Mdc Studios & Craft Ltd

Mdc Studios & Craft Ltd Our concern is to satisfy your needs when it comes to accuracy in information dissemination and quality printing services.

We also have computer Gurus who make you speak in the language of virtual service delivery.

RUWAN SAMA YA HALLAKA WATA DATTIJUWA TARE DA JIKARTA, YA LALATA GIDAJE DA DUKIYOYIKirfi, Bauchi — A wani ruwan sama da a...
11/06/2026

RUWAN SAMA YA HALLAKA WATA DATTIJUWA TARE DA JIKARTA, YA LALATA GIDAJE DA DUKIYOYI

Kirfi, Bauchi — A wani ruwan sama da aka tafka kamar da bakin Ƙwarya tare da iska mai ƙarfi ya yi ajalin wata mata mai shekaru 50, Aisha Sagir, da jikarta mai shekaru huɗu, Aisha Shuaibu, a ƙauyen Bara da ke gundumar Katsinawa a Ƙaramar Hukumar Kirfi ta Jihar Bauchi.

Rahotanni sun nuna cewa haɗarin ya afku ne da safiyar ranar Laraba, 10 ga Yuni, 2026, inda ya haddasa asarar rayuka tare da lalata gidaje, dabbobi da wasu muhimman kadarori da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Jami'an 'yan sanda na Rundunar Kirfi sun kai ziyara yankin domin tantance irin barnar da aka yi tare da ɗaukar matakan tabbatar da zaman lafiya da tsaro a tsakanin al'ummar da abin ya shafa.

A cikin saƙon ta'aziyya da Rundunar 'Yan Sandan Jihar Bauchi ta fitar, Kwamishinan 'Yan Sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya jajanta wa iyalan mamatan da kuma al'ummar Ƙaramar Hukumar Kirfi bisa wannan babban rashi.

Ya yi addu'ar Allah Ya jikansu da rahama, Ya kuma bai wa iyalansu da danginsu haƙurin jure wannan ibtila'i.

Haka kuma, rundunar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da haɗa kai da hukumomin da abin ya shafa wajen tallafawa ayyukan agajin gaggawa da kare rayuka da dukiyoyin jama'a.

⚠️ A yayin da damina ke ƙara ƙamari, an buƙaci mazauna jihar su, musamman waɗanda suke zaune kusa da koguna su kasance masu lura da yanayin muhalli tare da gaggauta sanar da hukumomin da abin ya shafa idan s**a fuskanci wata barazana ko gaggawa.

🤲 Allah Ya gafarta wa mamatan, Ya karemu daga afkuwar irin wannan ibtila'i.

SOJOJI SUN KAI HARI SANSANONIN ’YAN TA'ADDA A BAUCHI, SUN KASHE DA DAMA, SUN CETO MUTANE 13Dakarun sojin Najeriya karkas...
12/04/2026

SOJOJI SUN KAI HARI SANSANONIN ’YAN TA'ADDA A BAUCHI, SUN KASHE DA DAMA, SUN CETO MUTANE 13

Dakarun sojin Najeriya karkashin Operation Enduring Peace (OPEP) sun kai farmaki kan sansanonin ’yan ta’adda a karamar hukumar Alkaleri, Jihar Bauchi, inda s**a kashe da dama tare da ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su.

An gudanar da harin ne da misalin karfe 10:30 na safe ranar 10 ga Afrilu, inda dakarun Brigade ta 33 Artillery karkashin jagorancin Birgediya Janar SS Shehu s**a kai hari sansanin Auta Kachalla da yankin Kuka tare da hadin gwiwar jami’an Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (ONSA).

Rahotanni sun ce dakarun sun yi artabu da ’yan ta’addan, inda s**a fatattake su sakamakon karfin wutar da s**a yi amfani da ita, wasu daga cikinsu kuma an kashe su yayin fafatawar.

Kayayyakin da aka kwato sun hada da bindiga kirar Dane, bindigar gida daya, na’urorin sadarwa guda biyar (Baofeng), na’urar POS, waya da kuma kwamfutar tafi-da-gidanka. Haka kuma an lalata wasu babura da ’yan ta’addan ke amfani da su.

A wani samame na gaba, dakarun rundunar soji tare da hadin gwiwar Civilian Joint Task Force (CJTF) sun gudanar da sintiri a yankin Mansur bayan harin sama da aka kai Garin Bagobiri a ranar 9 ga Afrilu.

A yayin wannan aiki, an samu nasarar ceto mutane 13 da aka sace, wadanda yanzu haka suke hannun sojoji domin tantancewa kafin a mayar da su ga iyalansu.

Wannan nasara na nuna kokarin da sojoji ke ci gaba da yi wajen murkushe ’yan ta’adda da dawo da zaman lafiya a Jihar Bauchi da ma yankunan da ke makwabtaka.

As political alliances gather momentum toward the 2027 elections, what appears on the surface as unity raises deeper, un...
12/04/2026

As political alliances gather momentum toward the 2027 elections, what appears on the surface as unity raises deeper, uncomfortable questions about responsibility, silence, and selective outrage. The same actors now speaking in one voice for power were, in many instances, fragmented—or conspicuously quiet—when the nation faced some of its gravest security and humanitarian challenges.

