KTG News Hausa

KTG News Hausa Wannan Company ne dake kawo Muku sahihan Labarai da S**a Shafi Nigeria, Arewa harma da Kasashen ketare cikin harshen Hausa.

Domin Kulla Alakar Kasuwanci ko Talla:
Zaku iya tuntubarmu a DM ko ta wannan number:
WhatsApp/Call ~
08036248621 or 07035173379

02/08/2026

KAI TSAYE: Yadda Kungiyar RUMFA-RUMFA ta karbi dandazon Al'ummar Cibiyayi, Maraba Gumai, Dambaja, Sandi-Galau zuwa tafiyar Hon. Ibrahim Muhammad Baba IMBA dan takarar Sanatan Bauchi Ta Arewa karkashin jagorancin Shugaban Kungiyar Baba Alaska Azare.

Part 8

LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda Dandazon Al'ummar Cibiyayi, Maraba Gumai, Dambaja da Sandi-Galau dake Zaki LG Sun Shiga Tafiy...
02/08/2026

LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda Dandazon Al'ummar Cibiyayi, Maraba Gumai, Dambaja da Sandi-Galau dake Zaki LG Sun Shiga Tafiyar Hon. Ibrahim Muhammad Baba IMBA.

Kungiyar RUMFA-RUMFA Youth Mobilization Katagum Zone karkashin jagorancin Baba Alaska Azare ta karbi dandazon al'umma daga yankunan Cibiyayi, Maraba Gumai, Dambaja da Sandi-Galau dake Zaki LG, wadanda s**a bayyana aniyarsu ta shiga tafiyar Hon. Ibrahim Muhammad Baba (IMBA), mai neman kujerar Sanatan Bauchi Ta Arewa.

A yayin taron karbar sabbin mambobin, shugaban kungiyar, Baba Alaska Azare, ya yi maraba da su tare da bayyana cewa hadewar al'umma daga sassa daban-daban na nuna karuwar karbuwa da goyon bayan da tafiyar IMBA ke samu a fadin mazabar Bauchi Ta Arewa.

Ya kuma bukaci sabbin mambobin da su kasance masu hadin kai, da kuma ci gaba da wayar da kan al'umma kan muhimmancin wayar da Al'ummar kan nagartar Hon. IMBA

Wakilan yankin sun bayyana cewa sun yanke shawarar mara wa Hon. Ibrahim Muhammad Baba (IMBA) baya ne saboda irin manufofin da s**a ce suna da yakinin za su kawo ci gaba ga yankin Bauchi Ta Arewa.

KTG News Hausa

02/08/2026

KAI TSAYE: Yadda Kungiyar RUMFA-RUMFA ta karbi dandazon Al'ummar Cibiyayi, Maraba Gumai, Dambaja, Sandi-Galau zuwa tafiyar Hon. Ibrahim Muhammad Baba IMBA dan takarar Sanatan Bauchi Ta Arewa karkashin jagorancin Shugaban Kungiyar Baba Alaska Azare.

Gwamna jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi ganawar ƙarshe da gawar Mawaƙi Kosan Waƙa
02/08/2026

Gwamna jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi ganawar ƙarshe da gawar Mawaƙi Kosan Waƙa

HOTUNA: Yadda Ango Aminu M. Ahmad (AMINU SAIRA) Da Amarya Maryam Mahmud Muhammad Tare Da Naziru Sarkin Waka S**a Kai Ziy...
02/08/2026

HOTUNA: Yadda Ango Aminu M. Ahmad (AMINU SAIRA) Da Amarya Maryam Mahmud Muhammad Tare Da Naziru Sarkin Waka S**a Kai Ziyara Ga Mai Martaba Sarkin Katagum Bayan Ɗaurin Aure

Bayan an ɗaura auren Darakta Aminu M. Ahmad (Aminu Saira) da Maryam Mahmud Muhammad, sabbin ma'auratan sun kai ziyarar girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Katagum a fadarsa da ke Azare.

A yayin ziyarar, fitaccen mawaki Naziru Sarkin Waka ya kasance tare da Ango Aminu M. Ahmad (Aminu Saira) da Amarya Maryam Mahmud Muhammad, inda s**a gabatar da gaisuwa tare da neman albarka da addu'a daga Mai Martaba.

KTG News Hausa.

📷 Chief Editor

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.Allah ya yi wa fitaccen mawaƙin siyasa Muhammad Buhari, wanda aka fi sani da Kosan Wa...
02/08/2026

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.

Allah ya yi wa fitaccen mawaƙin siyasa Muhammad Buhari, wanda aka fi sani da Kosan Waka rasuwa.

Kosan Waka ya rasu ne bayan ya sha fama da rashin lafiya.

TIRKASHI: Majiyoyi masu karfi na bangaren Damben Gargajiya sun tabbatar da cewa tun shekaranjiya da Dan Dambe Samgwam ya...
01/08/2026

TIRKASHI: Majiyoyi masu karfi na bangaren Damben Gargajiya sun tabbatar da cewa tun shekaranjiya da Dan Dambe Samgwam ya sumar da Ali K***n Bello a Damben 250,000 na jihar Sokoto har yanzu Ali K***n Bello na Asibiti bai Farfado ba.

