BDN Hausa

BDN Hausa Jarida don gaskiya da gaskiya
(5)

14/08/2026

Saurara Kuji 🗣️

Shugaba Tinubu Ya Ƙudiri Niyyar Farfaɗo da Matatun Man Fetur Na Najeriya Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce Gwamnatin...
14/08/2026

Shugaba Tinubu Ya Ƙudiri Niyyar Farfaɗo da Matatun Man Fetur Na Najeriya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce Gwamnatin Tarayya ba za ta bari matatun man fetur na Najeriya su lalace ba, yana mai cewa za a sake fasalin yadda ake tafiyar da su ta hanyar bincike mai zurfi, sake fasalin tsarin gudanarwa da samar da ingantaccen shugabanci domin su koma aiki tare da samar da riba.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne ranar Alhamis a Abuja, lokacin da ya karɓi shugabannin Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (NUPENG), ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Salimon Akanni Oladiti.

Shugaban Ƙasar ya ce matsalolin da ke addabar matatun za a magance su ne ta hanyar tsari mai inganci da ya dogara da hujjoji, maimakon ɗaukar matakan wucin gadi. Ya ce za a gudanar da cikakken bincike da tantancewar ƙwararru domin gano matsalolin tsarin gine-gine, aiki, kuɗi da gudanarwa da ke hana matatun samar da abin da aka gina su domin yi. Ya jaddada cewa ganin wuta da hayaƙi daga matatar mai ba shi ne ma’aunin nasara ba, sai matatar ta samar da ƙima tare da riba.

Tinubu ya kuma ce Gwamnatin Tarayya na duba batutuwan da s**a shafi aiwatar da ‘yancin cin gashin kan ƙananan hukumomi, musamman batutuwan kundin tsarin mulki da ke da alaƙa da lamarin. Ya yi kira ga masu ruwa da tsaki su fahimci matakan da ake ɗauka. Haka kuma, ya tuna da tsohon shugaban NUPENG, marigayi Frank Kokori, yana mai cewa sun yi gwagwarmayar kafa tsarin dimokuraɗiyya tare.

Shugaban Ƙasar ya kuma yi alkawarin ƙara bai wa NUPENG damar shiga cikin aiwatar da shirin Shugaban Ƙasa na amfani da CNG, tare da ƙalubalantar ƙungiyar da ta tabbatar da cewa amfanin shirin ya isa ga masu sufuri.

A nasa jawabin, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya yaba wa NUPENG bisa amincewa da sakamakon wasu daga cikin sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa. Ya ce irin wannan fahimta ta taimaka wajen rage saɓani tsakanin ƙungiyoyin ƙwadago da gwamnati. Idris ya ambaci cire tallafin man fetur da kuma ayyukan gina ababen more rayuwa a faɗin ƙasar a matsayin manyan sauye-sauyen da ƙungiyar ta yaba da su.

Shugaban NUPENG, Salimon Oladiti, ya yaba wa Tinubu kan cire tallafin man fetur, yana mai cewa matakin ya taimaka wajen dakile asarar dimbin kuɗaɗen gwamnati da kuma buɗe damar zuba jari a ababen more rayuwa. Ya kuma yaba da ayyukan manyan tituna, musamman hanyar Lagos–Calabar mai tsawon kilomita 750 da kuma babbar hanyar Sokoto–Badagry mai tsawon kilomita 1,068. Daga bisani, shugabannin NUPENG s**a naɗa Tinubu a matsayin Babban Uban ƙungiyar.

13/08/2026

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, a yayinda yake bayyana muhimman abubuwan da aka tattauna a wajen taron Ƙungiyar Kasashen Musulmi ta Duniya (World Muslim League), a zauren taro na Bola Ahmed Tinubu, a Abuja.

13/08/2026

Maganganun Shekh Sani Yahaya Jingir suna kan cigaba da Jawo cece-kuce 🗣️

13/08/2026

Komai da ilimin sa, ku Kalli Yanda ake koyar da masu kai abinci wa Customers 🤗

Mawaƙin Dauda Kahutu Rarara yace shima a shirye take domin rubutawa jagoran addinin Iran Mujtaba Khamene'i wasiƙa kamar ...
13/08/2026

Mawaƙin Dauda Kahutu Rarara yace shima a shirye take domin rubutawa jagoran addinin Iran Mujtaba Khamene'i wasiƙa kamar yadda Davido ya rubutawa Trump.

Nijeriya na buƙatar haɗin kai yanzu fiye da kowane lokaci – Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ...
12/08/2026

Nijeriya na buƙatar haɗin kai yanzu fiye da kowane lokaci – Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga 'yan Nijeriya da su ɗaukaka tunanin su sama da bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa, su haɗa kai wajen yaƙi da rashin tsaro da sauran ƙalubalen da ke fuskantar ƙasar.

Idris ya yi wannan kiran ne a ranar Talata, a wajen taron ƙasa da ƙasa mai taken “Bambance-bambance da Zaman Lafiyar Al'umma: Haɗin Gwiwa don Kyakkyawar Makoma,” wanda ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta shirya tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League) a Abuja.

