31/05/2026
Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Katagum, Hon. Auwalu Abdu Gwalebe, ya bayyana cewa komawarsa Majalisar Wakilai zai kara wa mazabar Katagum karfi da damar anfani a zauren Majalisar Tarayya, kasancewar shi ba sabon shiga bane a harkokin majalisa.
Yayin wata hira da KTG News Hausa, Hon. Gwalebe ya ce ya sake tsayawa takarar dan majalisar ne domin ya ci gaba da bibiyar muhimman kudurorin da ya gabatar, musamman kudirin neman kirkirar Jihar Katagum wanda ke cikin shirye-shiryen da ake yi na kara yawan jihohi a Najeriya.
Ya kara da cewa dawowarsa Majalisa zai taimaka wajen ci gaba da wakiltar muradun al'ummar mazabar tare da tabbatar da an cimma manufofin da aka fara aiwatarwa.
Dan Majalisar ya kuma bayyana cewa zai zama koma baya idan aka zabi wanda zai je Majalisar a karon farko, domin a cewarsa irin wadannan sabbin 'yan majalisa kan dauki lokaci kafin su fahimci yadda harkokin majalisa ke gudana, a lokacin da muhimman abubuwa s**a riga s**a yi nisa.
Hon. Gwalebe ya ce wannan ne ya sa ya ga dacewar sake neman amincewar al'ummar Katagum domin ya ci gaba da wakiltarsu da kuma kare muradunsu a Majalisar Tarayya.
KTG News Hausa