ADAP TV News 24

ADAP TV News 24 ADAP TV News 24, Kafar labarai ce mai tushe da kuke dogaro da ita. Zaku Iya Tuntubar mu Akoda yaushe ku danna Like 👍ko follow👍 08149010243

JARIDA

Shirye shiryen mu: Siyasa, Kasuwanci, Fadakarwa Tare da Ilmantar wa, Tallace Tallace, Cikiya Da Sanarwa.

Sponsored: A KAN WACCE MANUFA KO WATA RIBA ZA MU SAKE SHIGA TAFIYAR SABON ƊAN TAKARA A MAI ROGO ?Shin bashin da muke bi ...
29/05/2026

Sponsored:

A KAN WACCE MANUFA KO WATA RIBA ZA MU SAKE SHIGA TAFIYAR SABON ƊAN TAKARA A MAI ROGO ?

Shin bashin da muke bi na baya ma an biya ne? Ko kuwa ana son mu sake ɗaura wa kanmu nauyin da tun farko ya gagare mu ɗauka ne , kuma yanzu ya sake ƙaruwa?

Har yau ba a biya wahalhalunmu da sadaukarwar da muka yi tsawon shekaru takwas ba, amma kuma a sake neman mu shiga wani sabon ciniki marar tabbas?

Tambayoyi sun cika min kai matuƙa. Wasu na ganin kamar girma da mutuncinmu ya rataya ne a kan wasu, alhali kuwa ba mu samu wata dama ta musamman da za mu jingina rayuwarmu gare su ba. Kowa da yadda Allah yake rufa masa asiri, amma saboda mu na rufe wasu asirai cikin hikima da mutunci, sai a ɗauka kamar su ne ke ɗawainiya da rayuwarmu.

Siyasa ta wuce anfani da mutane kawai. Ya ku ƴan’uwa matasa, idan ba mu yi hankali yanzu ba, watakila ba za mu sake samun damar yin hakan ba. Wannan ne lokacin gyara tunani, gyara manufa da kuma tsarkake niyya.

Babu wanda zai ce mun gaza wajen haƙuri ko kuma mun cika yawan ƙorafi, musamman a kan wannan batu, domin yau mun shafe kusan shekaru bakwai tun kafuwar wannan gwamnati.

Biyayyata tana nan daram, musamman ga ubangidana, amma wannan magana ce ta gaskiya da nuna damuwa kan makomar abin da ake son cimmawa.

Kamal Ahmad Azare

DA DUMI DUMI: Atiku Abubakar ya lashe zaɓen fitar da gwani na ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyar ADC
27/05/2026

DA DUMI DUMI:

Atiku Abubakar ya lashe zaɓen fitar da gwani na ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyar ADC

A yau ne Mai Girma Mohammed Abdullahi Abubakar ya halarci Sallar Babbar Sallah a Babban Masallacin Idi na Bauchi tare da...
27/05/2026

A yau ne Mai Girma Mohammed Abdullahi Abubakar ya halarci Sallar Babbar Sallah a Babban Masallacin Idi na Bauchi tare da rakiyar manyan jiga-jigan siyasa, kungiyoyi da dubban magoya baya daga sassa daban-daban na Jihar Bauchi.

Daga cikin wadanda s**a raka shi akwai Shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress na Jihar Bauchi, Muhammad Alhassan Tilde, tare da Yakubu Abdullahi Shehu Wakilin Birni, Abdullahi Sirajo Jibrin, da kuma kungiyoyin goyon baya irin su MA Social Media, MA Boys, Mommy Boys da sauran matasa masu kauna da biyayya ga jagoran.

Bayan idar da Sallar Idi, al’umma sun raka Mai Girma Makama Babba zuwa gida inda ya gudanar da hotunan Sallah tare da Uwargidansa, HE Hajiya Khadija Mohammed Abdullahi Abubakar SAN, sannan ya kai ziyara gidan amaryarsa Barrister Aisha Mohammed Abdullahi Abubakar SAN domin ci gaba da bukukuwan Sallah tare da iyalai da masoya.

A sakonsa na Babbar Sallah, Mai Girma Makama Babba ya taya al’ummar Musulmi murna tare da addu’ar Allah Ya karbi ibadu, Ya maimaita mana wannan lokaci cikin zaman lafiya da ci gaban Jihar Bauchi.

HOTUNA: Yadda jam'iyyar PRP ta tabbatar da Sanata Shehu Buba a matsayin dan takarar gwamnan jihar Bauchi, Shehu Aliyu Mu...
25/05/2026

HOTUNA: Yadda jam'iyyar PRP ta tabbatar da Sanata Shehu Buba a matsayin dan takarar gwamnan jihar Bauchi, Shehu Aliyu Musa a matsayin dan takarar Sanatan Bauchi ta kudu, Sanata Sama'ila Dahuwa Kaila a matsayin dan takarar Sanatan Bauchi ta arewa, Salisu Zakari Ningi a matsayin dan takarar Sanatan Bauchi ta tsakiya, da sauran yan takara a kujeru dabam dabam kafin zuwan hukuncin kotu.

