BDN Hausa

BDN Hausa Jarida don gaskiya da gaskiya
(4)

13/06/2026

Sabuwar rigimar SALEM GOJE da amaryar sa HAFSAT GOJE da HADIZA GABON, Yana kan jawo cece-kuce a Arewacin Nigeria🤗

Ranar Dimokuraɗiyya: Daliban jami’o’i uku a Kano sun karɓi kyautar motocin bas masu amfani da CNG daga Gwamnatin Tarayya...
12/06/2026

Ranar Dimokuraɗiyya: Daliban jami’o’i uku a Kano sun karɓi kyautar motocin bas masu amfani da CNG daga Gwamnatin Tarayya

Daliban Jami’ar Bayero Kano (BUK), Northwest University Kano da Yusuf Maitama Sule Federal University of Education (YUMSFUE) sun karɓi kyautar sabbin motocin bas masu amfani da iskar CNG daga Gwamnatin Tarayya domin sauƙaƙa musu zirga-zirga da rage musu wahalhalun sufuri.

A wani taro da aka gudanar a harabar Jami’ar Bayero Kano a yayin bukukuwan Ranar Dimokuraɗiyya, Ofishin Kula da Ayyukan Gwamnatin Tarayya a Arewacin Najeriya (Northern Project Coordination Office), tare da Hukumar Bayar da Lamunin Karatu ta NELFUND da shirin shugaban ƙasa na PI-CNG, ne s**a jagoranci rabon motocin ga ƙungiyoyin ɗaliban jami’o’in uku.

An bayyana cewa shirin na daga cikin matakan da Gwamnatin Tarayya ke ɗauka na tallafa wa ɗalibai, rage musu nauyin kuɗaɗen sufuri da kuma ƙarfafa amfani da makamashi mai tsafta a fannin zirga-zirga.

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Malam Abdulaziz Abdulaziz, wanda ke cikin tawagar da shugaban ƙasa ya aike domin gudanar da bikin, ya yaba da shirin, yana mai cewa hakan wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnati na tallafa wa ilimi da inganta rayuwar ɗalibai. Ya kuma buƙaci waɗanda s**a amfana da motocin da su yi amfani da su yadda ya kamata domin cimma manufar da aka samar da su.

Cikar Dimokuraɗiyya Shekaru 27: Tinubu Ya Yabawa Jaruman 12 gaYuni, Ya Kira 'Yan Najeriya Su Kare DimokuraɗiyyaShugaban ...
12/06/2026

Cikar Dimokuraɗiyya Shekaru 27: Tinubu Ya Yabawa Jaruman 12 gaYuni, Ya Kira 'Yan Najeriya Su Kare Dimokuraɗiyya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga 'yan Najeriya da su ci gaba da kare dimokuraɗiyya tare da ƙarfafa cibiyoyin gwamnati, yana mai cewa ƙasar ta samu mafi tsawon lokacin mulkin farar hula a tarihinta.

A jawabin da ya gabatar domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, Shugaba Tinubu ya ce shekaru 27 da s**a gabata sun nuna cewa Najeriya na iya gudanar da sauye-sauyen mulki cikin lumana ta hanyar zaɓe da bin doka.

Ya kuma yi kira ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), jami'an tsaro da jam'iyyun siyasa da su tabbatar da cewa zaɓukan da za a gudanar a jihohin Ekiti da Osun sun kasance cikin gaskiya da adalci.

Shugaban ya yabawa Majalisar Tarayya, bangaren shari'a, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula bisa rawar da suke takawa wajen kare dimokuraɗiyyar ƙasar.

Tinubu ya kuma yi amfani da damar wajen tunawa da marigayi MKO Abiola, Kudirat Abiola, Shehu Musa Yar'Adua, Gani Fawehinmi da sauran fitattun mutane da s**a taka rawa a gwagwarmayar dawo da mulkin dimokuraɗiyya.

Haka kuma ya sanar da cewa gwamnatin tarayya za ta sauya sunan Cibiyar Nazarin Man Fetur da ke Kaduna zuwa Jami'ar Kimiyyar Kasa da Fasahar Injiniya ta Janar Shehu Musa Yar'Adua domin girmama gudummawar marigayin.

Shugaban ya kuma bayyana sunayen wasu fitattun 'yan gwagwarmayar dimokuraɗiyya da sojojin da s**a mara wa gwagwarmayar baya waɗanda za a karrama da lambobin yabo na ƙasa.

Gwamnatin Tarayya Ta Ba Da Hutu Ranar Juma’a Domin Bikin Shekaru 27 Na Cigaban Dimokiraɗiyya Ba Tare Da Katsewa BaGwamna...
12/06/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Ba Da Hutu Ranar Juma’a Domin Bikin Shekaru 27 Na Cigaban Dimokiraɗiyya Ba Tare Da Katsewa Ba

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata domin bikin cika shekaru 27 da Nijeriya take gudanar da mulkin dimokiraɗiyya ba tare da katsewa ba.

