Zamani TV

Zamani TV Zamani TV kamfani ne dake kawo sahihan labaran da suke faruwa a Najeriya harma da ƙasashen ƙetare.
(1)

28/07/2025

Shirin Tsangayar Kura Tare da Hon. Yahuza Abdullahi

28/07/2025

Muslim Isah Yuguda ya fi karfin cin mutunci, musamman idan aka duba irin ayyukan alheri da mahaifinsa, Dr. Malam Isah Yuguda ya yi wa Al'umma

28/07/2025

Ba a taɓa samun Sanatan Bauchi ta Kudu da ya yi ayyuka masu amfani da nagarta kamar Sanata Shehu Buba Umar ba

Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, Ya Yi Hasashen Komawar Peter Obi Zuwa Jam’iyyar PDPTsohon gwamnan j...
28/07/2025

Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, Ya Yi Hasashen Komawar Peter Obi Zuwa Jam’iyyar PDP

Tsohon gwamnan jihar Borno kuma jigo a siyasar Najeriya, Sanata Ali Modu Sheriff, ya bayyana cewa akwai alamun cewa tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Mista Peter Obi, na dab da komawa jam’iyyar PDP domin sake yin takara a zaben shugaban kasa na 2027.

Sanata Sheriff ya ce, “Bisa bayanan da ke gabana, duk da cewa ba zan fadi komai a hukumance ba, akwai yiwuwar Peter Obi zai dawo jam’iyyar PDP a kowane lokaci daga yanzu, kuma zai tsaya takarar shugaban kasa a ƙarƙashin tutar PDP.”

Wannan furuci na zuwa a daidai lokacin da ake ci gaba da rade-radin sauyin matsayi daga wasu fitattun ’yan siyasa a Najeriya, musamman yayin da shirye-shiryen zaben 2027 ke kara daukar zafi.

Peter Obi, wanda ya taba kasancewa mataimakin dan takarar shugaban kasa a PDP kafin ya fice daga jam’iyyar a shekarar 2022 domin tsayawa takara a karkashin Labour Party, bai kai ga yin wani karin bayani kan maganar ba a hukumance. Sai dai maganganun Sanata Sheriff na iya janyo ce-ce-ku-ce.

-Zamani TV

28/07/2025

Cikakken Shirin Tsangayar Kura tare da Hon. Yusuf Ahmad

TIRƘASHI: Yadda Gwamnan Jihar Benue Ya Rabawa Matan Jihar Tallafin Baro [Wheel-Barrow] Domin Su Dogara Da Kansu
28/07/2025

TIRƘASHI: Yadda Gwamnan Jihar Benue Ya Rabawa Matan Jihar Tallafin Baro [Wheel-Barrow] Domin Su Dogara Da Kansu

Tinubu Bai Yi Kuskure Ba Idan Ya Sake Haɗa Kai Da Kwankwaso, Cewar Hadimim Tinubu Mallam Abdulaziz AbdulazizHadimi na mu...
28/07/2025

Tinubu Bai Yi Kuskure Ba Idan Ya Sake Haɗa Kai Da Kwankwaso, Cewar Hadimim Tinubu Mallam Abdulaziz Abdulaziz

Hadimi na musamman ga shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu kan harkokin sadarwa, Mallam Abdulaziz Abdulaziz, ya bayyana cewa tun tale-tale akwai alaƙa tsakanin Tinubu da Kwankwaso a matsayinsu na tsofin sanatoci, kuma tsofin gwamnoni, dan haka, Tinubu bai aikata wani laifi ba dan ya sake haɗa kai da Kwankwaso a wannan lokaci.

"Magana tsakanin ƴan siyasa ba laifi ba ne, dan haka idan fadar shugaban ƙasa ko abokan shugaban ƙasa sun yi magana da Kwankwaso babu wani laifi ko aibu kan hakan. Baya da haka, siyasa ce, mutane suna haɗuwa, suna kuma sake haɗuwa su daidaita ra'ayi ko matsayinsu a siyasance". Ya ce.

