17/07/2026
Gwamna Bala Mohammed Ya Yi Sauye-Sauye Kaɗan a Majalisar Zartarwar Jihar Bauchi
Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, CON, FNIPR (Kauran Daular Usumaniyya), ya amince da yin wasu ƙananan sauye-sauye a cikin Majalisar Zartarwar Jihar domin ƙara inganta harkokin mulki da kuma tabbatar da ingantaccen isar da ayyukan gwamnati ga al'ummar jihar.
A cewar wata sanarwar da Fadar Gwamnatin Jihar Bauchi ta fitar, sauye-sauyen sun haɗa da ficewar Kwamishinan Kasuwanci, Masana'antu da Zuba Jari, Alhaji Mohammed Salis Gamawa, da kuma tsohon Kwamishinan Ilimi wanda daga baya aka mayar Ma'aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha, Dakta Mohammed Lawal Rimin Zayam, daga Majalisar Zartarwar Jihar, kuma matakin ya fara aiki nan take.
Hakazalika, Gwamna Bala Mohammed ya amince da murabus ɗin tsohon Kwamishinan Raya Karkara da Ayyuka na Musamman, Hon. Faruk Mustapha.
Sanarwar ta ƙara da cewa, domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati ba tare da tsaiko ba, Gwamnan ya miƙa sunayen waɗanda aka zaɓa domin maye gurbin waɗanda s**a fice, tare da sunayen wasu sababbin waɗanda za su cike guraben da s**a samu sakamakon ficewar wasu kwamishinoni a baya, zuwa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi domin tantancewa da tabbatar da su.
Gwamna Bala Mohammed ya bayyana matuƙar godiyarsa ga kwamishinonin da s**a bar mukamansu bisa sadaukarwa, jajircewa da gudummawar da s**a bayar wajen ci gaban Jihar Bauchi a lokacin da suke kan aiki.
Ya kuma yi musu fatan alheri a rayuwarsu ta gaba, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da za su ƙara inganta shugabanci, inganta ayyukan gwamnati, da kuma samar da romon dimokuraɗiyya ga al'ummar Jihar Bauchi.