02/10/2025
Tinubu Ya Kaddamar da Gidan Wasa Na Ƙasa, don Girmama Soyinka
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake kaddamar da sabon ginin Gidan wasan kwaikwayo na Ƙasa a Lagos, inda aka yi wa ginin garambawul, tare da sanya masa sunan fitaccen marubuci kuma gwarzon lambar yabo ta Nobel, Farfesa Wole Soyinka. Wannan shi ne karo na biyu da shugaban ya girmama Soyinka, bayan da a baya aka saka sunan titin da ke Abuja da sunansa.
Tinubu ya bayyana cewa wannan mataki hanya ce ta nuna godiya da girmamawa ga Soyinka, wanda ayyukansa s**a ɗaga martabar Najeriya a duniya ta fuskar kirkire-kirkire da kuma kare haƙƙin ɗan adam.
Shugaban ya kuma nuna fata cewa sake farfado da wannan katafaren gini zai ƙarfafa harkokin fasaha, al’adu, da bunkasa tattalin arzikin kirkire-kirkire a Najeriya, wanda hakan zai taimaka wajen ƙirƙiro sabbin hanyoyin samun kudaden shiga da cigaba ga matasa