31/05/2026
HOTUNA: KUNGIYAR 'YAN AMALANKE ACADEMY DARAZO TA YI ZAGAYE A GARIN DARAZO DOMIN TAYA ARC. USMAN YA'U DARAZO MURNAR NASARA
Kungiyar 'Yan Amalanke Academy Darazo ta gudanar da tattakin zagaye a wasu sassan garin Darazo domin nuna farin cikinta da goyon baya ga dan takarar kujerar Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Darazo da Ganjuwa, Hon. Arc. Usman Ya'u Darazo, bayan nasarar da ya samu a zaben fidda gwani.
A yayin tattakin, mambobin kungiyar sun rika bayyana farin cikinsu tare da yabawa jagorancin Arc. Usman Ya'u Darazo, suna masu bayyana cewa nasarar da ya samu ta kara musu kwarin gwiwa da fata na ganin ci gaba da wakilci nagari ga al'ummar mazabar.
Shugaban kungiyar ya bayyana a Kima Tv cewa fitowar tasu ta nuna cikakken goyon baya da amincewa da takarar Arc. Usman Ya'u Darazo, yana mai cewa kungiyar za ta ci gaba da wayar da kai da hada kan matasa domin tabbatar da samun nasara a babban zaben da ke tafe.
Ya kara da cewa suna da yakinin cewa Arc. Usman Ya'u Darazo zai kawo ci gaba mai ma'ana ga al'ummar Darazo da Ganjuwa idan aka ba shi damar wakiltarsu.
Tattakin ya samu halartar dimbin matasa da magoya baya, inda s**a rika zagayawa cikin lumana tare da nuna farin ciki da murnar nasarar dan takarar.
- Kima Tv -