ADAP TV News 24

ADAP TV News 24 ADAP TV News 24, Kafar labarai ce mai tushe da kuke dogaro da ita. Zaku Iya Tuntubar mu Akoda yaushe ku danna Like 👍ko follow👍 08149010243

JARIDA

Shirye shiryen mu: Siyasa, Kasuwanci, Fadakarwa Tare da Ilmantar wa, Tallace Tallace, Cikiya Da Sanarwa.

CIKIYA CIKIYA CIKIYAAslm yan Uwa Da Abokan Arziki Muna Bada Cikiyar Wannan Bawan Allah Mai Suna Sadisu Muhammad Sadi Gam...
30/07/2026

CIKIYA CIKIYA CIKIYA

Aslm yan Uwa Da Abokan Arziki Muna Bada Cikiyar Wannan Bawan Allah Mai Suna Sadisu Muhammad Sadi Gambaki Ranar Monday Data Bagata Ya Bar Gida Kuma Har Yau Babu Labari Duk Yadda Ake Tunanin Jin Wani Labarin Sa Har Yanzu Babu Muna Rokon Dan Allah Duk Wanda Ya Gan Shi Ko Yaji Labari Ya Kira Wannan Number 09068568888 07076777879.

Dan Allah A Tayamu Share Ko post

Allah Ubangiji Ya Bayyana Mana Shi Yasa Yana Cikin Koshin Lafiya. Daga Muktar Dan Galadiman Gambaki.

An yi Allah wadai da rahotannin dukan jami'in gwamnatin Delta kan yabon gwamnatin TinubuAn bayyana Allah wadai kan rahot...
29/07/2026

An yi Allah wadai da rahotannin dukan jami'in gwamnatin Delta kan yabon gwamnatin Tinubu

An bayyana Allah wadai kan rahotannin da ke cewa wasu matasa sun lakada wa Jami'in Kula da Tsare-tsare (Protocol Officer) na Gwamnan Jihar Delta, Mista Tempo Mudi, duka, bayan ya bayyana a taron shugabannin APC na jihar cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ita ce mafi alheri ga 'yan Najeriya.

Rahoton ya jaddada cewa idan labarin ya tabbata, hakan ya saba wa ka'idar dimokuradiyya da 'yancin faɗar albarkacin baki. An kuma ce duk wanda bai amince da ra'ayin ba ya kamata ya mayar da martani da hujjoji da tattaunawa, ba tashin hankali ba. Duk da cewa mutane na da 'yancin s**ar ra'ayinsa, amfani da tashin hankali ba shi da gurbi a cikin dimokuradiyya.

Idan kai cikekken dan Bauchi ne, inane nan...??
23/07/2026

Idan kai cikekken dan Bauchi ne, inane nan...??

Aluta Professor (Tsohon Shugaban Daliban BUK) ya jagoranci dubban magoya bayan jam'iyyar APC gudanar da Zanga-zangar lum...
23/07/2026

Aluta Professor (Tsohon Shugaban Daliban BUK) ya jagoranci dubban magoya bayan jam'iyyar APC gudanar da Zanga-zangar lumana yau a Kano, don yin Allah wadai da kalaman batanci da cin mutunci da aka yiwa Sanata Barau Jibrin Maliya.

Freedom Radio Nigeria

Azare, Bauchi: Wata ƙungiya mai suna SDCI ta wallafa wasu bayanai da s**a nuna cewa Ƙaramar Hukumar Katagum ta karɓi jim...
23/07/2026

Azare, Bauchi: Wata ƙungiya mai suna SDCI ta wallafa wasu bayanai da s**a nuna cewa Ƙaramar Hukumar Katagum ta karɓi jimillar Naira biliyan 7.74 (₦7.74bn) daga rabon kuɗaɗen FAAC da Gwamnatin Tarayya ke bai wa ƙananan hukumomi a duk wata, tun daga farkon shekarar 2025 zuwa yanzu.

A cewar ƙungiyar, an gabatar da waɗannan bayanai ne ta hanyar zane-zanen bayanai (data visualization) domin sauƙaƙa wa al'umma fahimtar yawan kuɗaɗen da ke shigowa ƙaramar hukumarsu da kuma yadda ya kamata a yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan ci gaba.

Rahoton ya bayyana cewa, duk da kasancewar Katagum ce ke ɗauke da garin Azare, ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin kasuwanci a Jihar Bauchi, har yanzu al'ummar yankin na fuskantar matsalolin ambaliya da kuma yawan cunkoso da lalacewar Babbar Hanyar Kano Maiduguri. A cewar rahoton, waɗannan matsaloli na ci gaba da yin tasiri ga rayuwar al'umma, zirga-zirga da harkokin kasuwanci.

SDCI ta bayyana cewa fitar da bayanan na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi da aka tsara yi a ranar 17 ga Agusta, inda ta ce manufarta ita ce ƙarfafa al'umma su fahimci kuɗaɗen da ƙaramar hukumarsu ke karɓa tare da ƙara wayar da kai kan irin ayyukan da ya kamata su buƙaci shugabanninsu su aiwatar domin ci gaban yankinsu.

Yanzu haka ni'imar ruwan sama ta sauƙa a garin Azare.
22/07/2026

Yanzu haka ni'imar ruwan sama ta sauƙa a garin Azare.

Mai martaba sarkin katagum Alhaji Umar Farooq II OON yabi sahun sallar rokon ruwa da yasa aka kira yau a garin Azare.
22/07/2026

Mai martaba sarkin katagum Alhaji Umar Farooq II OON yabi sahun sallar rokon ruwa da yasa aka kira yau a garin Azare.

