Kabawan Kanta Fm Radio

Kabawan Kanta Fm Radio Kabawan Kanta Fm Radio Na Maraba Da Kowa Domin Kawo Muku Labarai Fadakarwa, Ilmantarwa,Nishadantarwa

An samu nutse war  jirgin ruwa a ruwan Garin Yawuri;Daga sani Twoeffect YawuriA halin yanzu dai babu tabbacin Asarar rai...
17/06/2025

An samu nutse war jirgin ruwa a ruwan Garin Yawuri;

Daga sani Twoeffect Yawuri

A halin yanzu dai babu tabbacin Asarar rai, Ana Nan Dai Ana kokarin ceton mutane a mashayar ƴan haki dake garin Yawuri a jihar kebbi.

Da dumi'dumi: Masu ruwa da tsakin jam'iyyar APC sun amince da sake zaben Tinubu tare da Nuhu Ribadu.Masu ruwa da tsaki n...
17/06/2025

Da dumi'dumi: Masu ruwa da tsakin jam'iyyar APC sun amince da sake zaben Tinubu tare da Nuhu Ribadu.

Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Adamawa sun kada kuri’ar amincewa da gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Don haka, masu ruwa da tsakin da s**a yi magana a taron shugabannin jam’iyyar a Hong a ranar Talata, sun yi alkawarin goyon bayan sake zaben shugaban kasa a shekarar 2027 domin a samu karin ribar dimokuradiyya.

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Gabas, Salihu Mustapha, ya ce taron an yi shi ne da nufin wayar da kan shuwagabannin jam’iyyar don tabbatar da hadin kai da ci gaban jam’iyyar a jihar da ma kasa baki daya.

Mista Mustapha ya ce jam’iyyar a karkashin jagorancin Tinubu, ta samu gagarumar nasara da ta yi tasiri ga kasar nan.

Ya zayyana wasu nasarorin da aka samu da s**a hada da: aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000, biyan bashi, cin gashin kan kananan hukumomi, cire tallafin mai da yaki da cin hanci da rashawa.


Shugaban kwamitin sasantawa da kawo sauyi a shiyyar Adamawa ta tsakiya, Yusuf Captain-Buba, ya kuma yabawa Tinubu bisa gagarumin kokarinsa na farfado da tattalin arziki da kawo sauyi a harkar noma.

“Tare da wadannan da wasu da dama wadanda ba za mu iya ambata a nan ba, mun kada kuri’ar amincewa da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da kuma mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, kan dakile matsalar rashin tsaro da ke addabar wasu sassan kasar nan,” inji shi.

Mista Captain-Buba ya ce aikin kwamitin na sa shi ne sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar da s**a ji ra’ayinsu, tara jama’ar da s**a zabe su, da kwato kujerar gwamnan jihar da kuma sake zaben Tinubu a karo na biyu a shekarar 2027.

Don haka ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar a fadin jihar da su tabbatar da adalci da kuma hakuri da juna a tsakanin ‘ya’yan kungiyar.

A nasa jawabin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gombi a majalisar dokokin jihar, Rufa'i Umar, ya ce taron ya bayyana wasu dabarun tunkarar kalubalen da ke fuskantar jam'iyyar.

17/06/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un

Rahotanni da ke fitowa daga Ƙaramar Hukumar Zuru da ke jihar Kebbi sun bayyana cewa a yanzu haka ƴan bindiga sun kai farmaki garin Tarduga da ke ƙarƙashin Ƙaramar Hukumar, inda aka buƙaci mahukunta da su kai wa mutanen garin ɗaukin gaggawa.