Where was this collective urgency when innocent civilians were repeatedly killed in Maiduguri—a region that has endured over a decade of insurgency linked to Boko Haram and its offshoots? Why was there no sustained, unified political front when mass abductions plagued communities across the North-West, especially in Zamfara State and Kaduna State, where banditry has displaced thousands and turned education into a risk?

Equally troubling is the silence that often surrounds issues of national sovereignty and transparency. When reports confirmed cooperation with foreign forces, including the United States military, within Nigerian territory for security operations, why did it not spark broader legislative debate or public accountability among those now forming coalitions?

But beyond the silence of politicians, citizens must also interrogate the performance of the present administration. Despite repeated assurances, many communities continue to face insecurity, with limited visible deterrence against recurring attacks, kidnappings, and rural banditry. Response mechanisms are often reactive rather than preventive. Intelligence failures, delayed military interventions, and inadequate protection for vulnerable communities have been recurring criticisms from civil society and local leaders.

Economic strain has compounded these concerns—rising cost of living, unemployment pressures, and limited social safety nets have deepened public frustration. In many areas, citizens feel left to rely on self-help or community vigilantes due to perceived gaps in formal security structures.

These realities raise critical questions:

1. Why do responses to insecurity remain inconsistent despite years of recurring patterns?
2. What structural reforms have truly been implemented to prevent—not just respond to—violence?
3. Why are rural and vulnerable communities still exposed despite national security spending?
4. Is political unity being driven by national interest—or electoral survival?
5. Can leaders who were silent in times of crisis convincingly promise change?

At its core, this is not just about politics—it is about trust.
A nation watches not only what leaders say during campaigns, but what they did when it mattered most.

In the end, the credibility of any political movement will not be measured by how loudly it campaigns—but by how boldly it confronted injustice, insecurity, and suffering when the stakes were highest.

Aminu Umar Madachi ✍️

DAN MAJALISAR TARAYYA DAGA KANO, BARR. MOHAMMED HASSAN, YA RASUDan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Dawakin Kudu/W...
11/04/2026

DAN MAJALISAR TARAYYA DAGA KANO, BARR. MOHAMMED HASSAN, YA RASU

Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Dawakin Kudu/Warawa a Jihar Kano, Barrister Mohammed Hassan, ya rasu yana da shekaru 62 a duniya.

Marigayin, wanda aka san shi a matsayin lauya kuma jagoran al’umma, ya rasu ne a ranar Juma’a a wani asibiti da ke Abuja bayan fama da jinya.

Shugaban masu yada labaransa, Mohammed Yaro Daba, ne ya tabbatar da rasuwar cikin wata sanarwa, inda ya ce za a gudanar da sallar jana’izarsa a gidansa da ke Abuja a ranar Asabar da karfe 2:00 na rana.

Marigayin ya shiga majalisar ne a karkashin jam’iyyar New Nigeria People Party (NNPP) a shekarar 2023, kafin daga bisani ya koma jam’iyyar African Democratic Congress.

An ce an gan shi a bainar jama’a a karo na karshe a wani taro da aka gudanar a gidan Rabiu Musa Kwankwaso a Abuja.

Ya rasu ya bar mata uku da ‘ya’ya 18.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya kuma bai wa iyalansa hakurin jure wannan rashi.

“BA ZA KU TABA ZAMA ABOKAN HADIN GWIWAR MU BA” – Isra’ila Ta Dauki Mataki Kan SpainFirayim Ministan Isra’ila, Benjamin N...
11/04/2026

“BA ZA KU TABA ZAMA ABOKAN HADIN GWIWAR MU BA” – Isra’ila Ta Dauki Mataki Kan Spain

Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya zargi ƙasar Spain da nuna ƙiyayya ga Isra’ila, bayan cire ta daga cibiyar haɗin gwiwar tsagaita wuta a Gaza.

A cikin wani saƙon bidiyo da ya fitar a ranar Juma’a, Netanyahu ya ce Isra’ila ba za ta yi shiru ba ga duk wanda ke kai mata hari, yana mai zargin Spain da s**ar sojojin Isra’ila.

Ya ce, “Ba za mu lamunci ƙasashen da ke kai mana hari ba. Duk wanda ya zaɓi s**ar Isra’ila maimakon masu ta’addanci, ba zai zama abokin hulɗarmu a nan gaba ba.”

Netanyahu ya kuma sanar da cire wakilan Spain daga cibiyar haɗin gwiwa ta soji da farar hula da ke Kiryat G*t, yana mai cewa Spain ta dade tana adawa da manufofin Isra’ila.

Wannan mataki ya biyo bayan s**ar da Firayim Ministan Spain, Pedro Sánchez, ya yi kan hare-haren Isra’ila a Lebanon, inda ya bayyana su a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, tare da zargin rashin mutunta rayuwar dan Adam da dokokin kasa da kasa.

Sánchez ya kuma bukaci Tarayyar Turai ta dakatar da yarjejeniyar hulɗa da Isra’ila, lamarin da ke kara tsananta takaddama tsakanin kasashen biyu.