Gwamna Bala Mohammed Ya Yi Sauye-Sauye Kaɗan a Majalisar Zartarwar Jihar BauchiGwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulka...
17/07/2026

Gwamna Bala Mohammed Ya Yi Sauye-Sauye Kaɗan a Majalisar Zartarwar Jihar Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, CON, FNIPR (Kauran Daular Usumaniyya), ya amince da yin wasu ƙananan sauye-sauye a cikin Majalisar Zartarwar Jihar domin ƙara inganta harkokin mulki da kuma tabbatar da ingantaccen isar da ayyukan gwamnati ga al'ummar jihar.

A cewar wata sanarwar da Fadar Gwamnatin Jihar Bauchi ta fitar, sauye-sauyen sun haɗa da ficewar Kwamishinan Kasuwanci, Masana'antu da Zuba Jari, Alhaji Mohammed Salis Gamawa, da kuma tsohon Kwamishinan Ilimi wanda daga baya aka mayar Ma'aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha, Dakta Mohammed Lawal Rimin Zayam, daga Majalisar Zartarwar Jihar, kuma matakin ya fara aiki nan take.

Hakazalika, Gwamna Bala Mohammed ya amince da murabus ɗin tsohon Kwamishinan Raya Karkara da Ayyuka na Musamman, Hon. Faruk Mustapha.

Sanarwar ta ƙara da cewa, domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati ba tare da tsaiko ba, Gwamnan ya miƙa sunayen waɗanda aka zaɓa domin maye gurbin waɗanda s**a fice, tare da sunayen wasu sababbin waɗanda za su cike guraben da s**a samu sakamakon ficewar wasu kwamishinoni a baya, zuwa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi domin tantancewa da tabbatar da su.

Gwamna Bala Mohammed ya bayyana matuƙar godiyarsa ga kwamishinonin da s**a bar mukamansu bisa sadaukarwa, jajircewa da gudummawar da s**a bayar wajen ci gaban Jihar Bauchi a lokacin da suke kan aiki.

Ya kuma yi musu fatan alheri a rayuwarsu ta gaba, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da za su ƙara inganta shugabanci, inganta ayyukan gwamnati, da kuma samar da romon dimokuraɗiyya ga al'ummar Jihar Bauchi.

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta soke hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta bayyana wasu ka'idojin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (...
16/07/2026

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta soke hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta bayyana wasu ka'idojin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a matsayin marasa inganci, tare da tabbatar da cewa ka'idojin za su ci gaba da aiki a zaɓen shekarar 2027.

A hukuncin da alkalan kotun uku s**a yanke baki ɗaya, kotun ta ce Jam'iyyar Youth Party (YP) ba ta da hurumin shigar da ƙarar, domin ba ta nuna yadda ka'idojin INEC s**a cutar da ita ko kuma s**a shafi zaɓukan fidda gwani da gabatar da 'yan takararta ba.

Kotun ta kuma bayyana cewa Babbar Kotun Tarayya ta yi kuskure wajen soke jadawalin INEC na gudanar da zaɓukan fidda gwani da kuma wa'adin gabatar da rajistar mambobin jam'iyyu.

Tun da farko, INEC ta ɗaukaka ƙara bayan Babbar Kotun Tarayya ta bayyana cewa wasu daga cikin ka'idojin da hukumar ta fitar sun saɓa da tanade-tanaden Dokar Zaɓe ta 2026.

Da wannan hukunci na Kotun Ɗaukaka Ƙara, ka'idojin INEC na shirya babban zaɓen 2027 sun dawo da cikakken inganci.

Harin 'Yan Sara-Suka a Tsakuwa: An Sake Yanke Kafar Wani Matashi a Teaching Hospital AzareAna ci gaba da kula da mutanen...
12/07/2026

Harin 'Yan Sara-Suka a Tsakuwa: An Sake Yanke Kafar Wani Matashi a Teaching Hospital Azare

Ana ci gaba da kula da mutanen da harin 'yan sara-s**a ya rutsa da su a unguwar Tsakuwa, Azare, inda wasu daga cikin waɗanda s**a jikkata ke ci gaba da karɓar magani a Asibitin koyar wa da kimiyyar fasaha na Azare.

Bayanai sun nuna cewa kwanaki biyu da s**a gabata, ɗaya daga cikin waɗanda harin ya shafa, mai suna Sufee, an yanke masa ƙafa sakamakon munanan raunukan da ya samu.

Haka kuma, a ranar jiya, likitoci a Azare sun sake yanke ƙafar wani matashi mai suna Sadik Sa'idu Waziri, bayan raunukan da ya samu a harin sun tsananta. Hakan ya sa ya zama mutum na biyu da wannan mummunan hari ya jawo masa rasa wani sashe na jikinsa.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗannan matasa suna barci ne a ƙofar gidansu lokacin da maharan s**a kai harin, lamarin da ya jefa su cikin mummunar jarabawa tare da haifar musu da raunuka masu tsanani.

Al'umma na ci gaba da nuna alhini kan wannan lamari tare da yin addu'ar Allah Ya ba waɗanda s**a jikkata cikakkiyar lafiya, Ya ba su ƙarfin jure wannan ƙalubale, sannan Ya tabbatar da adalci ga duk wanda wannan ta'addanci ya shafa.

Address

Bauchi
6006

Telephone

+2348149010243

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ADAP TV News 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ADAP TV News 24:

Share