Burra Daily News

Burra Daily News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Burra Daily News, Media/News Company, Bauchi Ningi Burra Budugu, Bauchi.

"MURYAR BUTAWA"

BURRA DAILY NEWS Shafine dazaina kawo muku Labaran Cikin Gida dana waje, Tareda labaran Duniya baki ɗaya MUNGODE da Zaɓinmu Amatsayin Shafin Jin Labaran Ku. 07089421279

GWAMNATIN TARAYYA TA ƘARA ƘAIMI WAJEN YAƘI DA RASHIN TSARO, AN YAYE DAKARUN FOREST GUARDS A KADUNA DA KOGIGwamnatin Tara...
03/08/2026

GWAMNATIN TARAYYA TA ƘARA ƘAIMI WAJEN YAƘI DA RASHIN TSARO, AN YAYE DAKARUN FOREST GUARDS A KADUNA DA KOGI

Gwamnatin Tarayya, tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohin Kaduna da Kogi, ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da rashin tsaro ta hanyar yaye sabbin dakarun Forest Guards domin daƙile ayyukan 'yan ta'adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka da ke amfani da dazuka a matsayin mafaka.

A Jihar Kaduna, Gwamna Sanata Uba Sani ya jagoranci bikin yaye dakaru sama da 1,000 da aka horas ta haɗin gwiwar Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA) da Hukumar DSS. An zaɓo dakarun ne daga cikin jami'an Kaduna Vigilance Service (KADVS) guda 7,000, inda aka ba su horo na musamman tare da tanadar musu kayan aiki domin ƙarfafa yaƙi da 'yan ta'adda a yankunan dazuka.

A Jihar Kogi kuwa, Gwamna Ahmed Usman Ododo ya yaye rukunin farko na dakarun Forest Guards guda 530 bayan sun kammala horo na makonni takwas. Ya bayyana cewa rundunar za ta yi aiki tare da sauran hukumomin tsaro wajen kare dazuka, tattara bayanan sirri da kuma hana masu aikata laifuka samun mafaka.

Gwamnonin jihohin biyu sun yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA) da sauran hukumomin tsaro bisa goyon baya da haɗin kai wajen aiwatar da shirin. Haka kuma, wani jami'in ONSA ya bayyana cewa Kaduna ita ce jiha ta farko da ta nemi Gwamnatin Tarayya ta horas da dakarun Forest Guards, yana mai cewa shirin ya samu gagarumar nasara.

Masana harkokin tsaro na ganin cewa faɗaɗa rundunar Forest Guards wani muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen hana 'yan ta'adda amfani da dazuka a matsayin mafaka, tare da inganta zaman lafiya da samar da yanayin da zai bunƙasa noma, kasuwanci da sauran ayyukan raya ƙasa.

— Burra Daily News

HOTUNA: Yadda Gwamnatin jihar Bauchi ta kaddamar da kotun tafi da gidanka karkashin ma'aikatar bunƙasa kiwon dabbobi ta ...
03/08/2026

HOTUNA: Yadda Gwamnatin jihar Bauchi ta kaddamar da kotun tafi da gidanka karkashin ma'aikatar bunƙasa kiwon dabbobi ta jihar Bauchi domin hukunta waɗanda s**a karya dokar hana noma a gefen manyan hanyoyi a tazarar mita 45 daga tsakiyar babbar hanya zuwa gefe da gefen hanya.

Daga Albarka Radio.

DANGOTE: Kamfani Dangote ya fara sakawa Motocin sa CCTV Camera Sabida masu Daukar kayan kari na Kaya kona Mutane idan su...
03/08/2026

DANGOTE: Kamfani Dangote ya fara sakawa Motocin sa CCTV Camera Sabida masu Daukar kayan kari na Kaya kona Mutane idan sun dauki kayan Kamfani zas**ai wani States din.

Meza Kuce.?

AYI SIYASA BADA GABA BADan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar Mazabar Burra a ƙarƙashin jam'iyy...
03/08/2026

AYI SIYASA BADA GABA BA

Dan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar Mazabar Burra a ƙarƙashin jam'iyyar APC, Hon. Jibrin Musa Kwangi, ya kai wa ɗan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi na jam'iyyar ADC, Hon. Abdulrahman Kurmi, ziyarar bazata a gidansa dake garin Kurmi.

