KIMA TV

KIMA TV Ku ci gaba da bibiyar Kima Tv (Hasken Al'umma)

Domin tallata hajarku, siyasa ko al'amuran jama'a, ku tuntube mu domin samun ingantaccen isar da saƙo.

Don Tallace-tallace,
📲 WhatsApp: 08072725161
📞 Ko kira: 09153710101

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya isa Ibadan domin halartar bikin nadin sabon Olubadan, Rashidi Ladoja a jihar Oyo
26/09/2025

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya isa Ibadan domin halartar bikin nadin sabon Olubadan, Rashidi Ladoja a jihar Oyo

Gwamnatin Jihar Kano ta umarci Majalisar Shura da ta duba tare da bayar da shawarwari kan korafe-korafen da ake yi wa Sh...
26/09/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta umarci Majalisar Shura da ta duba tare da bayar da shawarwari kan korafe-korafen da ake yi wa Sheikh Lawan Triumph, wanda ake zargin ya yi kalaman batanci ga Manzon Allah (SAW).

Kungiyoyin kamar haka ne s**a gabatar da koken.

1. Safiyatul Islam Nigeria
2. Dandalin Fadakarwa Matasan Tijjaniya
3. Jam'iyyun Masoyan Addinai Don Zaman Lafiya Da Ci Gaba
4. Sairul Qalbi Foundation
5. Habbullah Mateen Foundation
6. Limaman Masallatan Juma'a karkashin Harkar Qadiriyya
7. Majalisar Malaman Sunnah ta Kano
8. Multaqa Ahbab Alsufiyya

Kar ku dauki biyan haraji a matsayin horo ku dauke shi a matsayin hanya na Chigaba kasar Nigeria.Cewar shugaban hukumar ...
26/09/2025

Kar ku dauki biyan haraji a matsayin horo ku dauke shi a matsayin hanya na Chigaba kasar Nigeria.

Cewar shugaban hukumar tara haraji na Kasar Nigeria.

Da Dumi-Dumi: Bankin Zenith Reshen Jihar Yobe, Ya Baiwa Daliban Da S**a Yi Nasara A Gasar Turanci Ta Duniya Kyautar Nair...
26/09/2025

Da Dumi-Dumi: Bankin Zenith Reshen Jihar Yobe, Ya Baiwa Daliban Da S**a Yi Nasara A Gasar Turanci Ta Duniya Kyautar Naira Milyan biyar

Da Dumi-DumiHukumar zaben Nijeriya ta yi watsi da bukatar su Bulama Bukarti ta yi wa Tafiyar Matasa rajista a matsayin j...
26/09/2025

Da Dumi-Dumi

Hukumar zaben Nijeriya ta yi watsi da bukatar su Bulama Bukarti ta yi wa Tafiyar Matasa rajista a matsayin jam‘iyyar siyasa da sunan Access Party

Me zaku ce akan hakam???

Mataimakin Shugaban Kasa Sanata Kashim Shatima ya gana da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres a Bi...
26/09/2025

Mataimakin Shugaban Kasa Sanata Kashim Shatima ya gana da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres a Birnin New York kasar Amurka.

DA DUMI-DUMI: Abin Kunya, Dan Majalisar Tarayya na Ningi/Warji, Hon. Adamu Hashimu Ranga Na Jam’iyyar PDP, Ya Ce Bai San...
26/09/2025

DA DUMI-DUMI: Abin Kunya, Dan Majalisar Tarayya na Ningi/Warji, Hon. Adamu Hashimu Ranga Na Jam’iyyar PDP, Ya Ce Bai San Cewa Mutanen Yankinsa Sun Shekara Uku Ba Su Da wutan Nefa Ba

An samu ce-ce-ku-ce a siyasar Ningi/Warji bayan da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Ningi/Warji, Hon. Adamu Hashimu Ranga na jam’iyyar PDP, ya bayyana cewa bai san cewa al’ummarsa sun shafe kusan shekara uku ba tare da samun wutan nefa ba.

Wannan furuci nasa ya jawo ce-ce-ku-ce daga jama’a da kungiyoyin fararen hula, inda s**a nuna damuwa kan yadda wakili zai kasa sanin halin da jama’ar da yake wakilta ke ciki, musamman ganin irin rawar da wutan nefa ke takawa wajen sauƙaƙa rayuwar yau da kullum.

Wasu daga cikin al’ummar yankin sun bayyana cewa wannan al’amari na nuna akwai giɓi tsakanin shugabanni da al’umma, tare da nuna bukatar karin kusanci da tuntuba tsakanin masu wakilta da wadanda ake wakilta.

-Zamani TV

‎DA DUMI-DUMI: Majalisar Dokokin Jihar Bauchi Ta Buƙaci A Gabatar da Buƙatu Don Ƙirƙira Ko Dawowa da Kananan Hukumomi.‎‎...
25/09/2025

‎DA DUMI-DUMI: Majalisar Dokokin Jihar Bauchi Ta Buƙaci A Gabatar da Buƙatu Don Ƙirƙira Ko Dawowa da Kananan Hukumomi.

‎Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta buɗe ƙofa ga al’ummomi da ke sha’awar ganin an kirkira ko dawo da Kananan Hukumomi, da su gabatar da takardun bukata (memoranda) cikin mako biyu (2) daga ranar da aka fitar da wannan sanarwa.

‎Wurin karɓa:
‎Ofishin Mataimakin Magatakarda/Sakataren Majalisa, kusa da Gidan Gwamnati, Bauchi.

