Zamani TV

Zamani TV Zamani TV kamfani ne dake kawo sahihan labaran da suke faruwa a Najeriya harma da ƙasashen ƙetare. 09069687012

Ana gayyatar ɗaukacin al'umma zuwa wajen ɗaurin auren Mujaheed Shuaibu Karia da Amaryarsa In Sha Allahu Ummusalma Abubak...
03/06/2026

Ana gayyatar ɗaukacin al'umma zuwa wajen ɗaurin auren Mujaheed Shuaibu Karia da Amaryarsa In Sha Allahu Ummusalma Abubakar Sadik.

Za a ɗaura wannan aure mai cike da tarihi ne a ranar Asabar 06 ga watan Yunin shekarar 2026 da ƙarfe 11 na safe a masallacin Imam Mahmud da ke kan titin Kobi kusa da kotun ɗaukaka ƙara ta addinin Musulunci dake Jihar Bauchi.

Allah ya ba da ikon halarta, Allah ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyiba.

03/06/2026

Tsohon ɗan takarar kujerar Sanatan Bauchi ta Kudu, Hon. Abubakar Sulaiman Maikano Gori MNI (Rtd), ya yi magana kan zaɓen fidda gwani da jam’iyyar APC ta gudanar.

03/06/2026

Daure David ya ja hankalin ’yan takarar jam’iyyar APM, jam’iyya mai alamar rogo dangane da zaɓen shekarar 2027.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanar da fara bincike kan zargin samun kutse ko shiga rumbun ajiyar bayan...
03/06/2026

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta sanar da fara bincike kan zargin samun kutse ko shiga rumbun ajiyar bayananta ba bisa ƙa’ida ba.

Ana fargabar cewa bayanan masu zaɓe sama da miliyan 90 da ke cikin kundin rajistar INEC na iya kasancewa cikin haɗari idan har wannan zargi ya tabbata.

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron shari’ar da Nafiu Bala Gombe ya shigar kan shugabancin jam’iyyar ADC ƙ...
03/06/2026

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron shari’ar da Nafiu Bala Gombe ya shigar kan shugabancin jam’iyyar ADC ƙarƙashin Sanata David Mark zuwa ranar 8 ga Yuni, 2026.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa Mai Shari’a Peter Lifu ne ya ɗage shari’ar bayan lauyan Gombe, Robert Emukpoeruo (SAN), ya nemi ƙarin lokaci saboda rashin halartar lauyoyin wasu ɓangarorin da ke neman a haɗa su cikin shari’ar.

Yayin zaman kotun, lauyan ADC, Shaibu Aruwa (SAN), ya tunatar da kotun cewa tsohon mai sauraron ƙarar, Mai Shari’a Emeka Nwite, ya riga ya yi la’akari da waɗannan ɓangarorin a zaman da ya gabata. Ya roƙi kotun ta ba su damar bayyana dalilin da ya sa suke son shiga cikin shari’ar domin tabbatar da adalci ga kowa.

Sai dai lauyan mai ƙarar ya bayyana cewa Kotun Ƙoli ta umarci a gaggauta sauraron shari’ar, don haka ya nemi a ba dukkan ɓangarorin damar kammala shigar da takardunsu kafin a ci gaba da sauraron ƙarar. Lauyoyin ADC bangaren Sanata David Mark da Rauf Aregbesola da Ralph Nwosu ba su yi adawa da buƙatar ɗage sauraron ba.

Mai Shari’a Lifu ya bayyana cewa babu wanda ke da ikon zaɓar alkalin da zai saurari shari’arsa. Ya ce bisa umarnin Babban Alƙalin Kotun Tarayya da kuma hukuncin Kotun Ƙoli na gaggauta sauraron ƙarar, kotun za ta tabbatar da adalci ga kowane ɓangare.

Kotun ta kuma ɗora wa kanta alhakin rashin isar da sammaci ga waɗanda ke neman shiga cikin shari’ar, tare da umartar jami’in kotu ya kai musu takardun cikin sa’o’i 24. Haka kuma ta umurci dukkan ɓangarorin da su kammala shigar da takardunsu kafin ranar da za a sake zama.

