BDN Hausa

BDN Hausa Jarida don gaskiya da gaskiya
(4)

Fira Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ba da haƙuri ga hukumomin Qatar dangane da harin da ƙasarsa ta kai a kwanak...
30/09/2025

Fira Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ba da haƙuri ga hukumomin Qatar dangane da harin da ƙasarsa ta kai a kwanakin baya a birnin Doha wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wasu jagororin ƙungiyar Hamas da wani jami'in Qatar.

30/09/2025

Jami’an ICE sun bi wani mutum a tsakiyar birnin Chicago bayan ya yi wasu maganganu, amma da ya ga sun taso Sai Ya tsere Da gudu.

Ana ci gaba da aikin haƙo rijiyoyin mai guda uku a yankin Kolmani na jihohin Bauchi da Gombe. Gwamnatin Tarayya ta  mai ...
30/09/2025

Ana ci gaba da aikin haƙo rijiyoyin mai guda uku a yankin Kolmani na jihohin Bauchi da Gombe. Gwamnatin Tarayya ta mai da hankali sosai kan wannan aiki - Inji Ministan yaɗa Labarai da Wayar da Kai Mohammed Idris

Aikin Shimfiɗa Bututun Iskar Gas Na Ajaokuta Da Kaduna Har Zuwa Jihar Kano (AKK Gas Pipeline) Ya Yi NisaGwamnatin tarayy...
30/09/2025

Aikin Shimfiɗa Bututun Iskar Gas Na Ajaokuta Da Kaduna Har Zuwa Jihar Kano (AKK Gas Pipeline) Ya Yi Nisa

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa aikin shimfiɗa bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK Gas Pipeline) yayi nisa sosai. Wannan aiki na daga cikin manyan ayyukan raya tattalin arziƙin ƙasa da nufin kawo sauyi a fannin samar da makamashi da kuma bunkasa masana’antu da farfaɗo da kamfanoni da s**a daɗe da durƙushewa a Arewa.

Ministan yaɗa Labarai da Wayar da Kai Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a wajen taron manema labarai na murnar Najeriya cika shekaru 65 da samun incin kai, wanda aka gudanar a yau Litinin, a cibiyar 'yan jarida ta ƙasa dake Abuja

Gwamnan Jihar Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed ya gina Cibiyar Taron Ƙasa da Ƙasa, wacce aka gina daga farko har ...
30/09/2025

Gwamnan Jihar Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed ya gina Cibiyar Taron Ƙasa da Ƙasa, wacce aka gina daga farko har ƙarshe a ƙarƙashin jagoranci sa

Akwai mutane da yawa da suke da ra'ayi akan haka kamar yadda Abdulaziz T. Bako, ya faɗi nasa guda uku akan cewa1. Ɗaure ...
29/09/2025

Akwai mutane da yawa da suke da ra'ayi akan haka kamar yadda Abdulaziz T. Bako, ya faɗi nasa guda uku akan cewa

1. Ɗaure Lawan Triumph = consistency.
2. Sakinsu da shi da Abduljabbar = gyara kuskuren da aka yi a baya.
3. Rabuwa da Triumph da ci gaba da ɗaure Abduljabbar = favoritism (nuna son kai)

Meye ra'ayin ku akan abinda ya faɗa?

ZA A DAUKE RUWA NA TSAWON MAKONNI BIYAR A WASU SASSAN BIRNIN BAUCHI. Hukumar samar da da Ruwan Sha ta Jihar Bauchi ta sa...
29/09/2025

ZA A DAUKE RUWA NA TSAWON MAKONNI BIYAR A WASU SASSAN BIRNIN BAUCHI.

Hukumar samar da da Ruwan Sha ta Jihar Bauchi ta sanar da cewa za ta rufe tsarin tace ruwa lita miliyan 2.5 na wucin gadi daga yau Litinin, 29 ga watan Satumba, na shekarar 2025, domin gyare gyare da tsarin kulawa na lokaci lokaci.

Rufewar za ta ɗauki makonni biyar, inda ake sa ran gyaran zai kara inganci da yawan ruwan sha ga al’ummar Bauchi.

Wuraren da za su fi fuskantar matsalar ruwa sun haɗa da:

1. Gida Dubu Housing Estate
2. Rukunin gidajen Ma’aikatan ATBU (Kari Estate)
3. Rafin Makaranta
4. Sassan Magaji Quarters
5. Sassan School of Armour

Hukumar ta bayyana cewa za a tura tankokin ruwa domin rage wa jama’a raɗaɗin rashin ruwa a wannan lokaci.