Ministan ya ce bambance-bambancen mutanen da s**a halarci taron ya nuna cewa akwai fahimtar juna cewa tsaro, zaman lafiya da wadata a Nijeriya sun dogara ne da yadda 'yan ƙasa za su yi aiki tare ba tare da la'akari da bambance-bambancen addini, ƙabila da siyasa ba.

Idris ya ce: “Dukkan mu muna buƙatar mu haɗa kai, mu yi tunani a matsayin 'yan Nijeriya, mu yi tunani a matsayin 'yan'adam, kuma mu yi aiki tare ba tare da la'akari da bambance-bambancen mu ba, domin mu kasance tsintsiya maɗaurin ki ɗaya.”

Ya jaddada cewa rarrabuwar kawuna bisa addini da ƙabila za ta ƙara dagula yaƙi da rashin tsaro, yana mai kira ga 'yan Nijeriya da su yi watsi da tashin hankali, rashin haƙuri da ƙoƙarin amfani da bambance-bambancen ƙasar nan wajen raba kan al'umma.

“Babu lokacin bambance-bambance. Idan a yayin yaƙin da muke yi da rashin tsaro muka bari bambance-bambancen addini s**a shiga, hakan zai ƙara dagula matsalar. Buƙatar da muke da ita ta haɗa kan mu a matsayin al'umma ɗaya na da matuƙar muhimmanci,” inji shi.

Idris ya fayyace cewa ba Gwamnatin Tarayya ce ta shirya taron ba, sai dai ya ce gwamnati tana maraba da shirye-shiryen da ke inganta tattaunawa tsakanin mabiya addinai, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

“Idan muna son ci gaba da tafiya zuwa ga wadata, dole ne dukkan mu mu yi tunani da aiki tare, mu kuma haɗa kai a matsayin al'umma ɗaya,” inji ministan.

Ya ce yawan al'ummar Nijeriya, muhimmancin ta da kuma tasirin ta na nufin zaman lafiya da kwanciyar hankalin ƙasar na da matuƙar tasiri ga Afirka da ma sauran sassan duniya.

“Nijeriya ƙasa ce mai matuƙar muhimmanci. Ƙasa ce mai mutane sama da miliyan 230. Zaman lafiya da kwanciyar hankali a nan na nufin zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk faɗin Afirka, har ma da duniya baki ɗaya,” inji shi.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a taron, ya isar da saƙon aniyar Shugaban Ƙasa ta tabbatar da ingantaccen tsaro mai ɗorewa, haɗin kan ƙasa da haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa, yana mai cewa Nijeriya za ta ci gaba da aiki tare da abokan hulɗar ta na ƙasa da ƙasa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya kuma Shugaban Ƙungiyar Malaman Musulunci ta Duniya, Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su kare haƙƙin ɗan'adam da s**a yi tarayya a cikin ta, tare da yin watsi da ƙoƙarin amfani da addini, ƙabila ko talauci wajen raba kan ƙasa.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III, ya yi kira da a ci gaba da tattaunawa, tsare gaskiya da ƙara ƙaimi wajen aiwatar da hanyoyin magance ƙalubalen Nijeriya, tare da kira ga 'yan Nijeriya da su sake gina amana da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin mabiya addinai.

A nasa jawabin, Shugaban jam'iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya buƙaci 'yan Nijeriya da su ɗauki bambance-bambancen ƙasar a matsayin tushen ƙarfi maimakon rarrabuwar kai, yana mai cewa duk da cewa 'yan Nijeriya suna gudanar da ibada ta hanyoyi daban-daban, suna da buri da ƙalubale iri ɗaya.

Shugaban JIBWIS na Ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau, ya yi kira da a ƙara haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, ƙungiyoyin addini da al'ummomi wajen yaƙi da rashin tsaro, tare da ƙara zuba jari a fannin ilimi da bunƙasa ƙwarewa domin rage yiwuwar matasa su rungumi tsattsauran ra'ayi ko kuma a ɗauke su aikin laifi.

Daga cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu; Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi; Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum; Ministan Bunƙasa Kiwo, Idi Mukhtar Maiha; Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa'ad Abubakar III; Shugaban APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda; Sheikh Mohammed bin Abdulkarim Al-Issa; Shugaban JIBWIS na Ƙasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau; Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Nijeriya (NSCIA), da sauran manyan jami'an gwamnati, shugabannin addinai da na gargajiya, jami'an diflomasiyya, wakilan ƙungiyoyin fararen hula da sauran manyan baƙi.

12/08/2026

“Wasu mutane suna amfani da addini cikin mugunta domin su lalata harkokin siyasa da kuma tsaron ƙasar nan,” in ji Sheikh Nuru.

11/08/2026

Shin Kun Taba Ganin yanda Giwa Ke Shan Ruwa???

11/08/2026

Kwankwaso Na Magana 🗣️

Address

Abuja
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BDN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share