
14/07/2025
Dr. Musa Babayo (Talban Katagum) Ya Mika Sakon Ta’aziyya Kan Rasuwar Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.
Dr Musa Babayo, ya bayyana alhini da jimamin sa kan rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Dr Talba, ya bayyana Buhari a matsayin jagora na kwarai wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Najeriya hidima da kishin kasa.
Allah ya gafarta masa, ya yafe masa laifuffukansa, ya kuma saka masa da Aljannatul Firdaus.
Ya kuma mika ta’aziyya ga iyalan marigayin da daukacin al’ummar Najeriya, yana addu’ar Allah ya basu hakurin jure wannan babban rashi.