01/10/2025
JAWABIN MAI GIRMA BOLA AHMED TINUBU, GCFR, SHUGABAN TARAYYAR NIGERIA KAN CIKAR KASAR SHEKARU SITTIN DA BIYAR DA SAMIN `YANCIN-KAI, (1, OCTOBER 2025)
'YAN UWANA 'YAN NIJERIYA!
Yau ce ranar da wannan kasa tamu mai girma ke cika shekaru 65 da samun 'yancin kai. A yayin da muke bitar muhimmancin wannan rana da tuna yadda kasarmu ta faro tun daga rana irin ta yau, wato 1 ga watan Oktoba, shekarar 1960, ranar da gwarazan iyayenmu s**a karbi shaidar samin mulkin cin gashin kai daga turawan mulkin mallaka, dole ne mu tuna da sadaukarwarsu, da kwazonsu, da ma babban burinsu na samun tsayayyiya, wadatacciya kuma dunkulalliyar Nijeriya, wacce za ta jagoranci Afirka kana ta zama yar manuniya ga sauran kasashen duniya.
2 Gwarazan gwagwarmayar kafa kasar mu maza da mata—irin su Herbert Macaulay, Dr. Nnamdi Azikiwe, Sir Abubakar Tafawa Balewa, Chief Obafemi Awolowo, Sir Ahmadu Bello, Margaret Ekpo, Anthony Enahoro, Ladoke Akintola, Michael Okpara, Aminu Kano, Funmilayo Ransome-Kuti, da sauran 'yan kishin kasa—sun yi Imani da cewa a matsayin Najeriya na kasar bakake mafi girma a duniya, Allah Ya kaddara mata jagorancin dukan bakaken fata a duniya.
3. Tabbas tsawon shekaru da dama, yancin kanmu ya fuskanci kalubale mai tsanani a fannin zamantakewa, tattalin arziki, da siyasa, sai dai duk da haka mun yi nasara. Ta yiwu ba mu cika wa magabatanmu dukkan manyan burikansu ba, amma ba mu juya wa muradunsu baya ba, domin a cikin shekaru 65 da samun 'Yancin kanmu, mun samu ci gaba mai tarin yawa a fannonin da s**a hada da ci gaban tattalin arziki da hadin kan yan kasa.
Ko shakka babu, daga shekarar 1960 zuwa yanzu,tattalin arzikinmu ya samu ci gaba sosai.
4. Koda yake abu ne me sauki ga idanun masu kallon abu ta bangare daya su kasa hango irin ci gaban da aka samu, sai dai ya zama dole mu fahimci irin abubuwan ci gaba masu muhimmanci da kasar mu ta rabauta da su, har ma mu yi murna. 'Yan Nijeriya a yau suna da damar samun ingantaccen ilimi da kiwon lafiya fiye da na 1960. A lokacin samun 'Yancin kai, Nijeriya tana da makarantun sakandare 120 tare da yawan dalibai kusan 130,000. Amma bayanai sun nuna cewa, a karshen shekarar 2024, akwai makarantun sakandare sama da 23,000 a kasar mu. A lokacin 'Yancin kai, muna da Jami'ar Ibadan da Kwalejin Fasaha ta Yaba ne kawai a matsayin cibiyoyin manyan makarantun Nijeriya. A karshen shekarar da ta gabata, akwai jami'o'i 274, polytechnics 183, da Kwalejin Ilimi 236 a Nijeriya, wadanda s**a hada da cibiyoyin Gwamnatin Tarayya, na Jihohi, da na masu zaman kansu. Tabbas mun sami gagarumin ci gaba a kowane fanni na rayuwarmu daga samin 'Yancin kai zuwa yanzu - a fannin kiwon lafiya, samar da ababen more rayuwa, ayyukan kudi, masana'antu, sadarwa, fasahar zamani, jiragen sama, tsaro, da sauransu.
5. A cikin shekaru 65, kasarmu ta dandana zaki da dacin kasancewarta kasa, k**ar yadda yake iya faruwa ga kowace kasa da jama'arta. Mun dandana yakin basasa, mun dandana mulkin soja, kana mun rayu a cikin manyan matsalolin siyasa. Sai dai babu daya daga cikin wadannan kalubale da jarumtakar mu da juriyar mu basu ga bayansu ba. Ko da yake wasu lokuta masu adawa da ci gabanmu da al`adunmu kan yi wa tsarinmu da dankon zumuncinmu zagon kasa, hakan ba zai hana mu ci gaba da kokarin samar da dausayin da kowane dan Nijeriya zai rayu cikin walwala, hadafi da cikan burinsa ba.