Babbar Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, ita ta bayyana haka cikin takardar manema labarai da ta rattaba wa hannu a ranar Alhamis a Abuja.

Ajani ta ce Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya ba da sanarwar hutun a madadin Gwamnatin Tarayya.

Tunji-Ojo ya sake jaddada aniyar gwamnati na kare da kuma bunƙasa ƙa’idojin dimokiraɗiyya, ciki har da bin doka da oda, gaskiya da riƙon amana, ɗaukar nauyi, da kuma shugabanci mai haɗa kowa da kowa.

Ya tabbatar da cewa Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro da abin ya shafa, za su ci gaba da ɗaukar matakan da s**a dace domin tabbatar da tsaro da kuma ƙarfafa zaman lafiyar cikin gida a Nijeriya.

Ministan ya bayyana cewa samun yanayi mai cike da tsaro da kwanciyar hankali yana da matuƙar muhimmanci domin dimokiraɗiyya ta bunƙasa tare da tabbatar da cigaban ƙasa mai ɗorewa.

Ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan ranar hutun wajen yin nazari kan matsayin su na ‘yan ƙasa tare da sabunta jajircewar su wajen kare kyawawan ɗabi’u da ƙimomin ƙasa.

Ya ce, “Yayin da muke bikin wannan rana mai tarihi, muna kira ga kowane ɗan Nijeriya da ya kasance mai bin doka, ya mutunta cibiyoyin da ke ɗorewar dimokiraɗiyyar mu, tare da tuna cewa ƙarfin kowace dimokiraɗiyya yana ta’allaƙa ne ga halaye da ɗabi’un ‘yan ƙasar ta.”

Tunji-Ojo ya ƙara da cewa ranar 12 ga Yuni tana da muhimmin matsayi a tarihin Nijeriya, domin tana girmama jarumtaka, juriya da sadaukarwar waɗanda s**a bayar da gudunmawa wajen kafa mulkin dimokiraɗiyya a ƙasar nan.

“Har yanzu abin da muka gada daga gare su yana ci gaba da zama abin koyi wajen tsara ƙimomi da nauyin da ya rataya a wuyan ƙasar Nijeriya,” inji shi.

Manufofin Gwamnatin Tinubu na Tare da Matasan Najeriya - Kashim Shettima Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettim...
11/06/2026

Manufofin Gwamnatin Tinubu na Tare da Matasan Najeriya - Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa shirye-shirye da manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu an shirya suna ta yadda za su mori matasan Najeriya, saboda gwwmnati na amfani da sabbin dabaru wajen magance matsalolin zamani na wannan karni na 21.

Ya yi wannan bayani ne yayin ganawa da shugabannin kungiyar City Boy Movement a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, inda ya jaddada cewa gwamnati na daukar matasa a matsayin ginshikin ci gaban kasa da kuma makomar dimokuradiyya.

Shettima ya ce gwamnatin Tinubu na daukar matakai masu wahala amma masu muhimmanci don farfado da tattalin arziki da kuma tabbatar da ci gaba mai dorewa, yana mai cewa nasarar gyare-gyare na bukatar hakuri, jajircewa da goyon bayan ‘yan kasa.

Ya kuma bayyana cewa dimokuradiyya ba ta tsaya kan zabe kadai ba, tana bukatar shigar jama’a da kuma hadin kai wajen kare manufofin da ke kawo ci gaba ga kasa.

Mataimakin Shugaban Kasa ya yabawa kungiyar City Boy Movement bisa kokarinta na wayar da kan jama’a da kuma karfafa goyon bayan gwamnati, yana mai jaddada muhimmancin ladabi, amana da hadin kai a siyasa da shugabanci.

Kungiyar wadda Hon. Francis Oluwatosin Shoga, ke jagaranta ta yi alkawarin ci gaba da zagayawa fadin Najeriya domin tattara goyon baya ga sake zaben Shugaba Tinubu a shekarar 2027.

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci k...
10/06/2026

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci kusan dazukan anan da dama wuraren kiyon dabbobi ne. To, bayan da aka kirkiri Abuja, an tanadi wurare da aka tsara jama'a za su zauna, tare da wuraren ofisoshi da wuraren gina kasuwanni da sauran wuraren more rayuwa, amma aka manta a keɓe tare da inganta inda dabbobi za su yi kiwo.

Akwai gandun daji guda huɗu da faɗin su ya kai hekta 33 a Abuja da aka ware tun da, sannan tun da aka ware waɗannan gandun dajin a wancan lokacin da aka kirkiri Abuja, ba a taɓa yin wani abu na inganta wurin ta yadda za a maida makiyaya wurin ba.

