KTG News Hausa

KTG News Hausa Wannan Company ne dake kawo Muku sahihan Labarai da S**a Shafi Nigeria, Arewa harma da Kasashen ketare cikin harshen Hausa.

Domin Kulla Alakar Kasuwanci ko Talla:
Zaku iya tuntubarmu a DM ko ta wannan number:
WhatsApp/Call ~
08036248621 or 07035173379

31/05/2026

TALLA: Sport Arena Mai girman 3,348 square meters.

Farashi Mai Sauki, wajen zai dace da Gina wajen shakatawa, wasanni da sauran su.

Location: Fatara, Azare Bauchi

Call/WhatsApp: 08036248621

Liverpool Ta Sallami Kocinta Arne SlotRahotanni sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Liverpool F.C. ta sallami mai ...
31/05/2026

Liverpool Ta Sallami Kocinta Arne Slot

Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Liverpool F.C. ta sallami mai horas da 'yan wasanta, Arne Slot, daga mukaminsa na kociyan kungiyar.

Wani matashi mai suna Aminu Ada Azare ya mayar da martani kan kalaman Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Katagum, Hon. A...
31/05/2026

Wani matashi mai suna Aminu Ada Azare ya mayar da martani kan kalaman Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Katagum, Hon. Auwalu Abdu Gwalebe, inda ya bukace shi da ya hakura da sake neman komawa Majalisar Wakilai domin bai wa wani sabon wakili damar gwada nasa salon wakilci.

A cikin martanin da ya wallafa, Aminu Ada Azare ya ce yana ganin akwai bukatar a bawa wasu dama domin su ma su je Majalisa su gwada abin da za su iya yi wa al'umma.

Ya kuma yi ikirarin cewa duk da kasancewar Hon. Gwalebe gogaggen dan majalisa ne, an hana shi wasu kudaden da ake warewa ta fuskar kasafin kudi (Budget), yana mai cewa hakan ya kamata ya zama wani dalili na bai wa wani sabon wakili damar gwada nasa kokarin.

Sai dai Aminu ya jaddada cewa ra'ayinsa ne na siyasa, yana mai kira ga masu ruwa da tsaki da al'ummar mazaba su yi nazari kan wanda ya dace ya wakilce su a zaben da ke tafe.

KTG News Hausa

31/05/2026

Tattaunawa ta musamman tare da Hon. Auwalu Abdu Gwalebe dan majalisar tarayya mai wakiltar Katagum.

Cikakken shirin yananan tafe.

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Katagum, Hon. Auwalu Abdu Gwalebe, ya bayyana cewa komawarsa Majalisa...
31/05/2026

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Katagum, Hon. Auwalu Abdu Gwalebe, ya bayyana cewa komawarsa Majalisar Wakilai zai kara wa mazabar Katagum karfi da damar anfani a zauren Majalisar Tarayya, kasancewar shi ba sabon shiga bane a harkokin majalisa.

Yayin wata hira da KTG News Hausa, Hon. Gwalebe ya ce ya sake tsayawa takarar dan majalisar ne domin ya ci gaba da bibiyar muhimman kudurorin da ya gabatar, musamman kudirin neman kirkirar Jihar Katagum wanda ke cikin shirye-shiryen da ake yi na kara yawan jihohi a Najeriya.

Ya kara da cewa dawowarsa Majalisa zai taimaka wajen ci gaba da wakiltar muradun al'ummar mazabar tare da tabbatar da an cimma manufofin da aka fara aiwatarwa.

Dan Majalisar ya kuma bayyana cewa zai zama koma baya idan aka zabi wanda zai je Majalisar a karon farko, domin a cewarsa irin wadannan sabbin 'yan majalisa kan dauki lokaci kafin su fahimci yadda harkokin majalisa ke gudana, a lokacin da muhimman abubuwa s**a riga s**a yi nisa.

Hon. Gwalebe ya ce wannan ne ya sa ya ga dacewar sake neman amincewar al'ummar Katagum domin ya ci gaba da wakiltarsu da kuma kare muradunsu a Majalisar Tarayya.

KTG News Hausa

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Katagum, Hon. Auwalu Abdu Gwalebe, ya bayyana cewa sun wallafa wani l...
31/05/2026

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Katagum, Hon. Auwalu Abdu Gwalebe, ya bayyana cewa sun wallafa wani littafi mai suna "3 Years Pictorial Achievement of Hon. Auwalu Abdu Gwalebe" wanda ya kunshi muhimman ayyukan ci gaba da ya gudanar a mazabarsa cikin shekaru uku da s**a gabata.

Hon. Gwalebe ya bayyana hakan ne yayin wata hira ta musamman da KTG News Hausa, inda ya ce littafin ya tattara ayyukan raya kasa da cigaban al'umma da ya aiwatar a fadin gundumar Katagum.

Ya kara da cewa wannan littafi shi ne kashi na farko (Volume 1), yayin da ake shirin fitar da kashi na biyu wanda zai kunshi karin ayyukan ci gaba sama da guda 130 da aka aiwatar domin amfanin al'ummar mazabar.

Dan Majalisar ya ce manufar wallafa littafin ita ce domin bai wa al'umma damar ganin irin nasarori da ayyukan da aka gudanar tare da samar da cikakken tarihi na wakilcinsa.

KTG News Hausa

Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi ta bukaci dalibai da su kasance masu neman nasara a karatunsu kamar yadda kungiyar kwal...
31/05/2026

Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi ta bukaci dalibai da su kasance masu neman nasara a karatunsu kamar yadda kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain ke samun nasarori a fagen kwallon kafa, tana mai cewa ya kamata su kasance masu cin jarabawa akai-akai tare da samun sakamako mai kyau.

A cikin wani sako da ta wallafa, ma’aikatar ta ce ba ta son ganin dalibai suna fuskantar rashin nasara a fannin ilimi, inda ta yi ishara da kungiyar Arsenal F.C. a matsayin misali na kungiyar da ba ta kai ga samun manyan kofuna kamar yadda magoya bayanta ke fata ba a wasu lokuta.

DA DAMI-DUMI: Peter Obi ya ayyana Kwankwaso a matsayin wanda zai masa mataimakin takarar shugabancin Nijeriya a jam’iyya...
30/05/2026

DA DAMI-DUMI: Peter Obi ya ayyana Kwankwaso a matsayin wanda zai masa mataimakin takarar shugabancin Nijeriya a jam’iyyar NDC

Me zaku ce game da wannan hadi (OK)?

DA DAMI-DUMI: PSG ta doke Arsenal a bugun fenariti bayan da aka tashi 1-1 a minti 120.Wannan ne karo na biyu da ƙungiyar...
30/05/2026

DA DAMI-DUMI: PSG ta doke Arsenal a bugun fenariti bayan da aka tashi 1-1 a minti 120.

Wannan ne karo na biyu da ƙungiyar ta lashe kofin bayan lashewa a kakar wasan da ta gabata.

Yaya kuka ga wasan?

Arsenal Ko PSG; Wa Kuke Yi Wa Fatan Nasara A Karawar Su Na Daren Yau Asabar?
30/05/2026

Arsenal Ko PSG; Wa Kuke Yi Wa Fatan Nasara A Karawar Su Na Daren Yau Asabar?

Address

Masallacin Idi Street Azare
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KTG News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KTG News Hausa:

Share