Zamani TV

Zamani TV Zamani TV kamfani ne dake kawo sahihan labaran da suke faruwa a Najeriya harma da ƙasashen ƙetare.

Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Hadu da Ɗalibin da Ya Taimaka a Karatun Waje Wanda Yanzu Matukin Ji...
19/10/2025

Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Hadu da Ɗalibin da Ya Taimaka a Karatun Waje Wanda Yanzu Matukin Jirgin Sama

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya sadu da ɗaya daga cikin matasan da ya tallafa musu wajen yin karatu a ƙasashen waje, wanda a halin yanzu ya zama ɗaya daga cikin matukan jirgin sama na kamfanin Umza Express Airline.

Matashin, mai suna Malam Ibrahim, ya kasance ɗaya daga cikin dubban ɗaliban da Kwankwaso ya dauki nauyin karatunsu a lokacin yana gwamna, karkashin shirin tallafin karatu na jihar Kano.

A yayin ganawarsu, Malam Ibrahim ya bayyana farin cikinsa da ganin madugun da ya ba shi damar samun ilimi da kuma cimma irin wannan matsayi a rayuwa.

-Zamani TV

ELKANEMI WARRIORS TA DOKE WIKKI TOURISTS DA CI 2–1 A MAIDUGURIKungiyar Elkanemi Warriors ta samu nasara a gida bayan ta ...
19/10/2025

ELKANEMI WARRIORS TA DOKE WIKKI TOURISTS DA CI 2–1 A MAIDUGURI

Kungiyar Elkanemi Warriors ta samu nasara a gida bayan ta doke Wikki Tourists ta Bauchi da ci 2–1 a wasan NPFL26 Matchday 9 da aka buga a filin wasa na Elkanemi da ke Maiduguri.

Wasan ya kasance mai cike da zafi da gogayya, inda Wikki Tourists ta fi rinjaye a ɓangaren mallakar kwallo, amma ta kasa amfani da damar da ta samu bayan tafaɗa cikin rashin sa’a a farkon wasa.

Elkanemi ta zura kwallon farko ne a minti na 9 ta hannun Emmanuel Jonas, wanda ya ci daga cikin akwatin Wikki bayan rikice-rikicen da ya biyo bayan bugun kusurwa. Sai kuma a minti na 36, Samaila Bello ya kara na biyu ga masu masaukin baki bayan wata gaggawar kai hari da ta rikita tsaron Wikki.

Da yake ƙoƙarin dawo da martaba, Wikki Tourists ta samu nasarar rage tazarar cin a minti na 45 ta hannun Abdullahi Usman (Pepe), wanda ya ci daga kyakkyawan taimako da Jonathan Mairiga ya bayar kafin a tafi hutun rabin lokaci.

A zagaye na biyu, Wikki Tourists ta mamaye fili sosai, tana taka kwallo da natsuwa da kwarewa, amma duk da hakan, kwallon da za ta kawo daidaito ta ki shiga. Tsaron Elkanemi Warriors ya tsaya daram har zuwa minti na ƙarshe, inda s**a kare da nasarar gida.

Da yake bayyana ra’ayinsa bayan kammala wasa, Koci Abdu Maikaba na Wikki Tourists ya ce yana takaicin sakamakon, duk da cewa ‘yan wasansa sun nuna jajircewa da kwazo.

Ya kuma yabawa ingancin alkalancin wasannin bana na NPFL, yana mai cewa hukumar ta nuna gaggawa wajen gyara kura-kurai a wasu wasanni da s**a gabata.

Shi ma kapitan kungiyar, Mohammed Guda, ya ce rashin sa’a ce ta hana su tashi da maki daga Maiduguri, amma yana da kwarin gwiwar cewa ƙungiyar za ta dawo da kuzari a wasannin gaba.

Da wannan sakamako, Wikki Tourists za ta mayar da hankali kan wasan Matchday 10, inda za ta karɓi Shooting Stars (3SC) daga Ibadan a Bauchi wasa mai matuƙar muhimmanci domin neman dawowa kan turbar nasara a gaban masoyan ta.

-Zamani TV

19/10/2025

Danjuma Hassan Bununu ya mayar da martani ga wasu mutane da ke s**ar Dr. Bala Wunti.

19/10/2025

Ismail Saidu ya bayyana cewa maganar da ya yi kwanakin baya ba da nufin cin mutunci ba ce.

19/10/2025

Hon. Abbas Faggo Ya Yi Kira Ga Masu Sukar Dr. Bala Wunti Su Yi Haƙuri

Hon. Abbas Faggo ya yi kira ga mutanen da ke s**ar Dr. Bala Wunti da su dakata da irin wannan magana, yana mai cewa yanzu ba lokacin siyasa ba ne.

19/10/2025

Sponsored

Sanarwa daga Kungiyar Prof Muhammad Ali Pate Consultative Forum.

Barau FC Ta Yi Nasara Akan Kano Pillars Da Ci 2-1 A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya
19/10/2025

Barau FC Ta Yi Nasara Akan Kano Pillars Da Ci 2-1 A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

‎Al'umma da dama sun cancaki matakin daukar diyya da hukumar sojojin sama s**a dauka kan mutuwar wasu a karamar hukumar ...
19/10/2025

‎Al'umma da dama sun cancaki matakin daukar diyya da hukumar sojojin sama s**a dauka kan mutuwar wasu a karamar hukumar yunusari a jahar yobe

‎A cewarsu Ganin Inda akan dauki Ran dan Adam Baida Daraja Ba Kamar Kasarmu Najeriya

‎Anbawa iyalan bayin Allah guda 8 da sojojin sama s**a kashe a bisa kuskure a karamar hukumar Yunusari, jihar Yobe da basu Naira Miliyan daya-daya (N1m) ko nameye? sai Allah

‎Sun soki matakin da aka dauka inda suke tabbayar abin da me ake nufin gani a cewarsu? Yanzu wannan shine a zaman diyya na jininsu abunda a musulunci kudin diyyar kowanne daga cikinsu yakai sama da Naira Miliyan Dari Biyu da Hamsin da Biyar (N255m).

‎Daga bisani sun bayyana cewa Ko rakumika aka kashe ay zaka bada Naira Miliyan Daya.

‎daga karshe sun rufe da cewa Allah yakawo mana shuwagabanni nagari.

‎Daga Hussaini Tijjani Jallaba Wakilin ZAMANI TV Daga Jahar Yobe

Kungiyar Kwallon Kafa Na Mancheter United Ta Tabuka Abin Kirki A Yau Inda Ta Lallasa Liverpool  2-1 A Gasar Firimiya.
19/10/2025

Kungiyar Kwallon Kafa Na Mancheter United Ta Tabuka Abin Kirki A Yau Inda Ta Lallasa Liverpool 2-1 A Gasar Firimiya.

19/10/2025

Shirin Tsangayar Kura Tare da Abubakar Adamu.

19/10/2025

Mun duba mun tantance, babu wanda ya fi cancanta da kujerar Sanatan Bauchi ta Kudu sai Shamsuddeen Bala Muhammad — in ji Hon. Yahuza Abdullahi.

Cikekken Shirin Yana Tafe.

19/10/2025

Mawaki Yahaya Usman (CR7) ya bayyana yadda Dr. Bala Wunti ya tallafa masa a rayuwarsa.

Cikakken shirin yana tafe.

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani TV:

Share