A cikin ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1819/2025, Nafiu Bala Gombe, tsohon Mataimakin Shugaban ADC na Ƙasa, na neman kotu ta hana Sanata David Mark da Rauf Aregbesola da sauran shugabannin riƙo na jam’iyyar ci gaba da bayyana kansu a matsayin shugabannin ADC. Ya yi zargin cewa naɗinsu ya saɓa wa kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma Dokar Zaɓe.

Rikicin shugabancin ADC na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar ke shirin tunkarar zaɓen 2027, inda tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya samu tikitin takarar shugaban ƙasa daga wani ɓangaren jam’iyyar, yayin da wani ɓangaren kuma ya amince da Dumebi Kachikwu a matsayin ɗan takararsa.

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƴan Bindiga Sun Sace Ƙanwar Tsohon Ministan Wuta Bayo Adelabu Da Tagwayen ƳaƴantaWasu ƴan bindiga sun yi g...
03/06/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƴan Bindiga Sun Sace Ƙanwar Tsohon Ministan Wuta Bayo Adelabu Da Tagwayen Ƴaƴanta

Wasu ƴan bindiga sun yi garkuwa da ƙanwar tsohon Ministan Wutar Lantarki, Bayo Adelabu, tare da tagwayen ƴaƴanta a birnin Ibadan, jihar Oyo.

Kakakin Adelabu, Femi Awogboro, ya tabbatar da faruwar lamarin a safiyar ranar Laraba, inda ya bayyana cewa maharan sun kai hari a yankin Elewura da ke Challenge a Ibadan tare da yin awon gaba da matar da kuma tagwayen yaranta, Peter da Paul.

03/06/2026

Ga kadan daga cikin shirin Shugabanci A Yau tare da Malam Nazir Tahir Usman Bauchi, dan takarar Gwamnan jihar Bauchi a karkashin jam’iyyar APGA mai alamar Zakara.

Cikekken shirin yana tafe.

03/06/2026

Sabuwar wakar Alh Hussaini Saila shugaban mawakan Gwamna Bala Mohammed.

Allah Yayi rasuwa ma Hon. Yahaya Yaltin, tsohon ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar mazabar Toro/Jam...
02/06/2026

Allah Yayi rasuwa ma Hon. Yahaya Yaltin, tsohon ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar mazabar Toro/Jama’a a ƙaramar hukumar Toro.

Marigayin ya rasu ne a hannun wasu ɓata-gari da ake dangantawa da masu g@rkuw@ da mutane.

Iyalan marigayin sun sanar da cewa za a gudanar da sallar jana’izarsa da misalin ƙarfe 9:00 na safe a gobe Laraba a gidansu da ke Yaltin, a yankin Tulai da ke ƙaramar hukumar Toro.

Allah Ya gafarta masa. Ameen.

‎Jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce ba shi da tabbacin Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo ba zai ci ama...
02/06/2026

‎Jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce ba shi da tabbacin Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo ba zai ci amanarsa ba kamar yadda Gwamna Abba Kabir Yusuf da tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje s**a yi a cewarsa.

‎‎Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da Explorer Hausa, inda ya ce a siyasance babu wanda zai iya tabbatar da cikakkiyar biyayya daga wanda ya ɗora a kan wani matsayi, duk kuwa da irin amana da goyon bayan da aka nuna masa.

‎‎Sai dai jagoran Kwankwasiyyar ya jaddada cewa ya zaɓi Gwarzo ne bisa la’akari da ƙwarewa, jajircewa da kuma irin gudunmawar da ya bayar a tafiyar siyasar Kano da Kwankwasiyya.
‎‎
‎‎Kwankwaso ya ce tarihi ya nuna yadda wasu daga cikin waɗanda ya marawa baya a baya s**a sauya akala bayan sun samu mulki, lamarin da ya sa ba zai iya bayar da tabbacin abin da zai faru nan gaba ba.

-Premier Radio

Address

Dada Plaza, Opposite Fariah Foundation, Fadaman Masa Street
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani TV:

Share