6. 'Yan Uwana 'Yan Kasa Na gari, karo na uku kenan da sami damar yi muku jawabi a ranar cika shekaru da samin 'Yancin kanmu tun bayan da na zama Shugabanku a ranar 29 ga Mayu, 2023. A cikin watanni 28 da s**a gabata na gwamnatina, na yi koyi da jajircewar iyayen kasarmu, da sauran shugabannin da s**a gabace ni wajen yin tsayin daka a kan aikin gina kasa da bai kammala ba.
7. Da muka hau mulki, gwamnatinmu ta gaji marilin tattalin arziki da ke gab da kushewa wanda ya samo asali daga shekaru da dama na karkatar da manufofin kasafin kudi da rashin daidaito, wanda ya yi lahani na gaske ga ci gaban mu. A matsayin sabuwar gwamnati, muna da zabi mai sauki: Ko dai mu ci gaba da gudanar da al'amura k**ar yadda aka saba muna kallo kasarmu na ci gaban me hakon rijiya, ko kuma mu shiga aikin gyara tukuru cikin kau da kai da juriya. Gaskiya mun zabi hanyar gyara. Mun zabi jin dadin gobe da jibi akan na yau kawai. Mun dauki matsaya mai wahala, amma kasa da shekara uku ta fara samar da da mai ido.
8. Duk don mu dora kasar mu akan doron manufa muka kawo karshen tallafin man fetur da ke cike da cin hanci da rashawa, haka ma a fannin hada-hadar kudaden kasashen waje mun toshe kafar da ke takaita walwalar tattalin arzikin ga amfanin 'yan tsiraru, su hana talakawa komai daga dukiyar kasarmu. Gwamnatinmu ta sake mayar da tattalin arzikin zuwa hanyar da za ta wadaci kowa da kowa, ta hanyar karkatar da kudi don samar da ilimi, kiwon lafiya, tsaron kasa, noma, da muhimman ababen more rayuwa da habaka tattalin arziki, k**ar samar da manyan hanyoyi, wutar lantarki, da samar da jarin yau da kullun. Wadannan tsare-tsare, su ne za su inganta rayuwar 'yan Nijeriya gaba daya. Asak**akon dabarun da muka dauka na dakile manyan matsaloli, a yanzu daga Gwamnatin Tarayya zuwa gwamnatin Jihohi, kai har da Kananan Hukumomi, babu wanda bai sami isassun kula da jama`arsa a kowane mataki ba.
9. Ya ku 'Yan uwa `Yan Nijeriya, ba mu da sauran lokaci. Dole ne mu tashi tsaye mu gina hanyoyin da kasar mu ke bukata, mu gyara wadanda s**a lalace, kana mu gina makarantun da 'ya'yanmu za su je da kuma asibitocin da za su kula da jama'armu., Dole ne mu yi shiri don zuri'ar da za ta zo bayanmu. Ta dalilin kasa zuba dukiyar kasar mu a inda ya dace tun shekaru aru-aru, mun wayi gari ba mu da wadatacciyar wutar lantarki da za ta kunna masana'antunmu da gidajenmu a yau, ba mu da wadatar da za mu gyara hanyoyinmu da s**a lalace, ko kuma gina tashoshin jiragen ruwa, ko na kasa, kai har da filayen jiragen sama da zasu iya jera kafada da mafi kyau a duniya. Gwamnatinmu bata ga ta zama ba, ta dukufa gyara abubuwa.
10. Ina farin cikin sanar da ku cewa a karshe mun shawo kan manyan matsalolinmu. Mafiya munin sun wuce, ina fada ina kara fadi. kowane tsanani na tare da sauki. Na yaba wa juriyar da kuka nuna. Ina tabbatar muku da cewa, hadin kan da kuka bani, ya samar min da kwarin gwiwar da ba zan gushe ba ina aiki tukuru, har sai na kai kasarmu tudun-mun tsira.
11. A karkashin jagorancinmu, tattalin arzikinmu yana farfadowa cikin hanzari, kuma sauye-sauyen da muka faro shekaru biyu da s**a gabata suna bada sak**ako mai ma`ana. Alkaluman kudin shiga na zango na biyu na shekarar 2025 ya nuna karuwa da kashi 4.23 cikin dari—wanda shine ci gaba mafi sauri a Nijeriya a cikin shekaru hudu—har ma ya zarce kashi 3.4 da Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) ya yi hasashen za a samu. Hauhawar farashin kayayyaki ya ragu zuwa kashi 20.12% a watan Agusta 2025, abinda bai taba faruwa ba a cikin shekaru 3 da s**a gabata. Gwamnati na aiki tukuru don habaka noman ababen masarufi na yau da kullun don tabbatar da samar da abinci da zai rage farashin abinci.
