07/07/2026
DA DUMI-DUMI: Ana Hasashen Malam Nasiru El-Rufai Zai Janye Goyon Bayansa Daga Jam'iyyar ADC, majiyar ATP English ta sami wasu kwafin takardu na wasika da Malam Nasiru El-rufai ya aika ga Uwar jam'iyyar.
Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, na iya janye goyon bayansa ga Jam’iyyar ADC.
A cewar majiyar, wannan na da alaƙa da zargin cewa jam’iyyar ta nuna halin ko-in-kula game da halin da El-Rufai ke ciki bayan da hukumomin tsaro s**a tsare shi.
Haka kuma, a jiya wata murya ta bazu a kafafen sada zumunta, wadda ake zargin ta ɗan takarar gwamnan Jihar Kaduna na ADC, Isah Ashiru Kudan, ce. A cikin muryar, an ji ana caccakar El-Rufai, inda aka ce ba mutumin kirki ba ne, tare da ikirarin cewa shiga ADC da ya yi saboda neman tikitin takara ne kawai, ba wai don goyon bayan El-Rufai ko siyasar da yake tafiya a kanta ba.
Sai dai, har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, ba a tabbatar da sahihancin muryar ba, kuma babu wata sanarwa a hukumance daga El-Rufai, Isah Ashiru Kudan ko shugabannin ADC da ta tabbatar da waɗannan zarge-zarge.