KCB Hausa News

KCB Hausa News 𝐌𝐄𝐃𝐈𝐀

ABIN FARIN CIKI: Ya Je Tambayar Maigidansa Kudin Da Zai K**a Haya Saboda Aurensa Ya Gabato, Kawai Sai Maigidan Nasa Ya M...
11/07/2025

ABIN FARIN CIKI: Ya Je Tambayar Maigidansa Kudin Da Zai K**a Haya Saboda Aurensa Ya Gabato, Kawai Sai Maigidan Nasa Ya Mika Masa Takardar Gidan Da Ya Siya Masa Kyauta

Bikin abokina Abdul Ɗorayi za a yi saura sati hudu, sai ɗazu muka je gidan me gidansa domin maganar kuɗin hayar gidan da za su zauna.

Abin mamaki Wallahi sai maigidan nasa ya ce yana zuwa, muna nan zaune a ƙofar gidansa kawai sai gashi da takardar gida ashe ya siya masa gida, Wallahi tsabar daɗi ni da shi kawai sai ga hawaye a idanunmu.

Muka kira babarsa a waya muka gaya mata kawai sai ta saki wayar ta faɗi ta fashe tana kukan daɗi.

Ya Rabbi Ka sanya albarka, Ka biyawa Ogan nasa da gidan Aljannah.

Wannan shine cikakken uban gida.

Daga Comr Bashir Isiyaku Gaida

Gwamna Abiodun ya baiwa iyalan ƴan wasan Kano da su ka rasu a hatsarin mota Naira Miliyan 31Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abi...
02/06/2025

Gwamna Abiodun ya baiwa iyalan ƴan wasan Kano da su ka rasu a hatsarin mota Naira Miliyan 31

Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun, a ranar Lahadi ya aike da tawaga zuwa Jihar Kano domin yi wa gwamnatin jihar da al’ummar Kano ta’aziyya bisa rashin wasu 'yan wasa da jami'ai da s**a rasu yayin dawowa daga gasar wasanni ta kasa da aka kammala kwanan nan.

Gwamna Abiodun ya kuma ba da gudummawar Naira miliyan daya (N1m) ga kowanne iyali daga cikin iyalan mamatan a matsayin taimako na farko, wanda jimillar kudin ta kai Naira miliyan 31.

A cewar wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, mataimakiyar gwamna, Injiniya Noimot Salako-Oyedele ce ta jagoranci tawagar, da ta haɗa da Sakataren Gwamnatin Jihar Ogun, Mista Tokunbo Talabi; Kwamishinan Ci gaban Wasanni, Hon. Wasiu Isiaka; da Sakataren Gudanarwa na Kwamitin Shirya Gasar wasanni ta kasa Dr. Kweku Tandoh.

Tawagar ta iso Kano da misalin ƙarfe 9 na safe, inda mataimakin gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdusalam Gwarzo, tare da wasu jami'an gwamnatin Kano s**a tarbe su.

Yayin da ta ke bayyana jimamin Gwamna Abiodun kan wannan musiba, Salako-Oyedele ta miƙa sakon ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kano.

Ta ce:"Mun san cewa gwamnan yana wajen aikin Hajji a yanzu, amma mun ga ya dace mu zo da kanmu domin nuna goyon bayanmu ga Gwamna, Gwamnati da al’ummar Jihar Kano a wannan lokaci na jarrabawa.

"Wannan babban rashin da ya shafi Jihar Kano ne, masu ruwa da tsaki a fannin wasanni gaba ɗaya, musamman dangin mamatan da abokan arzikinsu. Muna kuma addu'ar Allah ya ba wa waɗanda ke kwance a asibiti lafiya cikin gaggawa.

YANZU-YANZU: Hukumar tace finai finai ta jihar Kano ta dakatar da nuna fim din 'Labarina' da gidan Sarauta da wasu karin...
19/05/2025

YANZU-YANZU: Hukumar tace finai finai ta jihar Kano ta dakatar da nuna fim din 'Labarina' da gidan Sarauta da wasu karin fina finai 20

A kokarinta na tabbatar da ana bin dokar tace fina-finai sauda kafa tare da kara dora masana'antar kannywood a kan saiti, Hukumar tace fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano karkashin jagorancin Alh Abba El-mustapha ta dauki wani gagarun mataki domin tsaftace yadda ake sakin fina-finai barkatai batare da cika ka'idar da doka ta tanadar musu ba na kawo kowanne film gabanta a tantance shi kafin ya isa ga idanun al'umma inda ta dakatar da wasu Manyan Fina-finai har guda 22 daga sakasu a kafafen Internet ko gidan TV

Abba El-mustapha ne ya bayyana wannan mataki biyo bayan tattaunawa da manyan jami'an Hukumar tare da dogon nazari domin kawo karshen korafe korafen da Hukumar take yawan karba dan kara inganta aiyukan Hukumar tare da masana'antar kannywood.