12. A cikin shekaru biyu da s**a gabata na gwamnatinmu, mun cimma muhimman nasarori 12 na tattalin arziki sak**akon aiwatar da ingantattun manufofinmu na kasafin kudi da na kudi: ga su k**ar haka:
Mun sami karin kudaden shiga da ga albarkatun da ba na man fetur ba, inda muka cimma burinmu na 2025 kafin watan Agusta ta hanyar samin fiye da Naira Tiriliyan 20, wannan wani abin ya shiga tarihi ne. A watan Satumba 2025 kadai, mun tara Naira Tiriliyan 3.65, wanda ya ninka adadin da aka tara a watan Mayu 2023 da kashi 411%. Mun farfado da darajar Kasafin Kudi: sabon tsarin biyan bashin da muke bi idan aka kwatanta da kudaden shiga ya ragu sosai daga kashi 97% zuwa kasa da kashi 50%. Mun biya "Ways and Means" da ke barazana ga kwanciyar hankalin tattalin arzikinmu har ma da haifar da hauhawar farashi. Bayan cire tallafin man fetur mai cike da cin hanci da rashawa, mun karkata Triliyoyin Naira zuwa ga ainahin hannayen jarin tattalin arziki da zai inganta rayuwar yan kasa marasa galihu.
Mun dada garajar Asusun Ajiyar Kasa fiye da yadda yake a shekaru uku da s**a gabata. A yanzu asusun ajiyar mu na waje ya karu zuwa Dala Biliyan $42.03 a wannan watan Satumba—wanda shine mafi girma tun 2019.
Harajinmu na kudaden shiga ya tashi daga kaso 10 zuwa kashi 13.5, kuma ana sa ran darajar za ta karu idan sabuwar dokar haraji ta fara aiki a watan Janairun badu. Sai dai a sani! Dokar haraji ba ta nufin kara wa masu biyan haraji nauyi, sai ma ragin harajin da ake Shirin yi wa masu karamin karfi, manufar dokar ita ce tattaro kudaden harajin tun daga tushe don gina Nijeriyar da muke mafarki.
Yanzu mu ne kan gaba a masu fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje (Net Exporter): Nijeriya ta rubanya karin cinikayya (trade surplus) har sau biyar a jere. Yanzu muna sayar da abubuwa da yawa ga duniya fiye da yadda muke saya, wani canji mai mahimmanci wanda ke karfafa kudinmu da samar da ayyukan yi a gida. Karin cinikayyar Nijeriya ya karu da kashi 44.3% a Q2 2025 zuwa ₦7.46 Tiriliyan ($4.74 Biliyan), wanda shine mafi girma a cikin kusan shekaru uku. Kayan da aka kera a Nijeriya kuma aka fitar sun karu da kashi 173%. Kayayyakin da ba danyen mai ba, sune kashi 48 a bangaren cinikayyar fitar da kayanmu, idan aka kwatanta da fitar da mai, wanda ya kai kashi 52%. Wannan yana nuna cewa mun fara raba tattalin arzikinmu da tushen kudin waje da ake samowa daga danyen mai da iskar gas.
Samar da danyen mai ya karu daga ganga kasa da milyan daya a watan Mayun 2023 zuwa ganga miliyan 1.68 a rana. Wannan karin ya samu ne sak**akon ingantaccen tsaro, da sabbin hannayen jari, da kula da hakkokin masu ruwa da tsaki a yankin Neja Delta. Bugu da kari, kasar ta samu gagarumin ci gaba ta hanyar tace man fetur (PMS) a cikin gida a karon farko cikin shekaru arba'in. Haka kuma ta kafa kanta a matsayin jagorar fitar da man jirgin sama a nahiyar Afirka.
Naira ta farfado daga rikta-riktar da ta sami kanta a tsakanin shekarar 2023 da ta 2024. Gibin da ke tsakanin farashin gwamnati da na kasuwar bayan fage ya ragu ainun, biyo bayan gyare-gyaren FX da sabbin kudaden shiga da ke rufa mata baya. Kazamar ribar da ake ci a hada-hadar Naira a baya yanzu ta zama tarihi. Kazalika farashin Nairar mu ya dena dogara da farashin danyen mai.
A karkashin shirye-shiryen zuba jari na zamantakewa don tallafa wa iyalai masu rangwamen gata a Nijeriya, an raba Naira Biliyan 330 ga iyalai miliyan takwas, akasarinsu sun karbi ko dai kashi daya ko biyu na kashi uku na Naira 25,000 kowanne.