17/06/2025

SIYASA TANA CIN MUTUNCIN SARAUTA SUN KAKABA WA MUTANE JAHILCI DA TALAUCI ALLAH KA YI MUNA MAGANIN AZZALUMAI

Inna lilahi wa innah Ilaihi raji'uun!Gobara ta ta sake kamata a wani yanki Kuma na cikin garin Argungu shiyar 'yardole k...
18/02/2025

Inna lilahi wa innah Ilaihi raji'uun!
Gobara ta ta sake kamata a wani yanki Kuma na cikin garin Argungu shiyar 'yardole kusa da M.T.D Inda ake zuba shara, Allah ya kawo muna dauki wannan Iftila'in Gobara dayake faruwa a Garin Argungu Amin

HUMAN RIGHT NETWORK KEBBI STATE EXCO'S1. STATE CO-ORDINATOR:- Muhammad Kabir Sallah (Yariman Kabi) 2.DUPUTY STATE CO-ORD...
17/02/2025

HUMAN RIGHT NETWORK KEBBI STATE EXCO'S

1. STATE CO-ORDINATOR:- Muhammad Kabir Sallah (Yariman Kabi)

2.DUPUTY STATE CO-ORDINATOR:
Jafar Ibrahim Commondo

3.ADMIN SECRETARY:
Surajo Kasimu Argungu

4.AMIN II SECRETARY:
Surajo Bello Warrah

5.STATE WOMEN CO-ORDINATOR:
Samira Shehu Duggu

6.DUPUTY STATE WOMEN CO-ORDINATOR:
Hauwa' AB Marafa

7.TREASURE :
Dr. Nasir Aliyu Maimagani Birnin Kebbi

8. INVESTIGATION OFFICER:
Comrade Dandare Jikan Jibo

9.TRAINING COORDINATOR:
Engr. Adamu Attahiru Dan Agaji

10. RESEARCH AND DOCUMENTATION OFFICER:
Mubarak Bala

11.HEAD OF PARALEGAL OFFICER:
Jafaru Muhammad Zager (Kakakin Cikin Gidan)

12.HEAD OF GUIDANCE AND COUNSELING:
Alhaji Abubakar Salihu Gulma

13.WELFARE OFFICER:
Garba Nahali Kamba

14.STATE LEGAL ADVISOR:
Nasir Salihu Gulma
Muhammad Sanusi Illo
Comrade Adamu Hasssan Argungu.

15.HEAD OF ICT:
Muhammad Tajudden Muhammad Bubuchi

16.HEAD OF MONITORING AND EVALUATION:
Surajo Aliyu Yalingo

17. HEAD OF CHILDREN PROTECTION UNIT:
Umar Samaila Dankal

18. PRO :
Bashar Salihu Ahmad ( Okala)

19. PROGRAM OFFICER:
Sahabi Garba
Abdullah AB Shooter

Majalisar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Ta Nada Sabbin Hakimawa 36 Da S**a Fito Daga Kananan Hukumomi 4 Na  Masarauta...
16/02/2025

Majalisar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Ta Nada Sabbin Hakimawa 36 Da S**a Fito Daga Kananan Hukumomi 4 Na Masarautar

Ga Sunayen Hakimawan Da Garuruwan Su Hadi Da Gundumomin Da S**a Fito

A . GUNDUMAR GULMA
1.Alh Idris Abubakar Gulma - Magajin Sabon Garin Gulma
2.Mal. Abubakar Salihu - Marafan Gulma
3.Alh Ummaru Sani -Chiroman Gulma

B.GUNDUMAR ZAZZAGAWA
4.Alh Saidu Husaini-Dan Kado Zazzagawa Birni

C. GUNDUMAR ALWASA
5.Alh Shehu Magaji - Barajen Alwasa

D. GUNDUMAR AUGIE
6.Mal. Mu,azu Isah Mera -Tudu Mera

E.GUNDUMAR KASAR BAYAWA
7.Mal.Yahaya Muhd Sabla -Mai Yakin Sabla

F .GUNDUMAR YOLA
8.Mal. Salihu Hakimawa -Mai Yakin Hakimawa

G. GUNDUMAR TIGGIE
9.Mustafa Zarummai-Zarumman Awade
10.Aminu Alh Usman Lugga -Marafan Lugga
11.Mal Usman Rugga Sambo -Rugga Bakaramba

