baya, taimakon kayan masarufi, kayan gini, matsuguni da kuma addu'o'in alheri domin su samu damar sake farfaɗo da rayuwarsu.
Addinin Musulunci ya koyar da mu tausayi da taimakon juna, musamman a lokutan ƙunci da jarabawa. Annabi (SAW) ya yi umarni da taimakon mabukata da tallafa wa waɗanda bala'i ya same su. Duk wanda ya taimaka wa ɗan'uwansa a lokacin tsanani, Allah Maɗaukakin Sarki zai taimake shi a lokacin da yake cikin buƙata.
Muna roƙon Allah (SWT) Ya jikan waɗanda abin ya shafa, Ya maye musu da mafificin alheri, Ya ba su haƙurin jure wannan jarabawa, Ya kuma saka wa duk masu taimako da alkhairi mai yawa.
🤲 Ya Allah Ka kare Argungu, Ka tsare al'ummarmu daga dukkan nau'ikan bala'o'i da fitintinu, Ka sanya wannan jarabawa ta zama sanadin samun rahama da alheri. Amin Ya Rabbal Alamin.
A taimaki al'umma, a ceci rayuka, a gina fata. 🤝💙

BIDADIYAR WASIKA ZUWA GA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR MULKI TA ARGUING 2nd June, 2026Hon. Aliyu Sani Gulma (Sarkin Aikin Kab...
02/06/2026

BIDADIYAR WASIKA ZUWA GA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR MULKI TA ARGUING 2nd June, 2026

Hon. Aliyu Sani Gulma
(Sarkin Aikin Kabi)

Assalamualaikum
Shuwagabannin mu masu albarka wato Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi Dr. Nasir Idris Kauran da Shugaban karamar hukumar mulki ta Argungu Hon. Sani Aliyu Gulma.

Matashiya:
• Gwamnatin Kauran Gwandu gwamnatin cigaba ce.
• Gwamnatin Kauran Gwandu gwamnatin jama'a ce.
• Gwamnatin Kauran Gwandu gwamnatin raya kasa ce.

Duk wata Gwamnati da ke kokarin sayarda kadarorin ta to akwai koma baya a cikin ta.

Gwargwado kunyi iya kokarin ku a jagorancin da Allah ya baku na al'umar Argungu, muna godiya Allah ya kara daukaka Argungu, Jihar Kebbi da Najeriya baki daya.

Game da jita jitar sayarda gidajen bayan gidan Mai Girma Tafidan Kabi da ke kai yana komowa don Allah muna fatan imma gaskiya ne to ayi tinani mai zurfi.

A karamar hukumar mulki ta Argungu babu wasu gidaje mallakar gwamnati da ake tsammanin ajiye wani babban jami'in gwamnati da ya wuce wadannan gidaje kuma mun san Kauran Gwandu indai kudi ake nema na gudanar da wani abu a kowace karamar hukuma yana iya kokarin sa.
Wannna gida baya kara ku ko rage ku da komai a cikin dukiyar ku.

Don Allah ku taimaki al'umar karamar hukumar mulki ta Argungu ta hanyar lalubo wani abu da zai taimaki al'amar ba sayarda gidaje ba.

Allah ya taimaka amin.

ENGR. GARBA HARUNA GARKUWAN KABI FOR SENATOR KEBBI NORTH SENATORIAL DISTRICT 2027 As you are casting your vote in the up...
09/05/2026

ENGR. GARBA HARUNA GARKUWAN KABI FOR SENATOR KEBBI NORTH SENATORIAL DISTRICT 2027

As you are casting your vote in the upcoming primaries and general elections, consider the values that Engr. Garba Haruna Garkuwan Kabi brings to the table. Vote for transparency, tranquility, innovative initiatives, youth inclusion, and exemplary leadership. Together, let us pave the way for a brighter future in Kebbi North.

He believes that an informed constituency is an empowered one and will prioritize open communication and accountability in all his dealings.

He understands the importance of community engagement, ensuring that every voice is heard and respected.

His track record showcases a commitment to developing innovative initiatives that address the pressing needs of our communities. From education and healthcare to infrastructure and economic development, his policies are designed to uplift and empower our citizens.

He is committed to including young voices in the decision making process, providing them with opportunities to lead and innovate. By investing in their potential, he aims to build a brighter tomorrow for us all.

His dedication to serving the community is evident in his actions, and he has the vision to steer Kebbi North toward a prosperous future.

Vote Engr. Garba Haruna Garkuwan Kabi for Senator, Kebbi North Senatorial District 2027

Garkuwan Kabi Media Team

Address

Tudun Wadan Argungu
Argungu

Telephone

+2348025755752

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kabawan Kanta Fm Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kabawan Kanta Fm Radio:

Shortcuts

Share