An farfado da hakar ma`adinin kwal sosai daga raguwar da yayi na kashi 22% a Q1 a baya zuwa karuwar kashi 57.5% a Q2, inda ya zama kan gaba cikin jerin ma`aninan Najeriya masu saurin murmurewa. Hakan na nufin sashin hakar ma'adanai ya sami gurbin zama mai muhimmanci a cikin tattalin arzikin kasarmu, ma`adinan da ke karkashin kasarmu sun zama kashin bayan samar da kayayyaki masu daraja.
Gwamnati na ci gaba da aikin fadada kayayyakin more rayuwa a bangaren sufuri a duk fadin kasar, wanda s**a hada da samar da jiragen kasa, manyan hanyoyi, filayen saukar jiragen sama, da tashoshin jiragen ruwa. Sufurin jirgin kasa da na ruwa, duk sun karu da fiye da 40% da 27%, bi da bi. Aikin layin dogo na Kano-Kastina-Maradi Standard Gauge mai tsawon kilomita 284 da layin dogo na Kaduna-Kano suna gab da kammalawa. Haka ma aikin titin Lagos-Calabar Coastal Highway da Sokoto-Badagry Highway duk sun yi nisa. Majalisar Zartaswa ta Tarayya kwanan nan ta amince da Dala Biliyan $3 don kammala Aikin Jirgin Kasa a gabashin kasar nan.
Duniya ta fara farga da kokarinmu. Hukumomin sa ido kan tattalin arziki da bayar da lamuni na kasa da kasa sun fara sauya Kallon da da suke wa Nijeriya a baya, yanzu suna gamsuwa da ingantattun matakanmu na tattalin arziki. Kasuwancinmu na hannun jari yana samun ci gaba da ba a taba gani ba, inda ya tashi daga ma'aunin index na 55,000 a watan Mayu 2003 zuwa 142,000 a ranar 26 ga Satumba, 2025.
A taron kwamitin manufofin kudi (MPC) na baya-bayan nan, Babban Bankin ya rage kudin ruwa a karon farko a cikin shekaru biyar, yana nuna amincewa da kwanciyar hankali na tattalin arzikin kasarmu.
TSARO
13. Muna aiki tukuru don inganta tsaron kasa, don tabbatar da cewa tattalin arzikinmu ya samu ingantaccen ci gaba. Dakarun sojojinmu da sauran hukumomin tsaro suna aiki ba dare ba rana, suna sadaukar rayuwarsu don kiyaye rayukanmu da dukiyoyin mu. Kuma suna cin nasara a yakin da muke yi da ta'addanci, fashi, da ma sauran manyan laifuka. Muna ganin nasarorin su a cikin jinin su da gumin su don kawar da Ta'addancin Boko Haram a Arewa maso Gabas, ta'addancin IPOB/ESN a Kudu maso Gabas da fashi da garkuwa da mutane. Dole ne mu ci gaba da yaba musu da jinjinawa jaruntakarsu a matsayinmu na al'ummar da ke yaba kyauta da tukuici. Zaman lafiya ya dawo ga daruruwan al'ummominmu da aka 'yanta a Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas, kuma dubban mutanenmu sun dawo gida lafiya.
MATASA
14. Ga Sakona zuwa ga matasanmu. Ku ne kan gaba kuma kune mafi girman baiwar da Allaha yayi wa wannan kasa mai albarka. Dole ne ku ci gaba da yin manyan mafarkai, ku gina manyan tunani, ku kirkiri sabbin abubuwa, ku ci nasara a fannoni daban-daban na kimiyya, fasaha, wasanni, da kuma bangaren kere-kere. Gwamnatinmu, zata ci gaba da zuba kudaden da za su kera muku fikafikai don ku tashi sama a ku yi gudun wuce-sa`a. Mun kirkiri NELFUND don tallafa wa dalibai da lamuni don karatunsu. Kusan dalibai 510,000 a cikin jihohi 36 da FCT sun amfana da wannan shiri, wanda ake gudanarwa a manyan makarantu 228. Ya zuwa ranar 10 ga Satumba, jimlar lamunin da aka raba ya kai Naira Biliyan 99.5, yayin da kudin kula da walwalar rayuwa ya kai Naira Biliyan 44.7.
15. Credicorp, wani Shirin garabasa ne daga gwamnatinmu, ya bai wa 'yan Nijeriya kimanin 153,000 lamuni mai rahusa har na Naira Biliyan 30 don siyan motoci, mak**ashin hasken rana, kayan kyale-kyalen gida, na'urorin dijital, da sauran su.