Abdullahi Sani Sulaiman shine jami'in yada labaran Hukumar ya bayyana fina-finai da aka dakatar kamar haka:

1. Dakin Amarya
2. Mashahuri
3. Gidan Sarauta
4. Wasiyya
5. Tawakkaltu
6. Mijina
7. Wani Zamani
8. Labarina
9. Mallaka
10. Kudin Ruwa
11. Boka Ko Malam
12. Wa yasan Gobe
13. Rana Dubu
14. Manyan Mata
15. Fatake
16. Gwarwashi
17. Jamilun Jiddan
18. Shahadar Nabila
19. Dadin Kowa
20. Tabarma
21. Kishiyata
22. Rigar Aro

Ya kara da cewa doka ce ta bawa Hukumar damar tace duk wani film tare da lura da aiyukan ‘yan masana'antar kannywood matsawar suna da rejista da Hukumar a ko ina suke, A saboda haka ana shawartar masu daukar nauyin wannan fina-finai da su tabbatar da sunbi wannan doka ta dakatarwa tare da tsayar da saka wannan fina-finai a gidajen TV ko kafar internet. Haka kuma ana sanardasu cewa su miko fina-finansu ga Hukumar domin tantance su tare da basu shaidar inganci ta tacewa nanda sati daya mai zuwa wato daga *LITININ, 19 ga watan MAYU, 2025 zuwa 25 ga MAYU, 2025* domin gujewa fushin doka.

A karshe Hukumar ta nemi hadinkan dukkannin gid

CIKIYA CIKIYA CIKIYA Muna kira ga al’umma da su taya mu da addu’a ga ɗan’uwanmu, Baba Azare, wanda aka neme shi aka rasa...
14/05/2025

CIKIYA CIKIYA CIKIYA

Muna kira ga al’umma da su taya mu da addu’a ga ɗan’uwanmu, Baba Azare, wanda aka neme shi aka rasa tun jiya da misalin ƙarfe goma na safe wayoyin sa a kashe.

Rahotanni sun nuna cewa zuwa yanzu ba mu da tabbacin lafiyarsa ko inda yake, lamarin da ya ɗaga hankalin dangi, abokai da al’umma gaba ɗaya.

Don haka, muna roƙon ku da ku tayamu da addu’a da fatan Allah Ya dawo mana da Baba Azare cikin koshin lafiya, Ya kare shi daga sharri, Ya kuma ba mu cikakken haske game da halin da yake ciki.

Daga. Abbati Mohammed

Taya Murna Ga Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani A Ranar Zagayowar Haihuwarsa Ta Shekara 54Bismillahir Rahma...
31/12/2024

Taya Murna Ga Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani A Ranar Zagayowar Haihuwarsa Ta Shekara 54

Bismillahir Rahmanir Rahim.

Ina taya Mai Girma Sanata Uba Sani, Gwamnan Jihar Kaduna, murnar zagayowar ranar haihuwarsa ta shekara 54.

Wannan rana ta musamman tana tunatar da mu irin namijin kokarin da ka yi wajen sadaukarwa don cigaban al’umma, jajircewa wajen samar da ci gaba, da tabbatar da adalci ga kowa da kowa.

A cikin shekaru masu yawa da s**a gabata, ka nuna cewa jagoranci abin koyi ne ta hanyar jajircewarka wajen kawo tsaro, ilimi mai nagarta, da aikin gyaran tattalin arziki a jihar Kaduna.

A matsayin ka na gwamna, ka taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa rayuwar talakawa da karfafa matasa don su zama tushen ci gaban al'umma.

Yayin da ka cika shekara 54, muna rokon Allah Ya albarkaci rayuwarka da karin lafiya, hikima, da nasarori. Allah Ya kara wa jihar Kaduna cigaba da albarka a karkashin jagorancinka.

Wannan shekara mai albarka ta zama cike da farin ciki da nasarori a gare ka da al’ummar da kake yi wa hidima.

Allah Ya yi maka jagora, ya kuma ninka alherin da kake yiwa al’umma ya albarkace ka da kai da iyalanka ya shiga dukkan al'amuranka ameen ya Allah.

