Katagum Dailypost

Katagum Dailypost Labarai Da Zarar Sun Faru...
(1)

Bauchi Gov Swears In Four New Commissioners
05/08/2026

Bauchi Gov Swears In Four New Commissioners

Bauchi State Governor, Senator Bala Abdulkadir Mohammed, on Wednesday swore in four new commissioners to fill vacancies created by the resignation of former commissioners who stepped down to pursue elective positions ahead of the 2027 general elections. The swearing-in ceremony took place at the Exe...

BREAKING: WAEC Releases 2026 Results
05/08/2026

BREAKING: WAEC Releases 2026 Results

The West African Examinations Council (WAEC) has released the 2026 Computer-Based West African Senior School Certificate Examination (WASSCE) results for school candidates. The examination body announced on Wednesday that 1,200,514 candidates, representing 61.54 per cent, obtained credits in at leas...

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bayyana cewa ba ya goyon bayan kowane ɗan takarar shugaban ƙasa da za...
05/08/2026

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya bayyana cewa ba ya goyon bayan kowane ɗan takarar shugaban ƙasa da zai fafata a zaɓen 2027, yana mai karyata rahotannin da ke yawo cewa ya bayyana goyon bayansa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Bashir Adefaka, ya fitar a ranar Talata, Sarkin Musulmin ya bayyana rahotannin a matsayin ƙarya da yaudara, yana mai jaddada cewa matsayinsa a matsayin jagoran addini da na gargajiya ba ya ba shi damar nuna goyon baya ga wani ɗan takara.

Sanarwar ta ce Sarkin Musulmin ba shi da wani ɗan takarar da ya fi so, kuma ba zai bayyana goyon bayansa ga kowane mai neman takarar shugaban ƙasa ba, a fili ko a ɓoye.

"Mun lura da wani rahoto da ke yawo a wasu kafafen sada zumunta wanda ke ƙoƙarin nuna cewa Sarkin Musulmi ya buƙaci 'yan Najeriya su goyi bayan sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2027.

"Martaninmu a takaice shi ne, ba zai yiwu Sarkin Musulmi, wanda uba ne ga kowa, ya yi irin wannan furuci ba, a bainar jama'a ko a wani wuri," in ji sanarwar.

Sarkin Musulmin ya ƙara da cewa matsayinsa na buƙatar ya kasance mai adalci da nuna tsaka-tsaki ga kowa, ba tare da la'akari da jam'iyyar siyasa ko ra'ayin siyasar mutum ba.

Ya ce ofishin da yake riƙe da shi ya wajabta masa kauce wa siyasar jam'iyya, don haka ba zai marawa wani ɗan takarar shugaban ƙasa baya kafin gudanar da zaɓen 2027 ba.

Sanarwar ta kuma zargi masu alaƙanta Sarkin Musulmin da yaƙin neman zaɓen 2027 da ƙoƙarin jefa shi cikin siyasar jam'iyya domin cimma muradunsu na kashin kai.

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a SakkwatoDaga Aliyu ...
05/08/2026

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a Sakkwato

Daga Aliyu Samba

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division Garrison sun ceto mutum 14 da aka yi garkuwa da su tare da kwato dabbobi 281 da wasu ’yan bindiga s**a sace bayan sun kai hari ƙauyen Horo Birni da ke Ƙaramar Hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

Wata majiya mai tushe a rundunar sojin ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata, inda dakarun s**a gaggauta kai ɗauki bayan samun kiran neman agaji daga mazauna yankin.

Majiyar ta ce da isar sojojin, sun yi arangama da ’yan bindigar da ke tafiya da mutanen da s**a yi garkuwa da su tare da dabbobin da s**a sace daga ƙauyen.

Ta bayyana cewa sojojin sun yi wa ’yan bindigar ruwan wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa cikin ruɗani bayan sun samu raunukan harbin bindiga, s**a bar mutanen da s**a sace da kuma dabbobin.

A cewar majiyar, sojojin sun yi nasarar ceto mutane 14 tare da kwato shanu 195, tumaki 84, rakuma biyu da kuma babura biyu.