16. YouthCred, din nan da na yi alkawarin bayarwa a watan Yuni da ta gabata, shi ma yanzu ya tabbata, inda dubban 'yan NYSC a yanzu suke cin moriyar bashi na Consumer Credit don sake daidaita komadarsu bayan kammala hidimar kasa.
17. A karkashin Ajandar Sabunta Fata Nagari (Renewed Hope Agenda), mun yi alkawarin gina Nijeriya inda kowane matashi, ko daga wane bangare ya fito, yana da damar samin ingantacciyar rayuwa—saboda haka shirin Zuba Jari a Kasuwancin Dijital da Kere-kere na (iDICE). Wanda bankin Masana'antu (Bank of Industry) ke jagorantar tare da hadin gwiwar Bankin Raya Afirka (African Development Bank), da Hukumar Raya Faransa (French Development Agency), da Bankin Musulunci (Islamic Development Bank). Wannan shiri yana gab da fara aiwatarwa. A cikin shekaru biyu da s**a gabata, mun yi aiki tare da abokan huldanmu don kaddamar da shirin, wanda zai tallafa wa matasanmu da s**a fara aiki da masu mafarkin farawa, duk a fannin fasaha da kirkire-kirkire.
SAKON KYAUTATA FATA
18. Ya ku 'Yan Nijeriya 'Yan Uwana! Ko yaushe ina nanata cewa bana musa cewa, sauye-sauyen tattalin arzikin gwamnatina sun zo da radadi, amma na wucin gadi ne. Mummunan tasirin hauhawar farashi da karuwar kudin akan ababen yau da kullun sun kasance babban abin damuwa ga gwamnatinmu. Sai dai, zabin da zai kai kasarmu ga fadawa cikin rikicin tattalin arziki ko dauwamammiyar fatara ba zabi ne me kyau ba. Ci gaban tattalin arzikinmu ya tabbatar da cewa sadaukarwarmu ba ta tafi a banza ba. Da ni da ku, muke kafa sabon harsashi da aka zubawa kankare, ba na tubalin toka ba.
19. Na lashi takobin ganin ma'aunin nasarar mu bai takaita ga alkaluman kididdigar tattalin arziki dake rubuce a zallar takarda ba, wannan karon sai mun gani a kasa, sai mun shaida shi a kwanon cin mu, sai mun gan shi a ingancin ilimin da 'ya'yanmu ke samu, sai mun shaida shi a wutar lantarkin gidajenmu, da tsaro rayuwakan al'ummominmu.
Bari in tabbatar muku da damarar da gwamnatinmu ta sha, na tabbatar da cewa albarkatun da muka ajiye da kuma kwanciyar hankali da muka gina an karkatar da su zuwa wadansu muhimman fannoni da s**a shafe ku s**a shafe mu. A yau, Gwamnonin jihohi da masu ikon cin gashin kai na kananan hukumomi suna iya haifar da karin ci gaba tun daga tushe.
20. Saboda haka, a sakon cika Shekaru 65 na 'Yancin kanmu, sakona shine Fata Nagari da aiki tukuru. Gwamnatin tarayya za ta ci gaba da yin nata kokarin don gyara matsalolin tattalin arzikinmu. Sauran aikinmu kuma shine ambulo fasahar samar da kayayyaki, kirkire-kirkire, da kasuwanci, k**ar yadda Ma’aikatar Cikin Gida ta yi da fasfunan tafiye-tafiye, ta hanyar saurin aiki da su. A wannan bangaren, ina kira ga kananan hukumomi da na jihohi da su yi aiki tare da mu don gina kasa. Mu mayar da Najeriya kasar masu samar da kayayyaki, ba wai masu saye kawai ba. Mu noma gonakinmu kuma mu gina masana'antu don sarrafa amfanin gonakinmu. Mu yi amfani da kayayyakin da aka kera a Nijeriya. Nijeriya ce farko. Mu biya harajinmu.
21. A karshe, ina kira da mu dage kafar wando mu k**a aiki, mu sake yarda da kasarmu, da karfin da take da shi da bai san iyaka ba.
22. Da Ikon Allah Maɗaukakin Sarki nake iya tabbatar muku cewa lokacin bayyanar sabuwar Najeriya, mai wadata, mai dogaro da kanta ya zo.
23. Ina taya mu murna da Cika Shekaru na 65 na 'Yancin Kai, Allah Ya albarkaci Jamhuriyar Tarayyar Nijeriya.
Amin.