H.GUNDUMAR KWAIDO
12.Alh Usman Rafi Abubakar -Rafin Illela
13.Mal Sanusi Sulaiman Musa -Magajin Tungar Magaji
14. Mal. Lawali Abubakar-Rafin Tungar Rafi
15 .Mal Buhari Yusuf Kwaido -Hakimin Sabon Gari

I.GUNDUMAR BUBUCHE
16.Samaila Yahuza -Gidan Koni
17.Umae Magaji Gudale -Magajin Gudale ||

J.GUNDUMAR YELDU
18.Yahaya Muhd Yeldu -Rafin Kudun Yeldu

K. GUNDUMAR BUI
19.Alh Hashimu Usman -Dikkon Bui
20.Alh Kabiru Haruna -Tudun Tambo
21.Mal Abdullahi Gandu -Gandun Tago

L. GUNDUMAR CHIBIKE
22.Alh Umar Kwando -Mai Falan Fawangu

M. GUNDUMAR JEFFEJI
23.Alh Sani Muhd - Hakimin Hakimawa
24.Alh Usman Salisu-Mai Yamma Tambo

N.GUNDUMAR LAIMA

25.Yahaya R Ibrahim Bagulmen Rausa

O.GUNDUMAR KWAKKWABA
26.Yusuf Garba -Gwade | Fingillah

27. Alh Surajo Marafa -Marafan Gabas Sabon Gari

P. GUNDUMAR FANA A

28.Nasiru Garba -Ubandoman Fana
29.Abdullahi Isah -Zarumman Isakaina
30.Muhammadu 31.Abdulmumuni-Zarumman Shiko ||

32.Amadu Dodo -Barajen Maigwaza

33.Musa Mai Gari -Guben Tsika

B.GUNDUMAR GEZA

34.Mal Mainasara Marafa Balu -Marafan Balu
35.Abubakar Abdullahi-Mai Yakin Dikushi
36. Garba Abdullahi-Belin Mai Fama

Ina Addu'ar Allah Ya Tayasu Riko

Daga Fadar Mai Martaba Sar

Shahararren Ɗan Bìndiga Babaro Shine Yake Rìƙe Da Janar Tsiga Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A KatsinaDaga Aliyu Adamu TsigaSh...
16/02/2025

Shahararren Ɗan Bìndiga Babaro Shine Yake Rìƙe Da Janar Tsiga Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A Katsina

Daga Aliyu Adamu Tsiga

Shahararren shugaban ƴan fashin dajin nan Babaro wanda ya addabi yankin Karaɗua ya yi garkuwa da Birgediya Janar Maharazu Tsiga ne a ranar Laraba a gidan sa dake cikin garin Tsiga.

Yanzu haka dai Maharazu Tsiga yana tsare ne a dajin Bununu da ke ƙaramar hukumar Faskari kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Yankara ta jihar Katsina.

Wasu mutane da akayi garkuwa dasu ranar 14 ga watan Janairu 2025 daga yankin Kandarawa da ke ƙaramar hukumar Bakori wanda s**a shaƙi iskar ƴanci ne s**a bayyana hakan cewa lallai sunga Maharazu Tsiga inda ya ke tsare a hannun ƴan bindigar.

An sako su ne bayan sun biya kuɗin fansa naira miliyan 30 kuma sun bayyana cewa sun ga Brig. Gen.Tsiga a tsare. Sun yi ikirarin cewa duk da cewa har yanzu ana tsare da shi lokacin da s**a tafi, sedai sun shaida cewa yana samun kulawar da yake buƙata a wurin ƴan fashin Dajin.