📸 Albarka Radio

Wata babbar Kotu A Jihar Bauchi mai lamba ta biyu ƙarƙashin Mai Shari’a Kunaza N. Hamidu ta dakatar da shirye-shiryen gu...
25/05/2026

Wata babbar Kotu A Jihar Bauchi mai lamba ta biyu ƙarƙashin Mai Shari’a Kunaza N. Hamidu ta dakatar da shirye-shiryen gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamnan Bauchi na jam’iyyar PRP.

Kotun ta bayar da umarnin ne bayan ƙarar da Idris Safiyanu Gambo ya shigar kan jam’iyyar PRP, Sanata Shehu Buba Umar da kuma hukumar zaɓe (INEC).

Rahotanni sun ce rikicin ya samo asali ne bayan yunƙurin bai wa Sanata Shehu Buba Umar takarar gwamna bayan shigowarsa jam’iyyar PRP, lamarin da ya haifar da rashin amincewa daga ɗan takarar jam’iyyar, Barrister S. G. Idris.

Kotun ta hana PRP gudanar da zaɓen fidda gwani ko wani taron zaɓe a jihar, tare da umartar INEC ta dakatar da sa ido kan tsarin har sai an yanke hukunci a shari’ar.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Laraba 27 ga Mayu da Alhamis 28 ga Mayu, 2026, a matsayin ranakun hutu domin bikin B...
25/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Laraba 27 ga Mayu da Alhamis 28 ga Mayu, 2026, a matsayin ranakun hutu domin bikin Babbar Sallah.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar ma’aikatar, Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Litinin.

Sanarwar ta bayyana cewa ayyana hutun na nuna irin girmamawa da darajar da Gwamnatin Tarayya ke bai wa addini da al’adun ibada na miliyoyin Musulman Najeriya da ke gudanar da wannan babban biki tare da al’ummar Musulmi na duniya baki ɗaya.

Me zaku ce akai ?
25/05/2026

Me zaku ce akai ?

DA DUMI DUMIMatashi ɗan siyasa daga jihar Bauchi mai suna Akibu Bauchi ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC nan take...
24/05/2026

DA DUMI DUMI

Matashi ɗan siyasa daga jihar Bauchi mai suna Akibu Bauchi ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC nan take.

A cikin wasiƙar murabus ɗin da ya fitar, Akibu Bauchi ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan dogon nazari da tunani na kashin kansa.

Ana hasashen cewa Akibu Bauchi zai koma jam’iyyar PRP mai alamar ɗan makulli ne, bayan sanar da ficewar sa daga jam’iyyar ta APC.

Sai dai har zuwa yanzu, bai fito fili ya bayyana sabuwar jam’iyyar da zai koma ba,

24/05/2026

Wane labarin kuke da shi?

Rahotonni na nuni da cewa Sanata Kachalla na shirin fita daga jam'iyar APC zuwa PRP domin yin takarar sanatan Bauchi ta ...
23/05/2026

Rahotonni na nuni da cewa Sanata Kachalla na shirin fita daga jam'iyar APC zuwa PRP domin yin takarar sanatan Bauchi ta arewa.

Wane fata zakuyi masa ?

HON. TIJJANI MUHAMMAD ALIYU YA FICE DAGA APC BAYAN ZAƁEN FIDDA GWANIHon. Tijjani Muhammad Aliyu ya sanar da ficewarsa da...
23/05/2026

HON. TIJJANI MUHAMMAD ALIYU YA FICE DAGA APC BAYAN ZAƁEN FIDDA GWANI

Hon. Tijjani Muhammad Aliyu ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC bayan kammala zaɓen fidda gwani na jam’iyyar da aka gudanar, inda ya sha kaye a takarar da ya tsaya.

Tijjani ya bayyana hakan ne ta cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya gode wa Allah SWT da kuma al’umma bisa goyon baya, addu’o’i da jajircewar da s**a nuna masa a lokacin takararsa.

Ya ce matakin barin APC ba saboda jam’iyyar ta yi masa wani laifi ba ne, sai dai saboda wasu yanayi da kuma ra’ayinsa na kare mutuncinsa da martabarsa.

Hon. Tijjani ya kuma yabawa jam’iyyar APC bisa damar da ta ba shi a baya, yana mai cewa zai ci gaba da gode mata kan irin gudunmawar da ta bayar a tafiyarsa ta siyasa.

Hakazalika, ya yi kira ga magoya bayansa da su guji zage-zage, cin mutunci ko ɗaukar wani mataki da ka iya haddasa tashin hankali ko rashin fahimta, yana mai jaddada cewa komai yana hannun Allah.

Dangane da matakin siyasa na gaba, ya bayyana cewa har yanzu bai yanke hukunci kan abin da zai yi nan gaba ba, domin ana ci gaba da nazari, tare da alƙawarin sanar da jama’a duk wata matsaya da za a ɗauka.

Address

Bauchi
6006

Telephone

+2348149010243

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ADAP TV News 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ADAP TV News 24:

Share