Zamani TV

Zamani TV Zamani TV kamfani ne dake kawo sahihan labaran da suke faruwa a Najeriya harma da ƙasashen ƙetare.
(1)

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’ar European-American ta karyata bayar da PhD ga Dauda Kahutu Rarara, ta ce za ta dauki mataki kan mas...
20/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’ar European-American ta karyata bayar da PhD ga Dauda Kahutu Rarara, ta ce za ta dauki mataki kan masu bada takardun bogi

Jami’ar European-American University ta fito fili ta bayyana cewa labarin da ya yadu cewa ta baiwa fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara, digirin girmamawa na PhD, ƙarya ne kuma ba shi da tushe.

A cikin sanarwar da jami’ar ta fitar, ta bayyana cewa rahoton da ake yadawa cewa tana aiki a ƙasashen Dominica da Panama ba gaskiya ba ne, domin wannan ya danganci tsoffin lasisi da s**a ƙare tun da dadewa. A halin yanzu jami’ar na aiki a matsayin jami’ar masu zaman kansu mai zaman nonprofit a Faransa, tare da samun Royal Charter of Incorporation daga Masarautar Bunyoro-Kitara a ƙasar Uganda.

Haka kuma, jami’ar ta sanar da cewa za ta tuntuɓi hukumomin shari’a a Najeriya domin dakile masu amfani da sunanta wajen bayar da takardun bogi, tare da tabbatar da cewa za a hukunta su bisa doka.

Wannan batu ya jawo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda jama’a ke nuna damuwa kan yadda ake taɓarɓarewa wajen ƙirƙirar digiri da lambobin yabo na bogi a Najeriya.

Ban bada sisin Kobo ba saboda a bani wannan digirin girmamawa. - Dakta Dauda Rarara
20/09/2025

Ban bada sisin Kobo ba saboda a bani wannan digirin girmamawa. - Dakta Dauda Rarara

Shettima zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron Majalisar Dinkin Duniya a New YorkMataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Sh...
20/09/2025

Shettima zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron Majalisar Dinkin Duniya a New York

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 da za a gudanar a birnin New York, da ke Amurka, daga ranar Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28 ga watan.

Wannan na zuwa ne bisa umarnin Shugaba Bola Tinubu, kamar yadda mai taimaka masa na musamman kan yaɗa labarai, Stanley Nkwocha, ya bayyana a wata sanarwa a Abuja.

A cewar sanarwar, Shettima zai halarci taron murnar cika shekara 80 da kafuwar Majalisar Ɗinkin Duniya a ranar Litinin 22 ga Satumba, sannan daga ranar Talata 23 zuwa Lahadi 28 zai shiga tattaunawar manyan shugabanni a zauren babban taro.

Haka kuma, a ranar Laraba 24 ga Satumba ne zai gabatar da jawabin ƙasa na Najeriya tsakanin ƙarfe 3 zuwa 9 na dare agogon New York.

Bugu da ƙari, Shettima zai shiga taro na musamman kan sauyin yanayi da Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya zai jagoranta a ranar 24 ga Satumba, inda Najeriya za ta sanar da sabbin manufofin ta bisa yarjejeniyar Paris.

Haka kuma zai halarci taron manyan shugabanni kan samar da gidaje masu araha da shugaban Kenya zai shirya.

Bayan kammala taron Majalisar, Shettima zai zarce Frankfurt a ƙasar Jamus domin ganawa da jami’an Deutche Bank kafin ya dawo gida Najeriya.

