16/08/2025
YANZU-YANZU: Muna kira ga Hukumar zaɓe INEC ta soke zaɓen cike gurbi saboda tashin hankali domin muna so Ayi mana Adalci -Jam'iyyar APC
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta bukaci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da ta soke zaɓen cike gurbi na mazabar Shanono/Bagwai da kuma sak**akon zaɓen na mazabar Ghari a Jihar Kano, saboda tashin hankali da s**a barke a wuraren zaɓe. APC ta bayyana cewa an k**a fiye da 'yan fashin Zaɓe sama da 200 a wasu wurare yayin gudanar da zaɓen .
A cikin wata sanarwa da Felix Morka, Sakataren yada labarai na ƙasa na jam’iyyar APC ya sanya wa hannu, APC ta ce rahotanni da s**a zo da tabbas daga yankunan Shanono, Bagwai da Ghari sun nuna cewa tsarin zaɓen ya lalace saboda ‘yan fashi sun tursasa masu jefa ƙuri’a su gudu daga wuraren zaɓe, kuma jami’an tsaro sun gagara tsayawa da zaɓen .
Jam’iyyar ta ƙara da cewa “ci gaba da gudanar da zaɓen a cikin rukuni-rukuni na tashin hankali da tsangwamar masu kada ƙuri’a zai sabawa ka’idojin zaɓe na gaskiya, adalci da zaman lafiya, kuma zai kafa mummunar alama ga makomar dimokuradiyya a ƙasar mu” .
Shugaban Jam'iyyar APC na jihar Kano dai Abdullahi Abbas Yayi kalamai kausasa kafin ranar zaɓen lamarin da ya jawo cece kuce tsakanin al'ummar ƙasa