ADAP TV News 24

ADAP TV News 24 ADAP TV News 24, Kafar labarai ce mai tushe da kuke dogaro da ita. 08149010243

Hon. Faruq Mustapha a yau ya karɓi dubban mambobin jam’iyyar APC da s**a sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP mai mulki.Masu s...
31/10/2025

Hon. Faruq Mustapha a yau ya karɓi dubban mambobin jam’iyyar APC da s**a sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP mai mulki.

Masu sauya shekan, ƙarƙashin jagorancin Hon. Nura Ganaru, sun bayyana rashin haɗin kai a cikin jam’iyyar APC da rikice-rikicen siyasa a matsayin manyan dalilan da s**a sa s**a fice daga jam’iyyar.

ADAP TV News 24

Jam’iyyar PDP ta bayyana rashin jin daɗinta kan hukuncin da Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a K...
31/10/2025

Jam’iyyar PDP ta bayyana rashin jin daɗinta kan hukuncin da Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Kolawole Omotosho ta yanke a yau, tana mai kiran hukuncin a matsayin hari ga tsarin dimokuraɗiyya a Najeriya.

Sai dai PDP ta bayyana cewa wannan hukunci ba ya hana jam’iyyar ci gaba da shirye-shiryen gudanar da babban taron ta na kasa (National Convention) domin zaɓen sababbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa.

Kamar yadda ADAP ta ruwaito jam’iyyar ta tunatar da hukuncin Kotun Koli na baya-bayan nan wanda ya tabbatar da 'yancin jam’iyya wajen tafiyar da al’amuranta na cikin gida ba tare da tsoma baki ba.

Don haka PDP ta umarci mambobinta, shugabannin rassan jam’iyyar da dukkan sassa, da su kasance cikin haƙuri, jajircewa da mayar da hankali wajen shirye-shiryen gudanar da babban taron kasa.

Sai dai a matsayinta na babbar jam’iyyar adawa mai kishin gaskiya da bin doka, PDP ta bayyana cewa ta ba lauyoyinta umarnin daukaka kara nan take, domin ci gaba da kare dimokuraɗiyya da tsarin jam’iyyu masu yawa a kasar.

ADAP TV News 24

Cikakken Bayani Kan Hukuncin Kotun Koli Dangane da Shari’ar Babban Taron Gangamin PDP a YauMuhimman Abubuwan da Hukuncin...
31/10/2025

Cikakken Bayani Kan Hukuncin Kotun Koli Dangane da Shari’ar Babban Taron Gangamin PDP a Yau

Muhimman Abubuwan da Hukuncin Kotun ya Kunsa

1. Iko da Hurumin Kotu
Kotun ta tabbatar da cewa tana da hurumin sauraron wannan ƙara, domin batutuwan da aka gabatar suna cikin ikon da Kundin Tsarin Mulki ya bata don yanke hukunci.

2. Lauyan Hukuma na Jam’iyya
Kotun ta sake tabbatar da cewa Ajibade, SAN, shi ne lauya na doka kuma wanda aka amince da shi a hukumance a matsayin wakilin jam’iyyar PDP. Wannan matsayi kotun ta tabbatar da shi cikin hukuncinta.

3. Matsayin Ali Odefa
Kotun ta bayyana cewa Mista Ali Odefa, tunda aka kore shi daga jam’iyyar, ba shi da ikon gudanar da ayyuka ko bayyana kansa a matsayin Shugaban Yankin Kudu maso Gabas ko wani jami’in jam’iyyar a kowane matsayi.

4. Rashin Cancanta a Hada Shi da Ƙarar
Kotun ta yanke cewa Odefa ba shi da wani matsayin doka da zai sa a haɗa shi cikin shari’ar, domin tuni an kore shi daga jam’iyyar. Saboda haka, ba shi da wata masaniya ta doka da ta shafe shi a cikin lamarin.

5. Kan Zargin Tsoma Baki a Cikin Harkokin Cikin Gidan Jam’iyya
Kotun ta bayyana cewa masu shigar da ƙarar ba sa kalubalantar gudanarwa ko tsarin cikin gida na jam’iyyar. Sai dai suna neman tabbatar da cewa jam’iyyar tana bin doka da kundinta wajen gudanar da dukkan ayyukanta.

