04/08/2026
Gwamnatin Jihar Bauchi ta ayyana bullar cutar kwalara a hukumance bayan da aka samu ƙaruwar masu fama da gudawa mai tsanani (Acute Watery Diarrhoea) tare da tabbatar da kamuwar wasu da cutar ta hanyar gwaje-gwajen dakin bincike.
Sanarwar, wadda Ma'aikatar Lafiya da Walwalar Jama'a ta Jihar Bauchi ta fitar a ranar 1 ga Agustan 2026, ta ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar Kwamitin Masana Kula da Yaɗuwar Cututtuka na jihar da kuma Cibiyar Gudanar da Ayyukan Gaggawa kan Lafiyar Jama'a.
Ma'aikatar ta bayyana cewa ayyana barkewar cutar ya yi daidai da ƙa'idojin Hukumar Lafiya ta Duniya na Kasa da Kasa (International Health Regulations 2005), Jagororin Ƙasa kan Shirin Kariya da Yaki da Kwalara, da kuma tsarin gudanar da matsalolin gaggawa na Ma'aikatar Lafiya ta Tarayya.
A cewar ma'aikatar, zuwa ranar 31 ga Yulin 2026, an samu mutum 398 da ake zargin sun kamu da cutar, yayin da aka samu rahotannin bullar cutar a ƙananan hukumomi 13 na jihar.
Haka kuma, mutane 16 sun rasa rayukansu sakamakon cutar, adadin da ya kai kaso huɗu cikin ɗari na waɗanda aka samu rahoton kamuwarsu.
Ƙananan hukumomin da cutar ta fi shafa sun haɗa da Toro, inda aka samu mutum 231 da ake zargi sun kamu, sai Alkaleri da Kirfi mai mutum 46 kowacce, Ganjuwa mai mutum 21, sannan Bauchi da Tafawa Balewa, inda aka samu mutum 14 a kowacce.
Ma'aikatar Lafiya ta yi kira ga abokan hulɗa a fannin ci gaba, ƙungiyoyin bayar da tallafi da kuma al'umma da su ba gwamnati haɗin kai wajen dakile yaɗuwar cutar.
Haka kuma ta buƙaci jama'a su kula da tsaftar muhalli da ta jiki, su riƙa shan ruwa mai tsafta, tare da garzayawa cibiyoyin lafiya idan s**a fara fama da gudawa mai tsanani ko amai, domin samun kulawar gaggawa.