03/06/2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta Aiki
Gwamnatin Tarayya ta ɗauki gabarar daidaita ayyukan hukumar yaƙi da kwararar hamada ta kasa, wato National Agency for the Great Green Wall (NAGGW), inda ta mayar da babban ofishinta na gudanar da ayyuka daga birnin tarayya Abuja zuwa jihar Kano.
Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ne ya bayyana hakan, inda ya bayyana cewa matakin na kunshe ne a karkashin tsarin 'Renewed Hope Agenda’ na Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Manufar hakan ita ce tallafa wa hukumar don ta gudanar da ayyukanta cikin hanzari da nagarta a jihohin da abin ya shafa.
Shirin na 'Great Green Wall' babban yunkuri ne na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da ya kunshi kasashe 11, da nufin yaki da kwararar hamada, lalacewar kasa, da kuma radadin sauyin yanayi a yankin Sahel da Sahara.
A nan Najeriya, shirin ya karkata ne a kan jihohi 11 na gaba-gaba da hamada ke barazana musamman ga rayuwarsu, wadanda s**a hada da: Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto, Yobe, Zamfara, da kuma Adamawa.
Ministan ya kara da cewa, babban burin hukumar shi ne shimfida dangar bishiyoyi (Green Wall) mai nisan kilomita 15 a fadi, da kuma tsawon kilomita 1,500 domin kare muhalli, rage radadin sauyin yanayi, samar da wadatar abinci, da kuma rage radadin talauci a karkara.
Tun lokacin da aka kaddamar da shirin a shekarar 2013, kafin daga bisani a mayar da shi cikakkiyar hukuma a 2015, an samu manyan nasarori k**ar haka:
Kafa dangar kariya daga iska da yashi (shelterbelts) fiye da guda 100.
Gina madatsun ruwa na sola da iskar gas guda 159 don samar da ruwan sha.
Daukar matasa guda 600 a matsayin dogaran daji (forest guards).
Samar da gonakin bishiyoyin itatuwa na (orchards and woodlots) guda 240 don bunkasa kudin shiga.
Malam Balarabe Abbas Lawal ya jaddada cewa, wannan sauyi zai magance kalubalen da hukumar ta dade tana fuskanta na gudanar da ayyuka daga ofishin haya a Abuja, wanda ke nesa da ainihin inda ayyukan suke a Arewa. Komawa Kano, wadda ita ce cibiyar yankunan da ayyukan s**a shafa, zai ba da damar sanya ido, da samar da kyakkyawar alaka tsakanin gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, da al'ummomin yankunansu.
Jihar Kano riga ta saba da irin wadannan ayyuka, domin tana dauke da ofishin tsara shirye-shiryen dashen bishiyoyi (APCU) tun a shekarar 1988, wanda yanzu ba a amfani da shi yadda ya k**ata tun bayan kammala shirin Bankin Duniya na dashen bishiyoyi a yankunan fari (Arid Zone Afforestation Programme) a shekarar 1996. Wannan cigaba a yanzu zai cigaba a hukumar ta NAGGW.
Daga karshe, Ministan ya bayyana yakinin cewa wannan mataki na kusanto da hukumomi kusa da inda suke aiki zai kawo sauyi na gaske ga rayuwar miliyoyin 'yan Najeriya da ke zaune a yankunan da kwararar hamada ke addaba.