KTG News Hausa

  • Home
  • KTG News Hausa

KTG News Hausa Wannan Shafi an kirkire shine domin kawo muku sahihan Labarai da S**a shafi Nigeria, Arewa harma da kasashen ketare.

Dr. Musa Babayo (Talban Katagum) Ya Mika Sakon Ta’aziyya Kan Rasuwar Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.Dr Musa Babay...
14/07/2025

Dr. Musa Babayo (Talban Katagum) Ya Mika Sakon Ta’aziyya Kan Rasuwar Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.

Dr Musa Babayo, ya bayyana alhini da jimamin sa kan rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Dr Talba, ya bayyana Buhari a matsayin jagora na kwarai wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Najeriya hidima da kishin kasa.

Allah ya gafarta masa, ya yafe masa laifuffukansa, ya kuma saka masa da Aljannatul Firdaus.

Ya kuma mika ta’aziyya ga iyalan marigayin da daukacin al’ummar Najeriya, yana addu’ar Allah ya basu hakurin jure wannan babban rashi.

Yadda Jadawalin Shirye-Shiryen Jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari Zai Kasance1-An ayyana ranar Talata a mat...
14/07/2025

Yadda Jadawalin Shirye-Shiryen Jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari Zai Kasance

1-An ayyana ranar Talata a matsayin ranar hutu a Najeriya don makokin Marigayin

2-An kafa Kwamitin Manyan Jami'an gwamnati don tsara jana'izar girmamawa ga tsohon shugaba Buhari wanda sakataren gwamnatin tarayya Sen. George Akume ya jagoranta.

3-An dage taron Majalisar Zartarwa ta Kasa daga gobe zuwa juma'a don zaman makoki

4 An umarci mambobi 25 na Majalisar Zartarwar da su wuce Daura don halartar jana'izar zaman makoki na kwanaki uku

4-An ayyana kwanaki 7 na zaman makoki a ilahirin Najeriya tare da yin ƙasa-ƙasa da tutar kasar

5- Babbar tawaga karkashin jagorancin mataimakin shugaban kasa na can na kammala shirye-shiryen kawo gawar da iyalan mamacin gida

6- Za a yi takaitaccen faretin Sojoji a filin jirgin sama na jahar Katsina don tarbar gawar.

7- Za a yi Sallar Jana'iza da rufe gawar a Daura.

8 An bude shafin karbar ta'aziyya a dukkan ma'aikatun gwamnatin tarayya, da na hukumomi, da ilahirin ofisoshin jakadanci na Najeriya da ke kasashen waje.

9- Ana sa ran isowar gawar Katsina da karfe 12 na rana ranar Talata.

10- Za a yi Jana’iza a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025.

10- Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai karbi gawar tsohon shugaban kasa a Katsina tare da manyan baƙi

~BBC Hausa

A shekarar 2016 ce ya ƙaddamar da shirin N-power, aka ɗauki matasa aiki, inda aka riƙa biyan su alawus na naira 30,000 d...
14/07/2025

A shekarar 2016 ce ya ƙaddamar da shirin N-power, aka ɗauki matasa aiki, inda aka riƙa biyan su alawus na naira 30,000 duk wata.

Shin ka amfana da N-power?

Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma ta amince baki daya ta ayyana ranar Talata 15 ga Yuli, 2025 a matsayin ranar hutu a ...
14/07/2025

Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma ta amince baki daya ta ayyana ranar Talata 15 ga Yuli, 2025 a matsayin ranar hutu a dukkan jihohin Arewa maso Yamma a matsayin abin girmamawa Ga marigayi Tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. Wannan karimcin yana nuna zurfin girmamawar da muke yiwa mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya wajen yiwa Najeriya hidima da bil'adama. Inji su

KBC Hausa

Iyalan Marigayi Muhammadu Buhari Sun Fashe Da Kuka Lokacin Da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shateema Ya Shiga Wajensu ...
14/07/2025

Iyalan Marigayi Muhammadu Buhari Sun Fashe Da Kuka Lokacin Da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shateema Ya Shiga Wajensu A Ƙasar London.

