Madubi TV

Madubi TV Gidan Talabijin ne na intanet da zai riƙa kawo tarihi, fashin baƙi da labaran yau da kullum.

Zaman Miji a Dakin Haihuwa Na Rage Radadin Nakuda ga Matar Aure – MasanaMasana a fannin kiwon lafiyar uwa da haihuwa sun...
14/09/2025

Zaman Miji a Dakin Haihuwa Na Rage Radadin Nakuda ga Matar Aure – Masana

Masana a fannin kiwon lafiyar uwa da haihuwa sun bayyana cewa, bayar da dama ga mazaje su kasance a dakin haihuwa na taka muhimmiyar rawa wajen inganta lafiyar uwa da kuma ƙarfafa zumuncin iyali.

A cewar masana, k**ar yadda jaridar Punch ta rawaito, idan maza s**a shiga cikin tsarin haihuwa kai tsaye, hakan na taimakawa rage damuwar uwa da kuma ƙara mata ƙarfin guiwa a lokacin haihuwa.

Me za ku ce?

Rahama Saidu da mahaifinta a wajen buɗe sabon shagonta a Abuja
13/09/2025

Rahama Saidu da mahaifinta a wajen buɗe sabon shagonta a Abuja

Yanzu-Yanzu: Raini ko Karamci?Gwamnatin Tarayya, a ranar Alhamis, ta bai wa wadda ta lashe gasar TeenEagle Global Finals...
28/08/2025

Yanzu-Yanzu: Raini ko Karamci?

Gwamnatin Tarayya, a ranar Alhamis, ta bai wa wadda ta lashe gasar TeenEagle Global Finals, Nafisah Abdullahi, kyautar naira 200,000.

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya gabatar da wannan kyauta a wajen wani biki da aka gudanar a Abuja.

Idan za ku iya tunawa dai, cibiyar Atiku Foundation ta riga ta karrama zakarun gasar TeenEagle wato Nafisah Abdullahi, Rukaiya Fema da Khadija Kalli, da tallafin karatu cikakke saboda bajintar da s**a nuna a gasar TeenEagle Global Finals.

Me za ku ce??

Alhamdulillah! Madubi TV has officially received the award from YouTube that is Silver Play Button 🎉This award is not ju...
27/08/2025

Alhamdulillah! Madubi TV has officially received the award from YouTube that is Silver Play Button 🎉

This award is not just for us, but for every single one of you who believed in Madubi TV, watched our videos, subscribed, liked, commented, and shared our content. Without your support, this milestone of 100,000 subscribers would have been impossible.

We are humbled and grateful for this journey. This Silver Play Button is a reminder that with hard work, consistency, and the help of Allah, dreams do come true.

To all our loyal fans: this is your victory as much as it is ours.
To future supporters: the journey has just begun. Bigger goals ahead, In sha Allah. 🚀

Thank you, and may Allah bless you all abundantly.

2027: Zan tsaya takarar shugaban ƙasa – AtikuTsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa zai tsaya ...
25/08/2025

2027: Zan tsaya takarar shugaban ƙasa – Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa zai tsaya takarar shugaban ƙasa a shekarar 2027.

Ya bayyana hakan ne ta bakin ɗaya daga cikin masu magana da yawunsa a lokacin zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Tunde Olusunle.

Da yake magana da Jaridar ThisDay, Olusunle ya ce Atiku zai sake tsayawa takara a 2027 saboda Najeriya na bukatar ceto daga “ƙanshin mutuwar” da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ta.

Me za ku ce?

Waje ya yi shiru fa 😂😂 mutane suna ta jiran next episode.Dafatan kai ma kana amfana da podcast ɗin su??
22/08/2025

Waje ya yi shiru fa 😂😂 mutane suna ta jiran next episode.

Dafatan kai ma kana amfana da podcast ɗin su??

Jaruma Hadiza Aliyu GabonWani fata za ku yi mata?
17/08/2025

Jaruma Hadiza Aliyu Gabon

Wani fata za ku yi mata?

"Ko a Fim ɗin Indiya, Mutum Mai Mugunta Yana Burge Ni" — Hauwa Musa AdamA wata tattaunawa da BBC Hausa, fitacciyar jarum...
14/08/2025

"Ko a Fim ɗin Indiya, Mutum Mai Mugunta Yana Burge Ni" — Hauwa Musa Adam

A wata tattaunawa da BBC Hausa, fitacciyar jarumar Kannywood, Hauwa Musa Adam, ta bayyana irin yadda ta fara sha’awar harkar fim tun tana ƙaramar yarinya a garin Jos, Jihar Filato.

Hauwa, ‘yar asalin kabilar Birom, ta ce ta tsaya karatunta ne a matakin sakandare, amma rayuwa ta koya mata darussa masu amfani.

Ta yi aure amma ta fuskanci ƙalubale, inda daga bisani ta rabu da mijinta. Bayan rabuwar, wata abokiyar ta mai suna Hajara — wadda yanzu haka kwamishiniya ce a Jihar Bauchi — ta gabatar da ita ga kamfanin Hayas Film Production.

