03/06/2026
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron shari’ar da Nafiu Bala Gombe ya shigar kan shugabancin jam’iyyar ADC ƙarƙashin Sanata David Mark zuwa ranar 8 ga Yuni, 2026.
Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa Mai Shari’a Peter Lifu ne ya ɗage shari’ar bayan lauyan Gombe, Robert Emukpoeruo (SAN), ya nemi ƙarin lokaci saboda rashin halartar lauyoyin wasu ɓangarorin da ke neman a haɗa su cikin shari’ar.
Yayin zaman kotun, lauyan ADC, Shaibu Aruwa (SAN), ya tunatar da kotun cewa tsohon mai sauraron ƙarar, Mai Shari’a Emeka Nwite, ya riga ya yi la’akari da waɗannan ɓangarorin a zaman da ya gabata. Ya roƙi kotun ta ba su damar bayyana dalilin da ya sa suke son shiga cikin shari’ar domin tabbatar da adalci ga kowa.
Sai dai lauyan mai ƙarar ya bayyana cewa Kotun Ƙoli ta umarci a gaggauta sauraron shari’ar, don haka ya nemi a ba dukkan ɓangarorin damar kammala shigar da takardunsu kafin a ci gaba da sauraron ƙarar. Lauyoyin ADC bangaren Sanata David Mark da Rauf Aregbesola da Ralph Nwosu ba su yi adawa da buƙatar ɗage sauraron ba.
Mai Shari’a Lifu ya bayyana cewa babu wanda ke da ikon zaɓar alkalin da zai saurari shari’arsa. Ya ce bisa umarnin Babban Alƙalin Kotun Tarayya da kuma hukuncin Kotun Ƙoli na gaggauta sauraron ƙarar, kotun za ta tabbatar da adalci ga kowane ɓangare.
Kotun ta kuma ɗora wa kanta alhakin rashin isar da sammaci ga waɗanda ke neman shiga cikin shari’ar, tare da umartar jami’in kotu ya kai musu takardun cikin sa’o’i 24. Haka kuma ta umurci dukkan ɓangarorin da su kammala shigar da takardunsu kafin ranar da za a sake zama.
A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1819/2025, Nafiu Bala Gombe, tsohon Mataimakin Shugaban ADC na Ƙasa, na neman kotu ta hana Sanata David Mark da Rauf Aregbesola da sauran shugabannin riƙo na jam’iyyar ci gaba da bayyana kansu a matsayin shugabannin ADC. Ya yi zargin cewa naɗinsu ya saɓa wa kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma Dokar Zaɓe.
Rikicin shugabancin ADC na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar ke shirin tunkarar zaɓen 2027, inda tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya samu tikitin takarar shugaban ƙasa daga wani ɓangaren jam’iyyar, yayin da wani ɓangaren kuma ya amince da Dumebi Kachikwu a matsayin ɗan takararsa.