👉 Ku biyo mu domin samun sabbin labaran duniya.

SARKIN YELWAN TUDU YA NADA SABBIN MASU SARAUTA 25Mai Girma Sarkin Yelwan Tudu, Malam Adamu Zubairu Umar, ya gudanar da b...
06/04/2026

SARKIN YELWAN TUDU YA NADA SABBIN MASU SARAUTA 25

Mai Girma Sarkin Yelwan Tudu, Malam Adamu Zubairu Umar, ya gudanar da bikin nadin sarauta ga mutane 25 a ranar 4 ga Afrilu, 2026.

Daga cikin wadanda aka nada akwai Mal. Yakubu Sa’idu a matsayin Sarkin Malaman Yelwan Tudu, Mal. Yahaya Jibrin Kawure a matsayin Tafidan Yelwan Tudu, da kuma Mal. Abubakar I. Jalingo a matsayin Sakin Yamman Yelwan Tudu.

Sauran sun hada da Kamalu Mohammed Hussaini (Wambai), Haruna Ibrahim Ladan (Maidawa), Mal. Shehu Usman Balteh (Mai Unguwan Tsakiya), Usman Abdullahi (Waziri), Jafaru T. Dutse (Dan-Masani), da Yahuza Ja’afar (Shamaki).

Haka kuma an nada Mr Reuben Edward Ishaku (Mai-Tangale), Shehu Muhammad Danladi (Sa’i), Alh. Muhammad Bashir Sulaiman (Mai-Dala), Aliyu Hamidu (Maga-Yaki), da Alh. Auwalu Ahmad Indabo (Turaki).

Sauran sun hada da Mannir I. Umar (Maji-Dadi), Yakubu Adamu (Madugu), Usman Ibrahim (Sarkin Fulani), Auwalu Hassan (Sarkin Fawa), Kabiru Hassan (Sarkin Bindiga), Sharif Isah (Chigari), Yusuf Usman (Dallatu), Bashir Yusuf (Wali), Ibrahim Dalhatu (Dan-Galadima), Abubakar Barde (Mai Unguwar Yamman), da Zainab Muhammad Magaji (Wakiliyar Ilimi).

Sarkin ya taya su murna tare da bukatar su yi aiki da gaskiya, rikon amana da hidima ga al’umma domin ci gaban Yelwan Tudu.

26/02/2026

Sakon Barka Da Shan Ruwa Daga MDC Studios, Rana Ta Tara (9) Cikin Watan Ramadan 1447 AH/2026

25/02/2026

Sakon Barka Da Shan Ruwa Daga MDC Studios, Rana Ta Takwas (8) Cikin Watan Ramadan 1447 AH/2026

A'ISHA BALA MUHAMMED TA BUKACI MATA SU RUNGUMI SANA'O'IN GIDA.Bauchi, 25 Fabrairu, 2026 — Hajiya Aisha Bala Mohammed, ma...
25/02/2026

A'ISHA BALA MUHAMMED TA BUKACI MATA SU RUNGUMI SANA'O'IN GIDA.

Bauchi, 25 Fabrairu, 2026 — Hajiya Aisha Bala Mohammed, matar Gwamnan Jihar Bauchi, ta yi kira ga mata da su rungumi ƙananan kasuwanci na gida domin inganta rayuwarsu da na iyalansu.

A yayin wata muhimmiyar hira da aka yi a Bauchi, Hajiya Aisha ta bayyana cewa sana’o’in gida kamar dinki, sayar da kayan miya, tukwane, gyaran gashi, noman kayan lambu da sauransu na iya taimakawa mata su samu ɗorewar samun kuɗi ba tare da dogaro da wani ba.

Ta ce ƙoƙarin fara kananan harkokin kasuwanci a gida zai bai wa mata damar tallafawa iyalansu, inganta ilimin yara, biyan kuɗin makaranta da kuma rage matsalolin talauci. Hajiya Aisha ta yi nuni da cewa mata da yawa na da baiwa da ƙwarewa da za su iya amfani da su wajen ƙirƙirar sana’o’i masu riba.

Matar gwamna ta kuma shawarci mata su nemi tallafi da shawarwari daga kungiyoyi da cibiyoyin da ke horas da kananan ‘yan kasuwa don su bunkasa sana’o’insu tare da fadada kasuwancin su.

Hajiya Aisha ta ce wannan kira nata na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke ƙara mayar da hankali kan bunkasa tattalin arzikin mata da matasa, tare da tabbatar da cewa kowane bangare na al’umma na samun dama ta ilimi da samun sana’a.

Ku biyo shafinmu domin karin labarai akan shirin bunkasa rayuwar mata da matasa a Bauchi.

Address

1 POWA Shopping Complex, Ahmadu Bello Way
Bauchi
740212

Opening Hours

Monday 08:00 - 21:00
Tuesday 08:00 - 21:00
Wednesday 08:00 - 21:00
Thursday 08:00 - 21:00
Friday 08:00 - 21:00
Saturday 08:00 - 21:00
Sunday 08:00 - 21:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mdc Studios & Craft Ltd posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share