Tun bayan kafa ma’aikatar kula da bunƙasa kiyon dabbobi kusan shekara biyu da s**a wuce, ma’aikatar ta kulla alaƙa tare da Hukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya ta yadda za a inganta waɗannan wurare da ke yankunan ƙauyen Kau, Karshi da sauran wurare da ke Abuja.

Muna aiki tare da masu ruwa da tsaki wajen inganta waɗannan gandun dajin, sannan a duba yiwuwar maida makiyaya wurin sannu a hankali."

— Idi Muktar Maiha, Ministan Bunƙasa Kiyon Dabbobi, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai na Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026 da aka gudanar a ranar Talata, 9 ga Yuni, 2026.

10/06/2026

In security in Nigeria 🗣️

10/06/2026

Tawagar Yan kwallon Kasar Iran sun Isa kasar Mexico domin Buga wa Kasar su Wasa, a gasar cin Kofin Duniya da ake daf da farawa, Ya kuke ganin Idan wasa ta kai su cikin Amurka???

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Kan Ebola, Ya Amince da Naira Biliyan 10 Don Shirin Bada KariyaShugaban Bola Ahm...
09/06/2026

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Kan Ebola, Ya Amince da Naira Biliyan 10 Don Shirin Bada Kariya

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa Kwamitin Musamman na Fadar Shugaban Ƙasa kan Shirin Kariya daga Cutar Ebola da Sauran Barazanar Lafiyar Jama’a, tare da bayar da umarnin sakin naira biliyan 10 domin shirye-shiryen gaggawa.

A cewar sanarwar da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, kuɗaɗen za su taimaka wajen ƙarfafa shirye-shiryen Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa ta Ƙasa (NCDC) da kuma ayyukan da s**a shafi tunkarar duk wata barazanar gaggawa ga lafiyar al’umma.

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne zai jagoranci sabon kwamitin, wanda zai haɗa da wakilai daga ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati daban-daban, da kuma wakilan jihohi.

Matakin ya biyo bayan sake bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da kuma Uganda.

Shugaba Tinubu ya amince da kafa kwamitin ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa ya jagoranta domin nazarin irin shirin da Najeriya ta yi da kuma dabarun da za su hana cutar shiga ƙasar.

Daga cikin mahalarta taron akwai wakilai daga Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN), Hukumar Shige da Fice (NIS), Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (NCAA), da gwamnatin jihar Legas.

Shugaban ƙasar ya kuma umarci dukkan jihohin da ke da filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa da kuma manyan hanyoyin shiga ƙasar daga ƙasashen waje da su gabatar da tsare-tsarensu, buƙatun kuɗi da irin tallafin da suke buƙata domin aiwatar da matakan kariya cikin haɗin gwiwa.

A cikin matakan da aka sanar za a ɗauka akwai ƙara tsaurara binciken fasinjoji a dukkan filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa, ciki har da duba zafin jiki da tsara yadda jama’a ke shiga da fita.

Haka kuma za a ƙarfafa sa ido kan fasinjojin da ke shigowa ta wasu hanyoyin jiragen sama da gwamnati ta ayyana a matsayin masu haɗari, ciki har da Air Uganda, RwandAir, Air Tanzania, Air Angola, Kenya Airways da Ethiopian Airlines.

Gwamnatin ta ce za a gaggauta bude cibiyoyin killace marasa lafiya da wuraren tura waɗanda ake zargin sun kamu da cutar a filayen jiragen saman Legas da Abuja, kafin daga baya a faɗaɗa tsarin zuwa sauran filayen jiragen saman ƙasar.

Sauran matakan sun haɗa da wajabta cike bayanan lafiyar matafiya ta hanyar tsarin QR Code kafin su iso ƙasar idan sun fito ko s**a bi ta ƙasashen da aka ayyana masu haɗari, da kuma tsaftace dakunan tashi da saukar jirage, wuraren kaya da sauran sassan filayen jiragen sama.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci kwamitin da ya tattauna da hukumomin tsaro, diflomasiyya da sufurin jiragen sama kan yiwuwar ɗaukar ƙarin matakan da s**a shafi zirga-zirgar jirage daga ƙasashen da cutar ta bulla ko waɗanda aka sanya cikin jerin masu haɗari.

Bugu da ƙari, kwamitin zai duba yiwuwar ware wasu filayen jiragen sama ko tashoshi na musamman domin karɓar jiragen da ake ganin suna da haɗari, tare da nazarin sauya lokutan saukar wasu jirage domin rage haɗuwar fasinjojin da ake sa ran za su buƙaci ƙarin bincike da sauran matafiya.

08/06/2026

Shugabanin Mata na Jam'iyyar APC sun Karyata rade-radin da ake fada na cewa sun koma Jam'iyar PRP, sunce babu Yanda zasu je sunan daram a APC, Kuma zasu yi MA ba Fashi.🗣️

Address

Abuja
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BDN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share