Zamani TV

Zamani TV Zamani TV kamfani ne dake kawo sahihan labaran da suke faruwa a Najeriya harma da ƙasashen ƙetare. 09069687012 / 08169100019

04/08/2026

Na gamsu da mulkin Bola Tinubu. Atiku Abubakar ya fito daga North East kuma ya yi Mataimakin Shugaban Ƙasa a mulkin Olusegun Obasanjo, amma ko culvate bai taɓa yi wa yankinsa ba. Saboda haka, ban ga cancantarsa ta sake neman shugabancin Najeriya ba.

— Hon. Hamza Yusuf Muhammad.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta ayyana bullar cutar kwalara a hukumance bayan da aka samu ƙaruwar masu fama da gudawa mai tsan...
04/08/2026

Gwamnatin Jihar Bauchi ta ayyana bullar cutar kwalara a hukumance bayan da aka samu ƙaruwar masu fama da gudawa mai tsanani (Acute Watery Diarrhoea) tare da tabbatar da kamuwar wasu da cutar ta hanyar gwaje-gwajen dakin bincike.

Sanarwar, wadda Ma'aikatar Lafiya da Walwalar Jama'a ta Jihar Bauchi ta fitar a ranar 1 ga Agustan 2026, ta ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar Kwamitin Masana Kula da Yaɗuwar Cututtuka na jihar da kuma Cibiyar Gudanar da Ayyukan Gaggawa kan Lafiyar Jama'a.

Ma'aikatar ta bayyana cewa ayyana barkewar cutar ya yi daidai da ƙa'idojin Hukumar Lafiya ta Duniya na Kasa da Kasa (International Health Regulations 2005), Jagororin Ƙasa kan Shirin Kariya da Yaki da Kwalara, da kuma tsarin gudanar da matsalolin gaggawa na Ma'aikatar Lafiya ta Tarayya.

A cewar ma'aikatar, zuwa ranar 31 ga Yulin 2026, an samu mutum 398 da ake zargin sun kamu da cutar, yayin da aka samu rahotannin bullar cutar a ƙananan hukumomi 13 na jihar.

Haka kuma, mutane 16 sun rasa rayukansu sakamakon cutar, adadin da ya kai kaso huɗu cikin ɗari na waɗanda aka samu rahoton kamuwarsu.

Ƙananan hukumomin da cutar ta fi shafa sun haɗa da Toro, inda aka samu mutum 231 da ake zargi sun kamu, sai Alkaleri da Kirfi mai mutum 46 kowacce, Ganjuwa mai mutum 21, sannan Bauchi da Tafawa Balewa, inda aka samu mutum 14 a kowacce.

Ma'aikatar Lafiya ta yi kira ga abokan hulɗa a fannin ci gaba, ƙungiyoyin bayar da tallafi da kuma al'umma da su ba gwamnati haɗin kai wajen dakile yaɗuwar cutar.

Haka kuma ta buƙaci jama'a su kula da tsaftar muhalli da ta jiki, su riƙa shan ruwa mai tsafta, tare da garzayawa cibiyoyin lafiya idan s**a fara fama da gudawa mai tsanani ko amai, domin samun kulawar gaggawa.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da sakin kuɗi Naira miliyan 618,312,000 domin biyan tallafin karatu ga ɗaliban jihar 15...
04/08/2026

Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da sakin kuɗi Naira miliyan 618,312,000 domin biyan tallafin karatu ga ɗaliban jihar 15,000 da aka zaɓa a ƙarƙashin Shirin Tallafin Karatu na Cikin Gida na shekarar 2026.

Ana sa ran fara biyan kuɗaɗen ne da kaso na farko, wanda zai shafi ɗalibai daga cibiyoyin ilimi 14 da ke cikin jerin farko na shirin.