Daga: Hon. Shu’aibu Mai Canter

DA ƊUMI ƊUMI: Yadda Jami'o'in Arewa S**a Zamo Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Lamunin Ɗalibai A Gwamnatin Shugaba Tinubu.
24/08/2024

DA ƊUMI ƊUMI: Yadda Jami'o'in Arewa S**a Zamo Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Lamunin Ɗalibai A Gwamnatin Shugaba Tinubu.

Tinubu na ƙoƙarin ruguza kungiyar kwadago ta NLC a Najeriya. Kungiyar kwadago ta caccaki Tinubu kan katsalandan a lamari...
17/08/2024

Tinubu na ƙoƙarin ruguza kungiyar kwadago ta NLC a Najeriya.

Kungiyar kwadago ta caccaki Tinubu kan katsalandan a lamarin jagorancin kungiyar NLC ta kasa.

son Upah, mai magana da yawun NLC ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Alhamis a Abuja.

Upah ya yi zargin cewa gwamnati na son sanya wa shugabannin kwadago wa'adin shekaru biyu rak. Ya ce irin wannan mataki zai kai ga yin katsalandan a harkokin cikin gida na kungiyoyin kwadago da kuma keta haddin dokar aiki da kuma yarjejeniyar kungiyar kwadago ta kasa da kasa (ILO).

“Yakamata gwamnatin tarayya ta kawo karshen yakin da ake yi da ‘yan majalisa. Duk da haka, idan gwamnati ta ga cewa shekaru biyu ne mafi kyawun wa'adin mulki, to ya kamata a kasance shekaru biyu ga kowa da kowa, ciki har da ofishin shugaban kasa da kuma manyan jami'an gwamnati," in ji jami'in NLC.

APC ta fara Yunkurin mayar da Sen Ndume Matsayin Babban Mai Tsawatarwa na Majalisar DattawaJam’iyyar All Progressives Co...
12/08/2024

APC ta fara Yunkurin mayar da Sen Ndume Matsayin Babban Mai Tsawatarwa na Majalisar Dattawa

Jam’iyyar All Progressives Congress mai mulki ta fara tuntubar shugabannin majalisar dattawa domin saukaka maido da Sanata Ali Ndume a matsayin babban mai Tsawatarwa.

Matakin na zuwa ne wata guda bayan an sauke Ndume mai wakiltar mazabar Borno ta Kudu daga mukaminsa sakamakon s**ar da ya yi wa shugaban kasa Bola Tinubu da kuma jam’iyyar APC mai mulki.

Dan majalisar na Borno ya yi ikirarin cewa an tsare shugaban ne da kuma kare shi daga jin wahalhalun da ‘yan Najeriya ke ciki, lamarin da ya harzuka jam’iyya mai mulki.

Nan take Sanata mai wakiltar Borno ta Arewa, Tahir Monguno ya maye gurbin Ndume, biyo bayan umarnin da aka bayar a kan hakan a wata wasika da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje da sakataren kasa, Sanata Basiru Ajibola s**a rubuta.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya gabatar da bukatar a kada kuri’a, sannan da babbar murya daga dukkan Sanatocin APC.

A ranar Talatar da ta gabata ne Ndume Ya shaida wa manema labarai bayan ganawar sirri da ya yi da kwamitin aiyuka na kasa na tsawon sa’o’i biyu a Abuja cewa ya mika wa jam’iyyar APC hakuri kan kalamansa nasa da yayi Dangane da shugaba Tinubu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Ganduje, ya ce an karbi uzurin Ndume, inda ya kwatanta lamarin a matsayin na iyali.

“Muna rubutawa Majalisar Dokoki ta kasa ne domin mu isar da abin da ya faru tsakanin Sanata Ndume da jam’iyyar. K**ar yadda kuka sani, ya nemi gafarar jam’iyyar da fatan za su sake duba matsayinsa,” in ji Ganduje.

Kwanaki uku bayan taron, Wata majiya a sakatariyar jam’iyyar da ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida Jaridar Funch cewa jam’iyyar ta bude tattaunawa da shugabannin majalisar dattawa domin duba batun tsige Ndume a matsayin babban mai Tsawatarwa na Majalisar Dattawa.

Da aka tuntubi mataimakin sakataren jam’iyyar APC na kasa, Nze Chidi Duru, ya tabbatar da tuntubar da ake yi, wanda a cewarsa, ba lallai ne a gudanar da shi a bainar jama’a ba.