Ta ƙara da cewa gaggawar da sojojin s**a yi wajen kai ɗauki ta taimaka wajen ceton rayuka da dukiyoyin al’umma, tana mai yabawa haɗin gwiwar jami’an tsaro da ya taimaka wajen nasarar aikin.

Majiyar ta jaddada cewa dakarun sojin na ci gaba da kasancewa cikin shiri domin yaƙi da duk wani nau’in ta’addanci da laifuffuka, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai da kuma kai rahoton duk wani abin da ba su yarda da shi ba.

Manufofin Tinubu na bunƙasa masana'antu suna samar da ayyuka, ayyukan yi da ƙirƙire-ƙirƙire – Ministan Yaɗa LabaraiMinis...
05/08/2026

Manufofin Tinubu na bunƙasa masana'antu suna samar da ayyuka, ayyukan yi da ƙirƙire-ƙirƙire – Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bunƙasa masana'antu a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata suna ci gaba da samar da manyan ayyuka, ayyukan yi, ƙirƙire-ƙirƙire, da damarmakin tattalin arziki a faɗin ƙasar nan.

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Talata a hedikwatar Hukumar Bunƙasa Kimiyya da Injiniya ta Ƙasa (NASENI) da ke Abuja, yayin rangadin da Tawagar Yaɗa Labarai ta Fadar Shugaban Ƙasa ta kai hukumar.

Ya ce an ƙaddamar da Rangadin Yaɗa Labarai na Ajandar Sabunta Fata ne domin bai wa 'yan Nijeriya damar ganin ayyuka da shirye-shiryen da Gwamnatin Tarayya take aiwatarwa da idon su.

Ministan ya ce: “Muna son 'yan Nijeriya su gani da idon su yadda manufofin gwamnati ke komawa ayyuka na zahiri, samar da ayyukan yi, ƙirƙire-ƙirƙire, da damarmaki. Ana ƙara tabbatar da gaskiya idan hukumomin gwamnati suna hulɗa kai-tsaye da jama'a, kuma ana ƙara ƙarfafa ɗaukar nauyi idan 'yan ƙasa za su iya tantance cigaban da aka samu da kansu.”

Idris ya bayyana NASENI a matsayin muhimmiyar hukuma da ke jagorantar sauyin masana'antun Nijeriya ta hanyar kimiyya, aikin injiniya da fasaha, inda take aiwatar da ayyuka a fannonin masana'antun cikin gida, makamashi mai sabuntawa, aikin gona na zamani, fasahar zamani, da bunƙasa ƙwarewar ma'aikata.

A cewar sa, manufar Shugaba Tinubu ita ce gina tattalin arziki mai ɗorewa kuma mai dogaro da kai, wanda ya ta'allaƙa kan ƙirƙire-ƙirƙire, ƙara darajar kayayyakin cikin gida da kuma ƙarfafa gasa a fannin masana'antu.

Ya ce: “Manufar mu a bayyane take; ita ce sauya Nijeriya daga ƙasar da ta fi zama mai amfani da kayayyaki zuwa ƙasar da ke samarwa, ƙirƙire-ƙirƙire da fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.”

Ministan ya ƙara da cewa Ajandar Sabunta Fata ta sanya bunƙasa masana'antu, fasaha da ƙarfafa matasa a matsayin ginshiƙan sauya tattalin arzikin ƙasa, ta hanyar samar da yanayi mai kyau ga zuba jari, kasuwanci da samar da ayyukan yi masu ɗorewa.

Ya kuma yaba wa shugabanci da ma'aikatan NASENI bisa gudunmawar da suke bayarwa wajen bunƙasa fasaha da hanyoyin aikin injiniya na cikin gida domin ƙarfafa ƙarfin samar da kayayyaki a ƙasar da rage dogaro da kayayyakin da ake shigowa da su daga ƙasashen waje.

Haka kuma, Idris ya yaba wa membobin Tawagar Yaɗa Labarai ta Fadar Shugaban Ƙasa bisa rawar da suke takawa wajen bayyana gaskiya ta hanyar yaɗa sahihan bayanai, rahotanni masu daidaito da kuma na gani da ido kan yadda ake aiwatar da manyan shirye-shirye da ayyukan gwamnati.