Cibiyoyin sun haɗa da Jami'ar Sa'adu Zungur (SAZU), Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU), Kwalejin Ilimi ta Azare, Abubakar Tatari Ali Polytechnic, Federal Polytechnic Bauchi, Adamu Tafawa Balewa College of Education Kangere, College of Agriculture Bauchi, Aliko Dangote College of Nursing Sciences Bauchi, Bill and Melinda Gates College of Health Sciences and Technology da ke Ningi, A.D. Rufai College of Legal and Islamic Studies da ke Misau, School of Nursing ta Asibitin Koyarwa na ATBU, Al-Muhibbah Open University, Bauchi Oil and Gas Academy da ke Alkaleri, da kuma Federal College of Education Jama'are.

Shirin tallafin karatun na cikin gida na gwamnatin jihar na da manufar tallafa wa ɗaliban Bauchi da ke karatu a manyan makarantun gaba da sakandare, domin rage musu nauyin kuɗaɗen karatu da kuma ƙarfafa su wajen ci gaba da neman ilimi.

Ana sa ran waɗanda aka zaɓa za su fara karɓar kuɗaɗen tallafin bisa tsarin da Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Bauchi ta tanada.

-Zamani TV

04/08/2026

Ina kira ga mambobin jam'iyyar PRP na Jihar Bauchi da su yi hattara da duk wani yunƙuri da ake yi na karkatar da hankalinsu daga goyon bayan Sanata Shehu Buba Umar. Haka kuma, muna kira ga al'ummar jihar Bauchi da su mara wa Sanata Shehu Buba Umar baya a zaɓen 2027 ƙarƙashin jam'iyyar PRP.

-Cewar Habibu Usman.

04/08/2026

Masu cewa Sanata Shehu Buba Umar ya bayyana inda yake samun kuɗinsa, shin sun taɓa jin EFCC, kotu ko ICPC sun gayyace shi? Babu ko ɗaya.

'Yan takarar gwamnan APC da APM duk 'yan crypto ne, amma Sanata Shehu Buba Umar shi ne mosquito coil, kuma shi za mu bi.

— Dr. Muslim Sulaiman (Dr. Ilela).

04/08/2026

Muna kira ga shugabannin jam'iyyar APC na Jihar Bauchi da na ƙasa da su tsayar da ɗan takarar da zai kawo wa jam'iyyar nasara. A ra'ayinmu, Hon. Kabiru Baba Maji ne ya fi cancanta. Haka kuma, bai kamata a cire fastocinsa daga ofisoshin jam'iyyar ba, tunda har yanzu ba a ayyana ɗan takarar gwamna ba.

— Cewar Tukur Kwaras.

04/08/2026

Abdurrashid Chemical Bakin Kura ya miƙa saƙon neman afuwa ga Hon. Hassana Arkila da magoya bayan mai girma gwamnan jihar Bauchi bisa kalaman da wani ɗan jam'iyyarsu ta APM ya yi a kanta.

Haka kuma, ya yi kira ga ɗan takarar gwamna na jam'iyyar APM da ya dakatar da mutumin daga matsayin dake kiran kansa na mai magana da yawunsa.

DA DUMI-DUMI: Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin NajeriyaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ...
04/08/2026

DA DUMI-DUMI: Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin Najeriya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ƙarin albashi ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce na inganta jin daɗin jami’an tsaro da ƙarfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Sanarwar da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata ta bayyana cewa kimanin jami’ai da sojoji 250,000 ne za su amfana da sabon tsarin albashin, wanda zai fara aiki daga 1 ga Satumban 2026.

A cewar sanarwar, jami’an da ke daga mukamin Brigadier Janar zuwa Janar za su samu ƙarin albashi na kashi 30 cikin ɗari, yayin da jami’an daga mukamin Kanal zuwa Warrant Officer za su samu ƙarin kashi 50 cikin ɗari. Haka kuma, sojojin da ke daga mukamin Private zuwa Staff Sergeant za su amfana da ƙarin albashi mafi girma na kashi 80 cikin ɗari.