Hukumar ta roƙi jama’a da su nuna haƙuri da fahimta, domin aikin na cikin shirin gwamnatin jihar Bauchi na ƙarfafa samar da ruwan sha mai dorewa.

Gwamnan Jihar Bauchi Ya sauke Hajiya Zainab Baban Takko daga mukaminta na Kwamishinan Harkokin Mata & Ci gaban Yara ba t...
29/09/2025

Gwamnan Jihar Bauchi Ya sauke Hajiya Zainab Baban Takko daga mukaminta na Kwamishinan Harkokin Mata & Ci gaban Yara ba tare da bata lokaci ba.

Gwamnan ya gode wa Kwamishinar bisa hidimarta ga cigaban Jihar , kuma yana mata fatan nasara a ayyukanta na gaba.

Bada Jimawa ba Itama Tshohuwar Kwamishinan ya Muto Da sako kamar haka

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah Wadai Tare Da Ƙaryata Zargin Kisan Ƙare Dangi Da Ake Yada Cewa Wai Yan Bindiga Na Ma Kiris...
28/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah Wadai Tare Da Ƙaryata Zargin Kisan Ƙare Dangi Da Ake Yada Cewa Wai Yan Bindiga Na Ma Kiristocin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi Allah-wadai tare da ƙaryata zarge-zargen da wasu kafafen watsa labarai na ƙasashen waje da masu tasiri a kafafen sada zumunta suke yi na cewa wai ‘yan ta’adda a Nijeriya suna yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi. Gwamnatin ta ce irin wannan iƙirarin “ƙarya ne, marasa tushe, abin ƙyama, kuma na raba kawuna.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce: “Bayyana matsalolin tsaro a Nijeriya a matsayin wani yaƙi da aka kitsa musamman kan wasu mabiya addini guda ɗaya ba daidai ba ne, kuma rashin adalci ne.”

Ya ƙara da cewa: “Ko da yake Nijeriya, kamar dai wasu ƙasashen, tana fuskantar matsalolin tsaro, ciki har da ta’addanci da ‘yan ta’adda suke aikatawa, fassara wannan a matsayin wani hari na musamman kan Kiristoci ba gaskiya ba ne, illa ma cutarwa ne.

“Hakan na wofintar da matsala mai matuƙar rikitarwa, kuma yana taimaka wa ‘yan ta’adda da sauran masu aikata laifi wajen raba kan ‘yan Nijeriya bisa addini ko ƙabila.”

Idris ya ce: “Ayyukan ta’addanci ba su taƙaita ga wata al’umma ta addini ko ƙabila ɗaya ba. Waɗannan miyagun suna kai hari ga duk wanda ya ƙi bin aƙidar su ta kisa, ko Musulmi, ko Kirista, har ma wanda ba ya bin wani addini. Duk suna shan wahala a hannun su.”

Ya nuna cewa Gwamnatin Tarayya tana da cikakken ƙudirin murƙushe ƙungiyoyin ta’addanci da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, kuma wannan tuni aka riga aka fara ganin sakamakon sa.

Ya ce: “Tsakanin watan Mayu na 2023 da Fabrairun 2025 kaɗai, an hallaka ‘yan ta’adda da masu laifi sama da 13,543 tare da kuɓutar da kusan mutum 10,000 daga hannun su a faɗin ƙasar nan. A watan da ya gabata ma, an cafke manyan shugabannin ƙungiyar ANSARU, ƙungiyar da ke da alaƙa da Al-Ƙa'ida, a wani babban samamen yaƙi da ta’addanci. Sun haɗa da Mahmud Muhammad Usman (wanda aka fi sani da Abu Bara’a/Abbas/Mukhtar), wanda ke kira kan sa Sarkin ANSARU, da kuma Mahmud al-Nijeri (wanda aka fi sani da Malam Mamuda), wanda ya kasance mataimakin sa.”

Ministan ya ce waɗannan nasarorin wata hujja ce ta jajircewar jami’an tsaro da kuma rashin ingancin zargin cewa Nijeriya tana lamunta da ta’addancin da ya ta’allaƙa da addini.

