11/06/2026
RUWAN SAMA YA HALLAKA WATA DATTIJUWA TARE DA JIKARTA, YA LALATA GIDAJE DA DUKIYOYI
Kirfi, Bauchi — A wani ruwan sama da aka tafka kamar da bakin Ƙwarya tare da iska mai ƙarfi ya yi ajalin wata mata mai shekaru 50, Aisha Sagir, da jikarta mai shekaru huɗu, Aisha Shuaibu, a ƙauyen Bara da ke gundumar Katsinawa a Ƙaramar Hukumar Kirfi ta Jihar Bauchi.
Rahotanni sun nuna cewa haɗarin ya afku ne da safiyar ranar Laraba, 10 ga Yuni, 2026, inda ya haddasa asarar rayuka tare da lalata gidaje, dabbobi da wasu muhimman kadarori da darajarsu ta kai miliyoyin naira.
Jami'an 'yan sanda na Rundunar Kirfi sun kai ziyara yankin domin tantance irin barnar da aka yi tare da ɗaukar matakan tabbatar da zaman lafiya da tsaro a tsakanin al'ummar da abin ya shafa.
A cikin saƙon ta'aziyya da Rundunar 'Yan Sandan Jihar Bauchi ta fitar, Kwamishinan 'Yan Sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya jajanta wa iyalan mamatan da kuma al'ummar Ƙaramar Hukumar Kirfi bisa wannan babban rashi.
Ya yi addu'ar Allah Ya jikansu da rahama, Ya kuma bai wa iyalansu da danginsu haƙurin jure wannan ibtila'i.
Haka kuma, rundunar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da haɗa kai da hukumomin da abin ya shafa wajen tallafawa ayyukan agajin gaggawa da kare rayuka da dukiyoyin jama'a.
⚠️ A yayin da damina ke ƙara ƙamari, an buƙaci mazauna jihar su, musamman waɗanda suke zaune kusa da koguna su kasance masu lura da yanayin muhalli tare da gaggauta sanar da hukumomin da abin ya shafa idan s**a fuskanci wata barazana ko gaggawa.
🤲 Allah Ya gafarta wa mamatan, Ya karemu daga afkuwar irin wannan ibtila'i.