Sanarwar ta ƙara da cewa sabon tsarin zai ƙara yawan kuɗin da gwamnati ke kashewa kan albashin jami’an sojin daga Naira biliyan 660 zuwa Naira biliyan 924 a duk shekara.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa na yaba wa jajircewa da sadaukarwar jami’an rundunar sojin wajen yaƙi da matsalolin tsaro da s**a haɗa da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan ƙasar.

Ya ce, “Mazan da matan da ke tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyinmu sun cancanci a tallafa musu tare da nuna musu godiya saboda hidimar da suke yi wa ƙasa. Gwamnatinmu za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin jami’an tsaro tare da samar musu da makamai da fasahohin zamani domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.”

Shugaban ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta iya samun ci gaba mai ɗorewa ba tare da ingantaccen tsaro ba, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen amfani da dukkan rundunonin tsaro domin kawar da barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya.

Tinubu ya kuma yi kira ga jami’an rundunar sojin da su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alamar godiya daga gwamnati bisa irin hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa Najeriya za ta yi nasara kan masu neman tada zaune tsaye da tarwatsa zaman lafiyar ƙasar.

DA DUMI-DUMI: Hon Hamza Koshe Akuyam ya fice daga jam'iyyar PDP.Alhaji Hamza Koshe Akuyam, ya sanar da ficewarsa daga ja...
04/08/2026

DA DUMI-DUMI: Hon Hamza Koshe Akuyam ya fice daga jam'iyyar PDP.

Alhaji Hamza Koshe Akuyam, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP).

A cikin takardar murabus mai kwanan wata 3 ga Agusta, 2026, wadda ya aike wa Shugaban PDP na Mazabar Akuyam/Osama da ke ƙaramar hukumar Misau, Hamza Koshe ya bayyana cewa ya daina kasancewa mamba a jam’iyyar daga ranar da ya rubuta takardar.

A cikin takardar, ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta ba shi na yin aiki tare da ita, yana mai cewa ya samu gagarumar karramawa da damar bayar da gudunmawa wajen cimma nasarori a lokacin da yake cikinta.

Ya kuma yi wa shugabanni da mambobin jam’iyyar fatan alheri, tare da nuna godiyarsa bisa haɗin kai da goyon bayan da s**a ba shi a tsawon lokacin da ya kasance mamba a PDP.

Takardar murabus ɗin ta nuna cewa shugabannin jam’iyyar a matakin mazaba sun karɓi sanarwar, tare da rubuta bayanin karɓa a jikin takardar.

Ɗan gwagwarmaya a tafiyar gidan Dr. Bala Wunti, Adamun Jibir, ya yi kira ga al'ummar Jihar Bauchi kada su yi kuskuren sa...
04/08/2026

Ɗan gwagwarmaya a tafiyar gidan Dr. Bala Wunti, Adamun Jibir, ya yi kira ga al'ummar Jihar Bauchi kada su yi kuskuren sake zaɓen ɗan takarar gwamna na jam'iyyar APC, M.A. Abubakar, a zaɓen 2027.

Adamun Jibir ya kasance masoyi kuma ɗan Jam'iyyar APC, ya bayyana cewa yana zargin wasu mutane tsiraru ne ɗaga cikin ƴaƴan jam'iyyar s**a kawo M.A Abubakar domin cimma wata manufa ta su. A cewarsa, idan al'ummar Bauchi s**a zaɓe shi, akwai yiwuwar zai fi yi wa waɗanda s**a kawo shi aiki maimakon ya fifita muradun al'ummar jihar Bauchi.

Adamun Jibir ya bukaci al’umma masu kaɗa ƙuri'a da su yi nazari sosai kafin su yanke hukuncin wanda zasu zaɓa a zaɓen 2027.

Address

Dada Plaza, Opposite Fariah Foundation, Fadaman Mada Street
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani TV:

Shortcuts

Share