Ya ƙara da cewa: “Gwamnatin Tarayya ba ta yi ƙasa a gwiwa ba a aikin ta na kare kowane ɗan Nijeriya, ba tare da la’akari da addini ko ƙabilar sa ba. Rundunar Sojojin Nijeriya da ta ‘Yan Sandan Nijeriya kuma suna gudanar da kotunan soja da shari’o’i don hukunta jami’an da s**a karya doka. Wannan na nuni da muhimmancin ladabi da bin doka a hukumomin tsaro.”

Ya jaddada cewa Nijeriya ƙasa ce mai addinai da dama, wadda ke ɗauke da manyan al’ummomin Musulmi da Kiristoci a duniya. “Kiristanci ba ya cikin haɗari ko kuma ana nuna masa wariya a Nijeriya,” in ji shi.

Ya kuma yi nuni da cewa: “Shin waɗannan masu saka baki daga ƙasashen waje sun san cewa manyan hafsoshin Rundunar Sojojin Nijeriya da ‘Yan Sandan Nijeriya a yanzu dukkansu Kiristoci ne? Wannan kansa na nuna yadda jagorancinmu ya kasance na haɗin kai.”

Game da yaƙi da ta’addanci, Ministan ya bayyana cewa an yi nasarar gurfanar da wasu ‘yan Boko Haram a gaban kuliya: “Zuwa yanzu, an yi nasarar gurfanar da rukuni bakwai na waɗanda ake zargi, inda aka samu hukunci sama da 700. A yanzu muna shiga zagayen takwas na shari'ar, don nuna tsananin ƙudurinmu wajen yaƙar ta’addanci da masu ɗaukar nauyinsa.”

A cewarsa, ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙari don tabbatar da adalci da ƙara tsaro.

“Labarin Nijeriya ba na kisan ƙare dangi na addini ba ne. Labarin ƙasa ce mai juriya, bambance-bambance, da ƙuduri na haɗin kai wanda duniya ta shaida.”

Ya tuna cewa a watan Maris na bana, lambar yabo ta farko ta Commonwealth Peace Prize an bai wa shugabannin addinai biyu na Nijeriya — Fasto James Movel Wuye da Liman Muhammad Nurayn Ashafa — saboda aikinsu na gina amana da haɗin kai tsakanin Musulmi da Kiristoci.

Ya ce: “Wannan na nufin cewa Nijeriya ba wai kawai tana fitar da al’adu da kiɗa zuwa duniya ba ne, har ma tana fitar da tabbataccen tsari na musamman na zaman lafiya tsakanin addinai.”

A ƙarshe ya yi kira ga kafafen watsa labarai na duniya da masu sharhi su guji rashin sani da yin tashe-tashen hankula ta hanyar kalaman rarraba kawuna. “Maimakon haka, ya kamata a tallafa wa ƙoƙarin Nijeriya na ci gaba da yaƙar ta’addanci da duk wani irin laifuka,” inji shi.

Daga Kasar Indiya: Mutane 29 sun mutu, daruruwa sun jikkata saboda cunkoso a taron gangamin siyasa na jarumi Vijay, wand...
28/09/2025

Daga Kasar Indiya: Mutane 29 sun mutu, daruruwa sun jikkata saboda cunkoso a taron gangamin siyasa na jarumi Vijay, wanda ya gudana a yankin Tamil Nadu na kasar India.

Wani matashin Ɗan siyasa a Jihar Kano, ya fadi ra'ayin sa akan Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da cewa “Wannan mutumin ba ɗan ...
28/09/2025

Wani matashin Ɗan siyasa a Jihar Kano, ya fadi ra'ayin sa akan Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da cewa “Wannan mutumin ba ɗan siyasa mai son kai ba ne, mutum ne mai wayo, hikima da kwarin gwiwa. Saboda haka muna binsa bashi da wasu shekaru 4. Ni kaina ba magoyin bayan APC ba ne, amma saboda wannan mutumin, na ayyana shi a matsayin wanda zai lashe zaben shugaban ƙasa na 2027 da ikon Allah. A wannan lokaci ba ma buƙatar sauyi, abin da muke nema shi ne ƙarin kuzari wajen tura Najeriya gaba"

Meye ra'ayin ku akan abinda Ya fada?

28/09/2025

Malamin Sunnah Sheikh Lawan Abubakar Shu'aib Triumph wani fata kuke masa?

Address

Abuja
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BDN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share