DA ƊUMI-ƊUMI: An ɗaga Jana'izar Marigayi Muhammadu Buhari zuwa gobe Talata, da misalin ƙarfe 2 na rana.~Dikko Radda
14/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: An ɗaga Jana'izar Marigayi Muhammadu Buhari zuwa gobe Talata, da misalin ƙarfe 2 na rana.

~Dikko Radda

DA ƊUMI-ƊUMI : Wani bene mai hawa 4 da ba a ida kammalawa ba, ya faɗo kan mutanen da s**a fakewa ruwan sama a Kano.Lamar...
14/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI : Wani bene mai hawa 4 da ba a ida kammalawa ba, ya faɗo kan mutanen da s**a fakewa ruwan sama a Kano.

Lamarin ya faru a yankin Abedi da ke Sabon Garin Kano, zuwa yanzu an garzaya da wasu Asibiti, don kula da lafiyarsu.

HOTO: Arewa Update

A kakar wasa ta bana Nuno Mendes ya hana duka wadannan manyan 'yan wasa shekar iska a wasannin da s**a gabata.🔒 Salah🔒 S...
14/07/2025

A kakar wasa ta bana Nuno Mendes ya hana duka wadannan manyan 'yan wasa shekar iska a wasannin da s**a gabata.

🔒 Salah
🔒 Saka
🔒 Yamal
🔒 Vini JR
🔒 Olise

…to amma fa jiya Nuno ya kasa tsaida Cole 🥶

JIGA-JIGAN JAM’IYYAR ADC SUN TARU A ABUJA DOMIN SABON TAFIYA A JIHAR BAUCHIA daren jiya Lahadi, birnin tarayya Abuja ya ...
14/07/2025

JIGA-JIGAN JAM’IYYAR ADC SUN TARU A ABUJA DOMIN SABON TAFIYA A JIHAR BAUCHI

A daren jiya Lahadi, birnin tarayya Abuja ya kasance cibiyar tattaunawa da tsari, yayin da jiga-jigan sabuwar tafiya ta jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Bauchi s**a gudanar da muhimmin taro domin tsara gaba da makomar siyasar jihar.

Zaman ya haɗa manyan kusoshin siyasa irin su:

Amb. Sadiq Baba Abubakar CFR (Air Marshal Rtd)

Sanata Halliru Dauda Jika (Dokajin Bauchi)

Sanata Nazir Gamawa

Hon. Salisu Zakari Ningi

Captain Bala Muhammad Jibrin

Hon. Garba Dahiru (Salanken Bauchi)

Alh. Mahmood Kari,
..da sauran fitattun al’umma da s**a sha gwagwarmaya a harkokin mulki da ci gaban jihar Bauchi.

Credit: Haske No Shaking

Takaitaccen tarihin tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari.
14/07/2025

Takaitaccen tarihin tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari.

Gwamnatin Katsina ta sanar da yau litinin 14 ga watan yuli a matsayin ranar hutu, domin girmamawa ga tsohon shugaban kas...
14/07/2025

Gwamnatin Katsina ta sanar da yau litinin 14 ga watan yuli a matsayin ranar hutu, domin girmamawa ga tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Sauka A Landan Don Daukar Gawar Marigayi Shugaba Muhammad Buhari.A safiyar L...
14/07/2025

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Sauka A Landan Don Daukar Gawar Marigayi Shugaba Muhammad Buhari.

A safiyar Litinin, Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, tare da Babban Sakataren Gwamnati, Femi Gbajabiamila, s**a isa birnin Landan bisa umurnin Shugaban Kasa Tinubu domin karɓar gawar Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari. Wannan tafiya na da matukar muhimmanci domin gudanar da aikin da ya shafi karramawa da maido da gawar zuwa Najeriya a cikar girmamawa ta ƙasa.

A lokacin isarsu, an tarbi tawagar a filin sauka da wakilan gwamnati, da s**a haɗa da Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, da Gwamnan Borno, Prof. Babagana Zulum .

Ana sa ran Za a gudanar da jana’izar Yau ranar Litinin a garin Daura mahaifar shugaba Buhari.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KTG News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KTG News Hausa:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share