Wannan hoto ya nuna cewa siyasa ba dole ba ce ta zama tushen gaba ko ƙiyayya ba. Duk da bambancin jam'iyya da ra'ayi, ana iya ci gaba da mutunta juna, girmama juna da kuma kyautata alaƙa.

Darasin da za a koya daga wannan hoto shi ne:

- Siyasa hanya ce ta hidimar al'umma, ba ta gaba ba.
- Bambancin jam'iyya bai kamata ya raba zumunci da mutunta juna ba.
- Tattaunawa da haɗin kai sun fi anfani fiye da rikici.
- A lokacin zaɓe, a yi takara cikin mutunci, sannan a ci gaba da zama 'yan uwa bayan siyasa.

Burra Daily News

HON IBRAHIM TANKO YANA AIKI IYA BAKIN KOKARINSA, YABA MASA YA KAMATA AYI DOMIN YA KARA KOKARI AKAN WANDA YAKE BA NUNA HA...
03/08/2026

HON IBRAHIM TANKO YANA AIKI IYA BAKIN KOKARINSA, YABA MASA YA KAMATA AYI DOMIN YA KARA KOKARI AKAN WANDA YAKE BA NUNA HASSADA KO ADAWAR CIN MUTUNCI BA

Abdullahi Choopice ya bayyana cewa adawar siyasa ta gari ita ce wadda ke kawo gyara da ci gaba ta hanyar nuna kura-kurai da gabatar da korafe-korafe masu ma'ana, ba ta hanyar cin mutunci ko aibata mutane ba.

Ya ce, tun lokacin da ake siyasa a Mazabar Burra, bai taba ganin jajirtaccen ɗan siyasa kamar Hon. Ibrahim Tanko Burra ba wajen tallafa wa matasa, marasa lafiya, da kuma bayar da gudummawa ga ci gaban al'ummar Burra baki ɗaya.

A cewarsa, irin waɗannan ayyuka ne s**a sa wasu ke ƙoƙarin muzanta shi ta kafafen yaɗa labarai. Ya bayyana cewa wannan ba salon siyasa mai kyau ba ne, yana mai jaddada cewa kamata ya yi a mayar da hankali kan s**a mai amfani da za ta haifar da gyara, maimakon cin mutunci da ƙoƙarin bata sunan mutane.

Ya yi kira ga 'yan siyasa da magoya baya da su sauya salon adawa, su rungumi siyasar da za ta amfani al'umma da kuma inganta ci gaban yankin Burra.

A ƙarshe, Abdullahi Choopice ya yabawa Hon. Ibrahim Tanko Burra bisa ƙoƙarin da yake yi, yana mai cewa ya kamata a ƙara masa ƙarfin guiwa domin ya ci gaba da samar da ayyukan alheri da za su amfani al'ummar Burra baki ɗaya.

Burra Daily News

TALLESAWABA SHOP na farin cikin sanar da al'umma cewa muna ci gaba da samar da ingantattun kayayyaki a farashi mai sauƙi...
03/08/2026

TALLE

SAWABA SHOP na farin cikin sanar da al'umma cewa muna ci gaba da samar da ingantattun kayayyaki a farashi mai sauƙi.

A wurinmu zaku samu:

Saye da sayar da jarkokin manja da man gyada.

Dukkan nau'o'in kayan Trader.

Manja kwanti gwargwadon adadin da kuke buƙata.

Ku ziyarce mu a Shagon Sawaba Shop, cikin garin Burra, Unguwar Budugu, Ƙaramar Hukumar Ningi, Jihar Bauchi.

Domin ƙarin bayani ko yin oda, ku kira: 08087438516

SAWABA SHOP – Muna maraba da kowanne abokin ciniki daga ko ina a faɗin duniya

"Mutanen Burra za su ga dimbin alherin da ke tattare da kujerar Kansila idan na samu nasara" – Hon. Zaharaddeen InuwaƊan...
02/08/2026

"Mutanen Burra za su ga dimbin alherin da ke tattare da kujerar Kansila idan na samu nasara" – Hon. Zaharaddeen Inuwa

Ɗan takarar kujerar Kansilan Burra a ƙarƙashin jam'iyyar APC, Hon. Zaharaddeen Inuwa, ya bayyana cewa al'ummar Burra za su shaida dimbin alherin da ake iya samarwa ta hanyar kujerar Kansila idan Allah Ya ba shi nasarar lashe zaɓen da ke tafe.