‎Abubuwan da takardar take bukata za ta ƙunsha:
‎- Sunan Karamar Hukumar da ake nema
‎- Takardar buƙata zuwa Shugaban Kwamitin Ad-hoc
‎- Kididdigar yawan jama’a
‎- Taswira da hotunan yankin
‎- Bayanin albarkatu da arzikin ƙasa
‎- Lissafin gundumomi da mazabu
‎- Sa hannun wakilan siyasa da na al’umma

‎Wannan mataki na da nufin ƙarfafa dimokuraɗiyya da ci gaban al’umma ta hanyar wakilci nagari.


‎-Kima Tv-

‎Wanne gari ne kuke so a bashi Karamar Hukuma???

Da dumi'dumi: Sheikh Pantami ya halarci taron jam’iyyar ADC a AbujaSheikh (Prof.) Isa Ali Pantami, tsohon Ministan Sadar...
25/09/2025

Da dumi'dumi: Sheikh Pantami ya halarci taron jam’iyyar ADC a Abuja

Sheikh (Prof.) Isa Ali Pantami, tsohon Ministan Sadarwa na Tarayya, ya bayyana a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar Action Democratic Congress (ADC) da aka gudanar yau Alhamis a birnin tarayya Abuja.

Taron, wanda ya tattaro manyan jiga-jigan jam’iyyar daga sassa daban-daban na ƙasar, ya mayar da hankali kan matsalolin da ke gaban jam’iyyar da shirin ta na tunkarar zaben 2027.

Me Zaku ce Akan Hakam???

ABUN BURGEWA: A Darazo, mabiya Shi’a wato Almajiran Sheikh Zakzaky, sun gudanar da wani gagarumin taro da suke kira Mako...
25/09/2025

ABUN BURGEWA: A Darazo, mabiya Shi’a wato Almajiran Sheikh Zakzaky, sun gudanar da wani gagarumin taro da suke kira Makon Haɗin Kai.

Taron ya samu halartar malamai, Fasto, da kuma sauran al’ummar gari daga sassa daban-daban.

Shin kuna daga cikin masu kishin ganin al’ummarsu na zaune cikin haɗin kai da fahimtar juna a wuri guda?

Dr. Haruna Maiwada Ya Bada Gaggarumin Tallafi Na Milyoyin Kudi Ga Al'ummar Jihar Katsina.tabbas Dr Maiwada ya cancanci y...
25/09/2025

Dr. Haruna Maiwada Ya Bada Gaggarumin Tallafi Na Milyoyin Kudi Ga Al'ummar Jihar Katsina
.tabbas Dr Maiwada ya cancanci yabo, inji Gwamna Dikko Radda a lokacin da yake kaddamar da bada tallafin

‎Dr. Haruna Umar Maiwada ya bada tallafin miliyoyin nairori ga al'ummar Katsina a yau Alhamis, inda taron ya wakana a filin wasa na Muhammad Dikko dake birnin Katsina.

Mutane kimanin 1,350 ne s**a amfana da tallafin motoci kirar Hijet 35, matoci 6, litattafai 20,000, mashina 100, injinan Markade 250, injinan taliya 500, da kuma mata masu kanana da matsakaitan masana'antu 700 da s**a amfana da tallafin zunzurutun kudi na naira miliyan talatin (₦30,000,000) hadi da tallafawa masu bukata ta musamman duk don habbaka tattalin arziki da kuma taimakawa kokarin Gwamnan jihar Katsina.

‎A yayin jawabinsa, Gwamanan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya yaba da kokarin da Haruna Maiwada ke yi, wanda yin hakan shine kowacce gwamnati ke kara samun cigaba idan ana samun ire-iren Dan Amanar Katsina, wanda hakan zai taimaka wajen samun sauki da kuma samar da sana'o'in dogaro da kai ga matasa maza da mata.

‎Gwamnan ya cigaba da cewa "ba mu yi mamaki ba saboda gado ka yi wajen mahaifan ka kuma uwar jam'iyyar APC tana godiya akan abinda kayi. Allah Ya kara daukaka Haruna Maiwada domin ya tallafi al'umma".

‎Daga karshe a madadin uwar jam'iyyar APC ta jihar Katsina, Alhaji Bala Abu Musawa ya godewa Dan Amanar Katsina akan wannan tallafi da ya bada, inda ya kara da cewa haka ake so duk wani mai hali ya yi.

‎Taron ya samu halartar shugaban karamar hukumar Katsina Hon. Isah Miqdad AD. Saude, Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Katsina Hon. Aliyu Abubakar Albaba, Alhaji Umar Tata, Engr. Muttaka Rabe Darma.

Sai kuma ‎Sarkin Sullubawan Katsina Alhaji Yazidu Abdul Kareem, Sheikh Yakubu Musa Hassan Katsina, Malam Abu Ammar shugaban hukumar Hisbah na Jihar Katsina, 'yan kasuwar. Da dai sauransu.

Daga ‎Muhammad Sani Ibrahim Kaita
‎Mataimaki na musamman ga Dr. Haruna Maiwada akan harkokin Sadarwa
‎ 25 ga watan Satumba 2025

MU TATTAUNA: Tsakanin Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara da Sheikh Abubakar Lawan Triumph, wanene ke bukatar adalci???Ku b...
25/09/2025

MU TATTAUNA: Tsakanin Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara da Sheikh Abubakar Lawan Triumph, wanene ke bukatar adalci???

Ku bayyana mana ra'ayinku a sashen sharhi!.

Address

Bauchi

Telephone

+2349133963242

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KIMA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KIMA TV:

Share