20/09/2025

Shirin Tsangayar Kura tare da Bello Ambo Santurakin Zungur, Chairman Political Balancing Bauchi

20/09/2025

Shiri na musamman tare da Haj. Maimuna Ahmad

YANZU-YANZU: An Sake Yin Zaman Sulhu Ď@ Ý@n B|nd|g@ A Kananan Hukumomin Sabuwa, Dandume Da Faskari Dake Jihar Katsina A ...
20/09/2025

YANZU-YANZU: An Sake Yin Zaman Sulhu Ď@ Ý@n B|nd|g@ A Kananan Hukumomin Sabuwa, Dandume Da Faskari Dake Jihar Katsina A Yau Asabar

HOTUNA

20/09/2025

Shirin Tsangayar Kura tare da Alh. Yahaya Wakili

Dan Arewa Daga Jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam Ya Zama Na Uku A Gasar Fasaha Mafi Girma A AfirkaGasar Digital for All...
20/09/2025

Dan Arewa Daga Jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam Ya Zama Na Uku A Gasar Fasaha Mafi Girma A Afirka

Gasar Digital for All Challenge, wacce ita ce gasar koyon fasaha mafi girma a Afirka, an shirya ta ne ta hannun Tech4Dev tare da haɗin gwiwar Foreign, Commonwealth & Development Office (FCDO), NITDA da kuma UK-international development Tech Hub. Gasar ta sake samun wani babban ci gaba inda Ismail Muhammad Adam, wanda ya wakilci yankin Arewa maso Yamma, ya fito a matsayin na uku (2nd Runner-Up) a rukuni na matasa (Youth Intermediate Category).

Rukunin, wanda shi ne mafi girma daga cikin rukunan gasar, an tsara shi ne domin gwada ƙwarewar mahalarta a fannin fasaha da kuma yadda za su iya amfani da ita a aikace.

A matsayin ladan nasarar da ya samu, Ismail Muhammad Adam ya karɓi kudin ₦10,000,000 tare da samun takardar shaidar ƙwararren mai haɓaka manhajar kwamfuta (Certified Software Developer), wanda ke nuna babban ci gaba a rayuwar aikinsa.

Yayin da yake wakiltar Jihar Jigawa, shi ne kaɗai ɗan takara da jami’an gwamnatin jiha s**a raka, abin da ya ƙara tabbatar da jajircewar Gwamnatin Jihar Jigawa wajen bunƙasa ilimin fasaha da ƙarfafa matasa. Sabon Daraktan Hukumar ICT da Tattalin Arzikin Dijital ta Jihar Jigawa ya bayar da muhimmin tallafi ta hanyar kasancewa tare da shi har zuwa ƙarshen gasar.

Kungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Sa’adu Zungur (SAZU Alumni) Ta Shirya Halartar Taron ANUA a BauchiKungiyar Tsoffin Ɗali...
20/09/2025

Kungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Sa’adu Zungur (SAZU Alumni) Ta Shirya Halartar Taron ANUA a Bauchi

Kungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’o’in Najeriya (ANUA) ta sanar da shirinta na gudanar da babban taronta na musamman a Bauchi daga 1 ga Oktoba zuwa 5 ga Oktoba, 2025. Taron zai gudana a Jami’ar Sa’adu Zungur Bauchi, karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Abdulkadir.

Kungiyar Tsoffin Ɗaliban Jami’ar Sa’adu Zungur (SAZU Alumni) ta tabbatar da halartar ta, inda za a kaddamar da taron a hukumance a ranar Asabar, 4 ga Oktoba, 2025, a cibiyar Yuli Campus.

Taron na bana zai gudana karkashin taken “Bridging the Gap: Alumni-Driven Solutions for Sustainable University Funding” Wannan zai kasance dandalin tattaunawa da haɗin kai don samar da hanyoyin da za su inganta ci gaban ilimi a Najeriya.

Sanarwa:
Hafeez Hassan Jibrin
Jami’in Ƙwamitin Hulɗa da Jama’a,
SAZU Alumni Association

20/09/2025

Shirin Tsangayar Kura Tare da Ibrahim Inuwa Wunti

20/09/2025

Al’ummar garin Guru sun koka da rashin asibiti da hanya a yankinsu, inda s**a yi kira ga Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Muhammad, da Sanatan Bauchi ta Kudu, Sanata Shehu Buba Umar, tare da sauran ’yan takarar siyasa, da su zo su taimaka musu.

20/09/2025

Cikakken Shirin Tsangayar Kura tare da Mallam Dan Mallam.

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani TV:

Share