Tun da farko, Mataimakin Shugaban Hukumar kuma Babban Jami'in Gudanarwa na NASENI, Khalil Suleiman Halilu, ya ce hukumar tana aiwatar da ingantacciyar dabarar bunƙasa masana'antu da ta mayar da hankali kan masana'antun cikin gida, musayar fasaha, ƙirƙire-ƙirƙire a fannin kiwon lafiya da kuma amfani da binciken kimiyya wajen samar da kayayyaki.

Ya ce ayyukan NASENI yanzu sun shafi manyan sassa takwas na masana'antu, tare da aiwatar da ayyuka a dukkan shiyyoyin siyasar ƙasar nan guda shida da kuma Babban Birnin Tarayya.

Halilu ya ce: “Manufar mu ita ce gina masana'antu masu ɗorewa ta hanyar ƙera kayayyakin da s**a dace da kasuwar Nijeriya, haɗa su a cikin gida, ƙara yawan abubuwan da ake samarwa a cikin gida a hankali, tare da gina masana'antun da za su iya yin gogayya a kasuwannin duniya. Ta haka ne muka samu damar kafa fiye da masana'antu 20 cikin ɗan ƙanƙanin lokaci.”

Daga cikin waɗanda s**a halarci taron akwai Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga; Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a, Cif Sunday Dare; Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Daidaita Manufofi, Hadiza Bala Usman; Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a, Temitope Ajayi; Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Hulɗa da Jama'a da Shigar da 'Yan Ƙasa Cikin Ayyukan Gwamnati; Malam Abdul'aziz Abdul'aziz; Mataimaki na Mussamman ga Shugaban Kasa kan Hudda da Jam'a da Wayar da Kai, da sauran manyan baƙi.

05/08/2026
Bauchi Gov’t Approves N618.3m Scholarship for 15,000 Students
04/08/2026

Bauchi Gov’t Approves N618.3m Scholarship for 15,000 Students

The Bauchi State Government has approved the release of N618.312 million for the payment of scholarships to 15,000 students selected under the 2026 Domestic Scholarship Programme, reaffirming its commitment to expanding access to higher education. The approved funds will be disbursed in the first ph...

Breaking: Tinubu Approves Up to 80% Salary Increase for Soldiers
04/08/2026

Breaking: Tinubu Approves Up to 80% Salary Increase for Soldiers

President Bola Tinubu has approved a salary increase of between 30 and 80 per cent for personnel of the Nigerian Armed Forces, with about 250,000 military personnel expected to benefit from the new pay package. According to a statement issued by the President’s Special Adviser on Information and S...

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Aikin Gyaran Titin Mando–Birnin Gwari Kan Naira Biliyan 178.1Daga Aliyu SambaGwamnatin ...
04/08/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Aikin Gyaran Titin Mando–Birnin Gwari Kan Naira Biliyan 178.1

Daga Aliyu Samba

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da aikin sake gina Titin Mando zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122.8 a Jihar Kaduna, wanda aka ware wa kuɗaɗen da s**a kai Naira biliyan 178.1. Titin ya tashi daga Mando da ke kusa da Filin Jirgin Sama na Kaduna zuwa iyakar Jihar Neja.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya wakilta wajen ƙaddamar da aikin a ranar Talata, ya ce aikin zai taimaka wajen inganta harkokin sufuri, ƙarfafa tsaro da kuma bunƙasa tattalin arzikin yankin. Ya ce titin na daga cikin manyan ayyukan raya ƙasa da za su ƙara haɗa yankunan Arewacin Najeriya da Kudu maso Yammacin ƙasar, tare da sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki.

Shugaban ya bayyana cewa aikin na cikin manyan ayyukan hanyoyin tarayya da gwamnatinsa ta amince da su a watan Mayun 2026 domin faɗaɗa ababen more rayuwa a faɗin ƙasar. Ya kuma tuna cewa tun lokacin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2022 ya yi alƙawarin sake gina titin idan aka zaɓe shi, yana mai cewa fara aikin ya nuna yadda gwamnatinsa ke cika alƙawuran da ta ɗauka ga 'yan Najeriya.

