29/05/2026
Sponsored:
A KAN WACCE MANUFA KO WATA RIBA ZA MU SAKE SHIGA TAFIYAR SABON ƊAN TAKARA A MAI ROGO ?
Shin bashin da muke bi na baya ma an biya ne? Ko kuwa ana son mu sake ɗaura wa kanmu nauyin da tun farko ya gagare mu ɗauka ne , kuma yanzu ya sake ƙaruwa?
Har yau ba a biya wahalhalunmu da sadaukarwar da muka yi tsawon shekaru takwas ba, amma kuma a sake neman mu shiga wani sabon ciniki marar tabbas?
Tambayoyi sun cika min kai matuƙa. Wasu na ganin kamar girma da mutuncinmu ya rataya ne a kan wasu, alhali kuwa ba mu samu wata dama ta musamman da za mu jingina rayuwarmu gare su ba. Kowa da yadda Allah yake rufa masa asiri, amma saboda mu na rufe wasu asirai cikin hikima da mutunci, sai a ɗauka kamar su ne ke ɗawainiya da rayuwarmu.
Siyasa ta wuce anfani da mutane kawai. Ya ku ƴan’uwa matasa, idan ba mu yi hankali yanzu ba, watakila ba za mu sake samun damar yin hakan ba. Wannan ne lokacin gyara tunani, gyara manufa da kuma tsarkake niyya.
Babu wanda zai ce mun gaza wajen haƙuri ko kuma mun cika yawan ƙorafi, musamman a kan wannan batu, domin yau mun shafe kusan shekaru bakwai tun kafuwar wannan gwamnati.
Biyayyata tana nan daram, musamman ga ubangidana, amma wannan magana ce ta gaskiya da nuna damuwa kan makomar abin da ake son cimmawa.
Kamal Ahmad Azare