01/08/2026

KARATUN LITTAFIN AL-WAJEEZ

DARASI NA
185
Duk Karatun Al-Wajeez Na Baya
https://sautulhikma.com/book/32

Tare Da :-- Dr. Magaji Baffah Sulaiman Azare

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

DAGA MASALLACIN ALHAJI IBRAHIM BATURE (KAFIN KUKA KUSA DA BAKIN PRISON SERVICE)

RANAR ASABAR
1448
2026

WhatsApp:
https://chat.whatsapp.com/DQn50hCkpRS85h5QydmbOp

Telegram:
https://t.me/+hvbMBxpG5HsyNzM8

Domin bada gudumawar ka wajen tafiyar da ayyukan sautul Hikma

Account Number.8246707333
Account Name.Sautul Hikma Nigeria
Bank Name.Monie point

Ayi sauraro lafiya.

Ku cigaba da kasancewa da Sautul Hikma a wadannan kafafen sada zumuntar domin samun karatuttukan Maluman Sunnah a saukake.

Radio: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.sautulh.radio

FSautul Hikma Nigeriaulhikmang

Telegram:
https://t.me/sautul_hikma

Whatsapp:
https://chat.whatsapp.com/CbrsShDVbCzBbL4m8dh7iO

YouTube:
https://youtube.com/?si=i8rnjdlqmElL1PRn

YouTube:
https://youtube.com/.hikmatv?si=ZSkCzRLWCWFCk4Xk

Twitter:
https://twitter.com/sautulhikmang

Website:
https://sautulhikma.com

Sautul Hikma Nigeria Karatuttukan Maluman Sunnah a Saukake.

Salim Yaya Azare

JIBWIS SOCIAL MEDIA KATAGUM

YADDA ƊALIBAN ASCOE AZARE S**A GUDANAR DA SHAGALIN CULTURAL DAY NA SHEKARAR 2026.Ɗaliban Kwalejin Ilimi ta Aminu Saleh C...
01/08/2026

YADDA ƊALIBAN ASCOE AZARE S**A GUDANAR DA SHAGALIN CULTURAL DAY NA SHEKARAR 2026.

Ɗaliban Kwalejin Ilimi ta Aminu Saleh College of Education (ASCOE), Azare, sun gudanar da bikin Cultural Day na shekarar 2026 cikin nishadi da armashi, inda s**a baje kolin al'adu da kabilu daban-daban na Najeriya.

Bikin ya gudana ne a harabar makarantar tare da halartar ɗalibai, malamai da sauran baƙi, inda aka gabatar da al'adun gargajiya ta hanyar sanya kayan gargajiya, raye-raye, wake-wake, abinci na gargajiya da kuma wasu wasannin al'adu da s**a nuna bambancin al'ummomin ƙasar nan.

Mahalarta taron sun bayyana cewa irin wannan biki na taimakawa wajen ƙarfafa haɗin kai, fahimtar juna da kuma bunƙasa al'adun Najeriya tsakanin matasa, tare da ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kan al'umma.

© KTG News Hausa

Fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara, ya ce bai yi wa kowa laifi ba a sabuwar wakarsa mai taken "Malam Ka Yi Raw...
01/08/2026

Fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara, ya ce bai yi wa kowa laifi ba a sabuwar wakarsa mai taken "Malam Ka Yi Rawa", yana mai cewa bai ambaci sunan wani mutum a cikin wakar ba.

Rarara ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da DCL Hausa, inda ya ce manufarsa ita ce yabon ɗan takarar gwamnan jam'iyyarsa ta APC, ba tare da yin nuni ga wani mutum kai tsaye ba.

A cewarsa, "Riga na dinka ba wuya; duk wanda ya ga ta masa dai-dai, sai ya saka." Ya jaddada cewa wakar ba ta ambaci sunan kowa ba, don haka bai ga cewa ya aikata wani laifi ba.

Sai dai, tun bayan fitar wakar, ta janyo muhawara a tsakanin al'umma. Wasu na ganin cewa wakar ta yi nuni da fitaccen malamin addinin Musulunci kuma ɗan takarar gwamna na jam'iyyar PDP a Jihar Gombe, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami, duk da cewa ba a ambaci sunansa kai tsaye ba.

Masu wannan ra'ayi sun yi zargin cewa wasu kalaman da ke cikin wakar na iya zama cin mutunci ko bata suna, inda suke ganin an danganta su da batutuwa kamar shan miyagun ƙwayoyi da ta'addanci.

A gefe guda kuma, akwai masu kare Rarara da ke cewa tunda bai ambaci sunan kowa ba a wakar, bai kamata a ɗauki cewa ya yi wa wani mutum nuni kai tsaye ba.

Lamarin dai na ci gaba da haifar da muhawara a kafafen sada zumunta, inda mutane ke bayyana ra'ayoyinsu mabambanta kan ma'anar wakar da tasirinta.

Shin ku mene ne ra'ayin ku?

Address

Masallacin Idi Street Azare
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KTG News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KTG News Hausa:

Shortcuts

Share