Tinubu ya ce tsawon shekaru da dama Titin Birnin Gwari ya kasance cikin halin lalacewa sakamakon rashin kulawa da gyara yadda ya kamata. Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen wannan matsala ta hanyar ci gaba da zuba jari a ayyukan hanyoyi, yana mai jaddada cewa matsayin Jihar Kaduna a matsayin ƙofar shiga yankin Arewa ya sa samar da ingantattun hanyoyi ya zama wajibi domin bunƙasa kasuwanci, zirga-zirga da ci gaban yankin.

Da yake jawabi, Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce aikin ya nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Tinubu na samar da ababen more rayuwa da za su inganta rayuwar al'umma kai tsaye. Ya ce baya ga ƙarfafa tsaro a hanyar, aikin zai buɗe damar bunƙasa noma a yankin, wanda zai taimaka wajen ƙara samar da abinci da kuma yaƙi da yunwa.

Umahi ya kuma bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu ta fara aiwatarwa suna ci gaba da haifar da sakamako mai kyau duk da ƙalubalen da gwamnatin ta gada a shekarar 2023. "Ta hanyar aiwatar da wannan aiki, Shugaban Ƙasa na cika alƙawarin da ya ɗauka ga al'umma, kuma hakan zai haifar da gagarumin sauyi a fannin noma a wannan yanki," in ji shi.

Tun da farko, Babban Sakataren Ma'aikatar Ayyuka ta Tarayya, Adeladan Rafiu Olarinre, ya ce aikin wani ɓangare ne na shirin gwamnatin tarayya na zamani da faɗaɗa hanyoyin Najeriya. Ya ce ana sa ran kammala aikin zai rage wahalar zirga-zirga, ya ƙara bunƙasa kasuwanci, tare da haɓaka tattalin arzikin Jihar Kaduna da jihohin da ke maƙwabtaka da ita.

Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin NajeriyaDaga Aliyu SambaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu...
04/08/2026

Tinubu Ya Amince da Ƙarin Albashi Har Kashi 80 Ga Jami’an Sojin Najeriya

Daga Aliyu Samba

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ƙarin albashi ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce na inganta jin daɗin jami’an tsaro da ƙarfafa musu gwiwa wajen gudanar da ayyukansu.

Sanarwar da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata ta bayyana cewa kimanin jami’ai da sojoji 250,000 ne za su amfana da sabon tsarin albashin, wanda zai fara aiki daga 1 ga Satumban 2026.

A cewar sanarwar, jami’an da ke daga mukamin Brigadier Janar zuwa Janar za su samu ƙarin albashi na kashi 30 cikin ɗari, yayin da jami’an daga mukamin Kanal zuwa Warrant Officer za su samu ƙarin kashi 50 cikin ɗari. Haka kuma, sojojin da ke daga mukamin Private zuwa Staff Sergeant za su amfana da ƙarin albashi mafi girma na kashi 80 cikin ɗari.

Sanarwar ta ƙara da cewa sabon tsarin zai ƙara yawan kuɗin da gwamnati ke kashewa kan albashin jami’an sojin daga Naira biliyan 660 zuwa Naira biliyan 924 a duk shekara.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa na yaba wa jajircewa da sadaukarwar jami’an rundunar sojin wajen yaƙi da matsalolin tsaro da s**a haɗa da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan ƙasar.

Ya ce, “Mazan da matan da ke tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyinmu sun cancanci a tallafa musu tare da nuna musu godiya saboda hidimar da suke yi wa ƙasa. Gwamnatinmu za ta ci gaba da ba da fifiko ga jin daɗin jami’an tsaro tare da samar musu da makamai da fasahohin zamani domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.”

Shugaban ya kuma jaddada cewa babu wata ƙasa da za ta iya samun ci gaba mai ɗorewa ba tare da ingantaccen tsaro ba, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen amfani da dukkan rundunonin tsaro domin kawar da barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Najeriya.

Tinubu ya kuma yi kira ga jami’an rundunar sojin da su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alamar godiya daga gwamnati bisa irin hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana ƙwarin gwiwar cewa Najeriya za ta yi nasara kan masu neman tada zaune tsaye da tarwatsa zaman lafiyar ƙasar.

Address

Kasuwar Kaji Azare
Bauchi

Telephone

+2347086806558

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katagum Dailypost posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katagum Dailypost:

Shortcuts

Share