KTG Hausa

Na Bawa Jam'iyyar APC Reshen Jihar Kano Awa 48 Ta Fito Ta Janye Kalaman Ta Da Tayi Na Zargin Audu Bulama Bukarti, Jafar-...
12/08/2024

Na Bawa Jam'iyyar APC Reshen Jihar Kano Awa 48 Ta Fito Ta Janye Kalaman Ta Da Tayi Na Zargin Audu Bulama Bukarti, Jafar-jafar, Da Ɗan Bello Na Kokarin Tayar Da Tarzoma A Jihar Kano, Idan Kuma Taki Zan Shige Mataki Na Gaba, Cewar Ɗan Bello

Me za ku ce ?

Babu adalci Ga masu iƙrarin Shugaba Tinubu ya fifita yankin Kudu fiye da Arewa Inji Kashim ShettimaMataimakin shugaban k...
12/08/2024

Babu adalci Ga masu iƙrarin Shugaba Tinubu ya fifita yankin Kudu fiye da Arewa Inji Kashim Shettima

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya yi tsokaci kan zage-zagen da ake yi cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da yankin Arewa, yana mai cewa irin waɗannan ikirari ba su da tushe b***e makama. Ya kuma jaddada cewa, bai kamata yankin Arewa ya fuskanci talauci ba, ganin dimbin albarkar dake cikinsa.

A wata hira da Rediyo Faransa RFI da Sashen Hausa na RFI da ke sa ido a Kaduna a ranar Lahadi, Shettima ya tattauna kan zanga-zangar da aka yi a baya-bayan nan, inda ya ce, “A tsarin dimokuradiyya, ‘yan kasa na da ‘yancin fadin kokensu cikin lumana. Duk da haka, dole ne mu guji barin ’yan siyasa masu mugun nufi da ’yan iskanci su tada fitina da rashin zaman lafiya. Abin takaici, irin wannan tarzoma ta faru.”

Shettima ya yarda cewa yayin da Shugaban kasa ke goyon bayan 'yancin 'yan kasa, abubuwan da s**a faru na baya-bayan nan sun kasance masu damuwa ga al'umma da gwamnati.

Dangane da tallafin da ake bai wa Arewa, Shettima ya ce, “Gwamnati ta dukufa wajen taimakawa al’ummar Arewa. Mun ware Naira Biliyan 100 don tallafa wa harkar noma da kuma shirin tallafa wa manoma miliyan 500, wadanda yawancinsu ‘yan Arewa ne. Bugu da kari, shugaban ya kafa ma’aikatar kiwo domin tallafa wa makiyayan da s**a fi yawa a Arewa. Mun kuma raba kimanin tan 42,000 na abinci daga asusun gwamnati don magance tsadar rayuwa da tsadar abinci.”

Akan ma’aikatan gwamnati, Shettima ya bayyana karin albashi mafi karanci daga N30,000 zuwa N70,000 tare da tabbatar wa ‘yan kasar kudurin shugaban kasa na magance matsalolin da suke ciki. Ya kara da cewa "Mun amince da matsalolin da mutane ke fuskanta kuma mun kuduri aniyar daukar matakan da s**a dace don rage musu radadi."

Shettima ya jaddada cewa, “’yan siyasar da ke ikirarin cewa gwamnatin ta fifita Kudu kan Arewa, ba Gaskiya suke ba. Daga cikin ministoci 46, 24 daga Arewa ne. A tarihance, babu wata gwamnati da ta samu wakilan Arewa masu yawa a manyan mukamai. Misali, Ministan Tsaro, Muhammadu Badaru Abubakar, dan Jigawa ne, sai kuma Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle Maradun, dan Zamfara ne. Ministan Noma, Abubakar Kyari dan Arewacin Borno ne, kuma Ministan Ilimi Tahir Mamman dan Adamawa ne.”

Shettima ya musanta zarge-zargen nuna son kai, inda ya bayyana cewa wakilcin gwamnati da ayyukanta na nuna aniyar magance bukatun dukkan yankuna.

KCB Hausa News

Yara miliyan huɗu 4m da muka tarar suńa gárarąmba a tituna yanzu mun kwáshe su mun mayar dasu makarańta -Inji Ministån I...
11/08/2024

Yara miliyan huɗu 4m da muka tarar suńa gárarąmba a tituna yanzu mun kwáshe su mun mayar dasu makarańta -Inji Ministån Ilimi, Prof Tahir Mamman

Me zaku ce ?

Yanzu anyi 1-1, su āzzālūmāi suna da RARARA, su kuma talakawa suna da  'DAN BELLO.Ya kuke ganin haka?
11/08/2024

Yanzu anyi 1-1, su āzzālūmāi suna da RARARA,
su kuma talakawa suna da 'DAN BELLO.

Ya kuke ganin haka?

Address

Azare

Telephone

+2347067658337

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KCB Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share