6. Yanayin Shari’ar
Kotun ta ƙara bayyana cewa wannan shari’ar ba ta cikin abubuwan da s**a shafi harkokin cikin gida na jam’iyya kai tsaye. A maimakon haka, ta shafi wajabcin jam’iyyar ta bi doka da kundinta wajen ɗaukar duk matakai da yanke shawara.

Kotun ta jaddada cewa doka da kundin tsarin jam’iyya su ne ginshiƙan tafiyar da harkokin cikin gida, kuma babu mutum ko ƙungiya da ta fi waɗannan doka ƙarfi.

7. Batun Gudanar da Zabe ba tare da INEC ba
Kotun ta kuma yanke cewa duk wani taron jam’iyya (kongires) da aka gudanar a kowace jiha ba tare da halartar hukumar INEC ba, babu ingancinsa wato null and void. Saboda haka, duk wata takardar da jam’iyyar ke aikawa INEC dole sai Shugaban jam’iyya na ƙasa da Sakatare Janar s**a sanya hannu.

8. Taron Ibadan
Kotun ta ƙara yanke cewa jam’iyyar PDP ba za ta iya ci gaba da shirya babban taron ƙasa da aka tsara a Ibadan ba, sai ta gyara cikin gidanta, ta daidaita dukkan matakan cikin gida, sannan ta sanar da INEC yadda doka ta tanada.

Babbar Kotun Tarayya dake Abuja a ranar Juma’a ta ƙi amincewa da buƙatar da tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya...
31/10/2025

Babbar Kotun Tarayya dake Abuja a ranar Juma’a ta ƙi amincewa da buƙatar da tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya shigar, inda yake neman a hana jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ci gaba da shirinta na gudanar da taron gangamin ƙasa da aka tsara.

DA DUMI DUMI: Kotu ta Dakatar da Taron Gangamin PDPBabbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarni ga jam’iyyar Peop...
31/10/2025

DA DUMI DUMI: Kotu ta Dakatar da Taron Gangamin PDP

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarni ga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da ta dakatar da gudanar da taron gangaminta da aka shirya yi a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, a watan gobe.

Babbar kotun jiha dake Miller Road a Kano, karkashin jagorancin Mai Shari’a Musa Dahiru, ta tura wani magidanci gidan gy...
31/10/2025

Babbar kotun jiha dake Miller Road a Kano, karkashin jagorancin Mai Shari’a Musa Dahiru, ta tura wani magidanci gidan gyaran hali bisa zarginsa da kashe matarsa, bayan ya ce ta ki daka masa ƙuli-ƙuli kamar yadda ya buƙata.

Freedom Radio ta rawaito cewa magidancin, mai suna Idris Kurma, ya gurfana a gaban kotun dauke da takardar tuhumar kisan kai, wanda ya saba da sashi na 221 na kundin hukunta laifuka.

Lauyan gwamnati, Barista Lamido Abba Soron Dinki, ne ya gabatar da karar, inda bayan karanto masa takardar tuhumar, wanda ake tuhumar ya musanta aikata laifin.

Lauyan gwamnati ya roki kotu ta ba su lokaci domin su kawo shaidu. A nasa bangaren, Barista Ibrahim Adakawa, wanda yake kare wanda ake tuhuma, ya roki kotu ta basu cikakken bayani kan shari’ar.

Kotun ta amince da rokon lauyoyin sannan ta sanya ranar 12 ga Disamba, 2025, domin sake gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban kotu.

Ana dai zargin Idris Kurma wanda yake zaune a garin Goda, cikin karamar hukumar Shanono, da kashe matarsa Aisha Idris, bayan ya umarceta da ta daka masa kuli-kuli amma ta ki yin hakan. A cewar rahotanni, hakan ne ya sa ake zargin ya shaketa, wanda kuma ya haifar da mutuwarta.

Kotu ta sauke dan majalisar wakilai daga jihar Zamfara daga kujerarsa bayan ya sauya sheka daga PDP zuwa APCBabbar Kotun...
31/10/2025

Kotu ta sauke dan majalisar wakilai daga jihar Zamfara daga kujerarsa bayan ya sauya sheka daga PDP zuwa APC

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige ɗan majalisa Abubakar Gummi, bisa sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Gummi shi ne ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a Majalisar Wakilai ta Tarayya.