Ya ce yana da tsare-tsare da manufofi da za su taimaka wajen bunƙasa ci gaban mazabar Burra tare da inganta walwalar al'umma.

Hon. Zaharaddeen Inuwa ya kuma yi kira ga matasa da sauran al'ummar mazabar Burra da su ba shi cikakken goyon baya da kuri'unsu domin samun damar aiwatar da waɗannan manufofi idan aka gudanar da zaɓen da ke tafe.

Burra Daily News

HON. ASHIRU ADAMU ZAHI YA NEMI GOYON BAYAN AL'UMMAR KYATA DA MAKWABTAN ƘAUYUKAMai neman takarar kujerar Kansilan Kyata a...
02/08/2026

HON. ASHIRU ADAMU ZAHI YA NEMI GOYON BAYAN AL'UMMAR KYATA DA MAKWABTAN ƘAUYUKA

Mai neman takarar kujerar Kansilan Kyata a ƙarƙashin jam'iyyar APC, Hon. Ashiru Adamu Zahi, ya yi kira ga al'ummar Kyata da sauran ƙauyukan da ke cikin mazabar da su ba shi cikakken goyon baya a zaɓe mai zuwa.

Hon. Ashiru Adamu Zahi ya bayyana cewa idan aka ba shi dama ya wakilci al'umma, zai yi aiki tuƙuru wajen bunƙasa yankin, kare muradun jama'a, tare da inganta walwala da ci gaban mazabar Kyata.

Ya kuma yi addu'ar Allah Ya ba wa yankin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba, sannan ya roƙi al'umma da su fito su mara masa baya domin cimma wannan buri.

Burra Daily News

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNAllah ya yi wa fitaccen mawaki Ƙosan Waƙa rasuwa bayan ya shafe lokaci yana fama da ra...
02/08/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah ya yi wa fitaccen mawaki Ƙosan Waƙa rasuwa bayan ya shafe lokaci yana fama da rashin lafiya.

Rahotanni sun nuna cewa marigayin ya rasu ne a yau Lahadi, bayan jinya da aka dade yana yi, lamarin da ya jefa iyalansa, masoyansa da al'ummar da s**a san shi cikin jimami.

👇🏽
Burra Daily News

SUNAYEN 'YAN TAKARAR SHUGABAN ƘASA NA KOWACE JAM'IYYA KAMAR YADDA HUKUMAR INEC TA FITARAction Alliance (AA) – Adekunle R...
02/08/2026

SUNAYEN 'YAN TAKARAR SHUGABAN ƘASA NA KOWACE JAM'IYYA KAMAR YADDA HUKUMAR INEC TA FITAR

Action Alliance (AA) – Adekunle Rufai Omoaje

African Action Congress (AAC) – Omoyele Sowore

African Democratic Congress (ADC) – Atiku Abubakar

Action Democratic Party (ADP) – Abbas-Bin Aliyu

All Progressives Congress (APC) – Bola Ahmed Tinubu

Allied Peoples Movement (APM) – Seyi Makinde

All Peoples Party (APP) – Yusuf Kabiru

Boot Party (BP) – Adenuga Sunday

Democratic League of Africa (DLA) – Memeh Samuel

Labour Party (LP) – Okereke Sunday Chibuzor

Nigeria Democratic Congress (NDC) – Peter Obi

National Democratic Party (NDP) – Okwori Ada Elizabeth Frederick

New Nigeria Peoples Party (NNPP) – Dikwa Suleiman Mohammed

National Rescue Movement (NRM) – Okereke Iken Esther

Peoples Democratic Party (PDP) – Sanata Sandy Onor

Peoples Redemption Party (PRP) – Donald Duke

Social Democratic Party (SDP) – Adebayo Adewole Ebenezer

Young Progressives Party (YPP) – Chukwu Anita Zugwai

Zenith Labour Party (ZLP) – Nwanyanwu Daniel Danerechukwu

Majiyar bayani: INEC
© Arise News247

Kuci gaba da kasancewa tare damu domin samun sahihan labarai 👇🏽
Burra Daily News

Address

Bauchi Ningi Burra Budugu
Bauchi

Telephone

+2347089421279

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Burra Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Burra Daily News:

Shortcuts

Share