Daga nan aka kai ta Lenzcup, sannan yayanta ya samu mata aiki a gidan rediyo, duk ba tare da ta sanar da iyalanta ba.

Ta fara fitowa a fina-finan Hausa ne a cikin shirin Babban Kasa, inda ta haɗu da jaruma Daso a karo na farko. “Na yi mamakin ganin ta sosai har sai da na buga kaina da murfin taga,” in ji ta cikin dariya.

Hauwa ta ce ƙalubalen da ta fi fuskanta a harkar fim shi ne yawan sauya kaya don ɗaukar gurare daban-daban.

Sai dai ta bayyana cewa abinda ya fi faranta mata rai shi ne yadda mahaifinta ya karɓi harkarta da hannu biyu, bayan jin an yi hira da ita ba tare da ta boye asalinta da yarenta ba.

“Mahaifina ya ce in ci gaba da yin fim ɗina, Allah ya sa a samu albarka,” in ji ta.

A cikin hirar, Hauwa ta bayyana wata dabi’a: “Ni ko a fina-finan Indiya, mutum mai mugunta yana burge ni,” in ji ta.

Jarumar ta ce babu abin da ya fi damunta a yanzu fiye da rashin mahaifi da mahaifiya, sai dai ta ce tana samun kwanciyar hankali idan ta yi wani abu da ta san zai faranta musu rai.

Ta kuma bayyana burinta na zama k**ar Laylah Ali Othman, matar wani ɗan majalisa a Jos, wadda ta shahara wajen taimakon al’umma.

Shawarar da ta bai wa sauran jaruman Kannywood ita ce su kasance masu tsoron Allah a duk inda suke da kuma a duk abin da suke yi.

Arewacin Najeriya na nuna cikakkiyar gamsuwa da tsarin tafiyar da mulkin Shugaban Ƙasa inji Daniel Bwala, Mashawarci na ...
14/08/2025

Arewacin Najeriya na nuna cikakkiyar gamsuwa da tsarin tafiyar da mulkin Shugaban Ƙasa inji Daniel Bwala, Mashawarci na Musamman kan Harkokin Yaɗa Manufofi ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Bwala yana mayar da martani ne a hirarsa da Channels TV kan s**a da ake yi wa gwamnatin Tinubu dangane da zargin nuna son kai wajen raba muk**ai.

Me za ku ce?

‘Yan sanda sun k**a na'ibin Liman kan zargin haɗin baki da ‘yan bindiga a SokotoJami’an tsaro sun k**a Sirajo Ahmad Dan ...
13/08/2025

‘Yan sanda sun k**a na'ibin Liman kan zargin haɗin baki da ‘yan bindiga a Sokoto

Jami’an tsaro sun k**a Sirajo Ahmad Dan Liman, Na'ibin Babban Limamin Masallacin Jumu’ah na Kangiye da ke gundumar Atakwanyo, ƙaramar hukumar Gwadabawa, jihar Sokoto, bisa zargin haɗin baki da ‘yan bindiga.

Binciken sirri ya gano cewa Sirajo na da hannu dumu-dumu wajen samar wa ‘yan bindiga babura da sauran muhimman kayayyaki da suke amfani da su a yankin iyakar Tangaza da Jamhuriyar Nijar.

Rahotanni da Zagazola Mak**a ya tattara sun ce an gano Naira miliyan 47 a cikin asusun bankinsa, waɗanda ake zargin sun fito ne daga hulɗarsa da waɗannan miyagu.

Bincike ya ƙara nuna cewa Sirajo shugaba ne na jam’iyyar siyasa a gundumar Atakwanyo, kuma shi ne sakataren ƙungiyar shugabannin jam’iyyun siyasa na ƙaramar hukumar Gwadabawa.

Majiyoyi sun bayyana cewa Siradi ya kan gudanar da wa’azi a Kangiye musamman a lokacin Ramadan, kuma sau da dama yana rike limanci da wa’azi a madadin mahaifinsa wanda shi ne Babban Limamin.

Me za ku ce?

Sutura ta mutunci tana ɗaya daga cikin manyan kayan kare martabar mace. Idan mace ta rufe jikinta yadda ya dace, k**ar a...
13/08/2025

Sutura ta mutunci tana ɗaya daga cikin manyan kayan kare martabar mace.

Idan mace ta rufe jikinta yadda ya dace, k**ar alewar da aka nade take — ta samu tsaro daga ƙazanta, barna da kuma kallon banza.

Amma idan ta fito ba tare da sutura ta dace ba, tana k**a da alewar da aka bari a buɗe, wanda kowa zai iya taɓa shi ko lalata shi.

Mutunci da tsaron mace suna fara ne daga yadda take kula da jikinta da suturarta.

Me za ku ce??

13/08/2025

Jama'a ku ce Alhamdulillah

Maha fa ya farfaɗo 😁😁

Address

Bauchi
740102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madubi TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share