RIKICI A JAM'IYAR PDP: Gwamna Bala da Damagum sun halarci zaman kotu yayin da ake jiran hukuncin shari’ar taron gangamin...
31/10/2025

RIKICI A JAM'IYAR PDP: Gwamna Bala da Damagum sun halarci zaman kotu yayin da ake jiran hukuncin shari’ar taron gangamin kasa na PDP

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Umar Iliya Damagum, tare da Shugaban taron gwamnonin PDP, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, da sauran mambobin kwamitin zartarwa na kasa (NWC) sun halarci zaman kotu a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a yau, jim kadan kafin yanke hukunci kan muhimmin karar da ake saurare.

Kotun na shirin yanke hukunci ne kan karar da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP daga jihohin Abia, Imo da Bayelsa s**a shigar, inda suke neman a dakatar da gudanar da taron gangamin kasa na PDP na shekarar 2025 da aka tsara gudanarwa a birnin Ibadan, Jihar Oyo.

Cikakkun bayanai na nan tafe.

GAYYATAR NADIN SARAUTA!Iyalan marigayi Alhaji Adamu Kuda (Dallatun Katagum) Suna gayyatar ƴan'uwa da abokan arziki zuwa ...
31/10/2025

GAYYATAR NADIN SARAUTA!

Iyalan marigayi Alhaji Adamu Kuda (Dallatun Katagum)

Suna gayyatar ƴan'uwa da abokan arziki zuwa wajen naɗin sarautar Alhaji Habu Kuda a matsayin (Dallatun Katagum) Da Alhaji Abdullahi Kuda a matsayin (Sarkin Hanyar Katagum)

Za'a yi ranar Asabat, 15 Nuwamba 2025 a fadar mai martaba sarkin katagum, Alhaji Dr. Umar Farooq II OON

Da misalin ƙarfe 11:00am na safe.

Sanarwa Daga Kamal Ahmad Azare, Hadimin Alhaji Abdullahi Kuda (Sarkin Hanyar Katagum) a kafar sadarwa ta zamani. Allah ya bada ikon halarta Aamin.

SEN. NATASHA AKPOTI TA GABATAR DA RABON KAYAYYAKI TARE DA BUDE MANYAN AYYUKA A KOGIBayan dawo wa daga dakatar da ita da ...
31/10/2025

SEN. NATASHA AKPOTI TA GABATAR DA RABON KAYAYYAKI TARE DA BUDE MANYAN AYYUKA A KOGI

Bayan dawo wa daga dakatar da ita da aka yi ba tare da wani jinkiri ba, Sanata Natasha Akpoti, wacce ke wakiltar Kogi Central a Majalisar Dattawa, ta gudanar da gagarumin taron rabon kayayyaki da kuma bude manyan ayyuka a mazabar ta.

Sanata Natasha ta gayyaci Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, tare da sauran abokan aikinta domin halartar kaddamar da wadannan muhimman ayyuka da s**a hada da gina hanyoyi, samar da ruwa, da tallafawa al’umma da kayan sana’a.

Wannan lamari ya samu halartar jama’a da dama, inda aka yaba da irin kokarin Sanatar wajen inganta rayuwar mutanen mazabar Kogi Central, musamman bayan dawowarta daga dakatarwar da ta fuskanta a baya.

ADAP TV News 24

HOTUNA: Kowa da aikin sa, yadda shugaban ƙaramar hukumar Roni a jihar Jigawa gwangwaje al'ummarsa da baron sayar da ruwa...
31/10/2025

HOTUNA:

Kowa da aikin sa, yadda shugaban ƙaramar hukumar Roni a jihar Jigawa gwangwaje al'ummarsa da baron sayar da ruwa domin dogaro da kai.

Tinubu mai mutum ne mai wayo wajen tara haraji, ba abin mamaki ba ne idan nan gaba ya fara karɓar harajin iska wato iska...
30/10/2025

Tinubu mai mutum ne mai wayo wajen tara haraji, ba abin mamaki ba ne idan nan gaba ya fara karɓar harajin iska wato iskar da muke shaƙa idan ba mu yi hankali ba.

Adewole Adebayo, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar SDP a shekarar 2023 yayi wannan jawabine a yayin da ake zantawa dashi a tashar (Channels Television)

Me zaku ce akai ?

Address

Bauchi
6006

Telephone

+2348149010243

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ADAP TV News 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ADAP TV News 24:

Share