A cewar Malam Abdulaziz ta cikin zantawarsa da manema labarai, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito a yau, "Da Tinubu da Kwankwaso sun zauna a majalissa a matsayin zaɓaɓɓun ƴan majalissar tarayya a 1993. Sannan kuma, an zaɓe su a matsayin gwamnoni a 1999, dan haka, suna da alaƙa daɗaɗɗiya irin ta siyasa wanda ba abun mamaki ba ne dan sun ƙara haɗewa waje guda". In ji shi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Tinubu ya ba ‘yan wasan Super Falcons da ma’aikatan horarwa lambar girmamawa ta ƙasa ta OON.Tinubu ya kuma...
28/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Tinubu ya ba ‘yan wasan Super Falcons da ma’aikatan horarwa lambar girmamawa ta ƙasa ta OON.

Tinubu ya kuma ware musu gidaje mai ɗakuna uku-uku a Renewed Hope Estate, tare da ba kowacce ‘yar wasa $100,000, kimanin miliyan 150, sannan ya ba masu horaswa $50,000, kimanin miliyan 75.

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, Ya Kai Ziyarar Taya Murna Ga Nentawe Yilwatda Kan Nadin Shugaban APC na Ka...
28/07/2025

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Maitama Tuggar, Ya Kai Ziyarar Taya Murna Ga Nentawe Yilwatda Kan Nadin Shugaban APC na Kasa

A yau Litinin, Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, OON, ya kai ziyarar taya murna ga abokinsa na dogon lokaci, Nentawe Goshwe Yilwatda, sakamakon nadinsa a matsayin sabon shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa.

Tuggar ya nuna kyakkyawan fata cewa jagorancin Nentawe zai kawo sabbin dabaru da hadin kai cikin jam’iyyar APC, tare da inganta tafiyar dimokuradiyya a Najeriya baki daya.

-Zamani TV

28/07/2025

Duk jihar Bauchi babu Sanata kaman Shehu Buba Umar- Yusuf Dan Hutu.

Hukumar EFCC Ta Cafke Matasa 32 da Ake Zargi da Zamba ta Intanet a BauchiJami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta...
28/07/2025

Hukumar EFCC Ta Cafke Matasa 32 da Ake Zargi da Zamba ta Intanet a Bauchi

Jami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC), reshen shiyyar Gombe, sun cafke matasa 32 da ake zargi da aikata zamba ta kafar intanet a unguwannin Sabon Kaura da Gwalameji da ke cikin birnin Bauchi, babban birnin Jihar Bauchi.

Wannan samame da aka gudanar a ranar Juma’a, 25 ga Yuli, 2025, ya biyo bayan sahihan bayanan sirri da hukumar ta samu, waɗanda s**a danganta waɗanda ake zargin da aikata ayyukan damfara ta yanar gizo da s**a haɗa da satan bayanan mutane da kuma zambatar su ta hanyoyi daban-daban.

EFCC ta bayyana cewa daga cikin kayan da aka gano a wajen wadanda ake zargin akwai: wayoyin salula guda 28 da s**a haɗa da iPhone 15, Samsung 9, Infinix 1, Redmi 3; kwamfutocin tafi-da-gidanka guda 8; na'urorin iPad guda 2; babura Neonx Auto guda 4; motar Peugeot 406 guda 1; kayan nishaɗi na PlayStation 4 guda 2 da PlayStation 5 guda 1; janareta nau'in Maxi E50KWH guda 1; da kuma bindiga guda ɗaya.

EFCC ta ce bincike na ci gaba, kuma za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala binciken.

Hukumar ta kuma ja hankalin matasa da su guji fadawa tarkon ayyukan da s**a sabawa doka, tana mai cewa za ta ci gaba da farautar masu aikata irin waɗannan laifuka domin kare lafiyar tattalin arzikin ƙasa da martabar al’umma.

-Zamani TV

Don Allah Ina Rokon Mutanen Da Suke Kashe Ni A Social Media Su Yi Hakuri Su Daina Kashe Ni Haka, Domin An Kashe Ni Ya Fi...
28/07/2025

Don Allah Ina Rokon Mutanen Da Suke Kashe Ni A Social Media Su Yi Hakuri Su Daina Kashe Ni Haka, Domin An Kashe Ni Ya Fi Sau Goma, A Bari Har Sai Mutuwa Ta Gaske Ta Zo Min.

Rokon Jarumin Kannywood Rabiu Rikadawa (Baba Dan Audu)

Address

Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani TV:

Share