Al’ummomin ƙananan hukumomin Yankara, Malumfashi, Bakori, Faskari, da Funtua duk sun sha fama da wannan ɗan bindiga mai suna Babaro. A halin yanzu dai ƴan bindigar sun nemi kuɗin fansa Naira Miliyan ₦250 domin su sako Maharazu Tsiga wanda tsohon shugaban hukumar yi wa kasa hidima (NYSC).

An dai sace MI Tsiga, Birgediya-Janar mai ritaya a rundunar sojojin Najeriya, a yammacin Larabar da ta gabata a gidansa da ke garin Tsiga, wanda ke karamar hukumar Bakori ta jihar Katsina.

Inna Ilahiri WA inna illahi raji'unGobara Da lakume Shaguna a Garin Argungu, Yan kasuwa Allah ya bayar muku da Alkhairi
16/02/2025

Inna Ilahiri WA inna illahi raji'un
Gobara Da lakume Shaguna a Garin Argungu, Yan kasuwa Allah ya bayar muku da Alkhairi

MUGU BAI DA K**ASunansa Abdulrahman Muhammad Ballo, yana yin Facebook, ya hadu da wannan yarinya a Facebook mai suna Haf...
16/02/2025

MUGU BAI DA K**A

Sunansa Abdulrahman Muhammad Ballo, yana yin Facebook, ya hadu da wannan yarinya a Facebook mai suna Hafsa Lawal inda s**a kulla soyayya s**ayi musayen nambar waya

Kwanaki shida da s**a wuce wato ranar 10-2-2025 Abdulrahman ya kira Hafsah akan su hadu, tunda daga wannan ranar aka nemeta aka rasa

'Yan sanda sun karbi nambar wayan Hafsah s**a duba last call da last location dinta wanda hakan ya taimaka aka gano da Abdulrahman tayi waya na karshe, sai akayi tracking dinsa aka kamashi

Da farko ya musa cewa shi ya ka$heta, yace wai cutar asthma ne yayi aja|inta, da akaje searching gidansu sai aka tarar da g@warta a wani daki ya daddat$a ta ya cire wasu sa$$a na jik!nta

Irin wadannan abubuwa da suke faruwa ya kamata ya zama babban darasi ga 'yan matan social media, ku shiga taitayinku, ku dinga sanin wadanda zaku hadu da su

Kuma ma imba lalacewa ba babu dalilin da zai sa mace budurwa tabi saurayi hotel ko gidansa, idan aure ne da gaske yake to ya je gidanki ba wai ke ki bishi ba

Allah Ya kare mu daga sharrin cin amanar wadanda muka basu aminci.

Daga Datti Assalafy

09/02/2025

Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun. Allah yayi wa Alhaji Sanda Adamu Tsafe (Sarkin yakin Tsafe) former General manager Rima radio Sokoto rasuwa a asibitin UDUTH dake Sokoto bayan rashin lafiya.

Ya rasu ya bar mata biyu da ya'ya 29.
Za'ayi Janaizarsa a Darul Da'awa da ke Kan titin Kaduna a Sokoto da karfe 2.00pm na rana a yau Lahadi.

Allah ya gafarta mashi yasa Aljannah ce makomarsa. Sanarwar daga Alhaji Aliyu Adamu Tsafe, Managing Director Gamji Radio da Television Gusau. Allah yajikanshi da rahama yasa aljannace makomarsa. Amin yaa Rabbi.👏

06/02/2025

Inna lillahi wa inna ilaihin raji'un
yanzun nan cikin daren nan wasu da ba asan ko suwayeba s**a shiga cikin garin Gulma a babban shagon Alh fatahu aljazeera inda s**a halbi mutane wajan goma cikinsu daya yasu saura na jikkiice a asibiti muna rokon Allah yakawo muna sauki wannan ta addanci a arewacin najeriya musamman jahar kebbi Amen summa Amen

Address

Tudun Wadan Argungu
Argungu

Telephone

+2348025755752

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kabawan Kanta Fm Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kabawan Kanta Fm Radio:

Share