Katagum Dailypost

Katagum Dailypost Labarai Da Zarar Sun Faru...

Jerin sunayen Sojoji 16 da s**a yi kokarin yin juyin mulki a Najeriya. Jaridar Premium Times ta rawaito cewa rundunar so...
30/10/2025

Jerin sunayen Sojoji 16 da s**a yi kokarin yin juyin mulki a Najeriya.

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa rundunar sojin Najeriya ta bayyana sunayen sojoji 16 da Hukumar Leƙen Asirin Tsaron Najeriya ke tsare da su bisa zargin yunƙurin shirya juyin mulki a ƙasar.

Ga cikakken sunayen k**ar yadda jaridar ta rawaito:

Brigadier General Musa Abubakar Sadiq

Colonel M.A. Ma’aji

Lieutenant Colonel S. Bappah

Lieutenant Colonel A.A. Hayatu

Lieutenant Colonel P. Dangnap

Lieutenant Colonel M. Almakura

Major A.J. Ibrahim

Major M.M. Jiddah

Major M.A. Usman

Major D. Yusuf

Major I. Dauda

Captain Ibrahim Bello

Captain A.A. Yusuf

Lieutenant S.S. Felix

Lieutenant Commander D.B. Abdullahi

Squadron Leader S.B. Adamu.

Tinubu ya umarci sabbin hafsoshin tsaro su zama masu hazaƙa wajen yakar ta’addanci da barazanar tsaroShugaban Najeriya B...
30/10/2025

Tinubu ya umarci sabbin hafsoshin tsaro su zama masu hazaƙa wajen yakar ta’addanci da barazanar tsaro

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya bukaci sabbin hafsoshin tsaro da ya nada su kasance masu samar da sabbin dabaru da jajircewa wajen tinkarar ta’addanci da barazanar tsaro da ke addabar kasar.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karrama sabbin hafsoshin tsaro da muk**ansu a fadarsa da ke Abuja ranar Alhamis.

Tinubu ya bayyana wannan yunƙurin a matsayin wata sabuwar aniya da jajircewar gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro ga ‘yan Najeriya baki ɗaya.

“Yau ba wai bikin ba da muk**ai kawai muke yi ba, muna sabunta kudirinmu na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a ƙasa. Sojojinmu sun bayar da gudunmawa mai girma wajen kare ƙasar nan, wasu ma sun sadaukar da rayukansu don zaman lafiyar Najeriya,” in ji shi.

Shugaban ya yaba da kokarin dakarun soji wajen dawo da zaman lafiya a yankunan da aka taba samun rikice-rikice da kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, yana mai cewa hakan ya raunana ƙungiyoyin ta’addanci da ke ƙasar.

Sai dai ya gargadi sabbin hafsoshin cewa barazanar tsaro tana ta sauyawa, inda sabbin ƙungiyoyin ‘yan bindiga da masu tayar da hankali ke fitowa musamman a Arewa ta Tsakiya, Arewa maso Yamma da wasu sassan Kudu.

“Ba za mu bari wannan barazanar ta ci gaba yaduwa ba. Dole mu yi gaggawa mu murƙushe su tun kafin su yi ƙarfi. Mu sare kan macijin tun wuri,” in ji Tinubu.

Ya kuma shawarce su da su yi amfani da fasahar zamani da sabbin dabaru domin su kasance gaba da waɗanda ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali na ƙasa.

“Ina so ku zama masu samar da sabbin dabaru, masu hangen nesa da jarumtaka. ‘Yan Najeriya suna jiran sak**ako, ba ƙorafi ba,” in ji shugaban.

Shugaban ƙasar ya kuma sake tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa rundunonin soji da kayan aiki da duk wata bukata don cimma nasarar aiki.

A jawabinsa bayan karramawar, Babban Hafsan Tsaron ƙasa, Janar Olufemi Oluyede, wanda ya yi maga

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabon harajin shigo da man fetur da dizal na kashi 15 cikin 100, wanda...
30/10/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabon harajin shigo da man fetur da dizal na kashi 15 cikin 100, wanda ake sa ran zai ƙara kimanin N100 a kowace lita.

Matakin, wanda aka tsara domin ƙarfafa matatun man cikin gida da daidaita kasuwar man fetur, zai fara aiki nan take, bisa wasiƙar da aka aikewa Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS) da Hukumar Kula da Man Fetur (NMDPRA).

Shugaban FIRS, Zacch Adedeji, ya ce wannan tsari na daga cikin gyare-gyaren gwamnati don rage dogaro da shigo da mai daga ƙasashen waje da kuma ƙarfafa tattalin arzikin cikin gida.

Sai dai masana sun gargadi cewa sabon harajin zai iya jawo ƙarin farashi da tashin hankali a kasuwa, musamman ga masu amfani da man fetur a gida da masana’antu.

Ɗan Majen Katagum Ya Karɓi Takardar Wankewa Daga Gwamnatin Jihar BauchiGwamnatin Jihar Bauchi ta tsarkake tsohon Hakimin...
30/10/2025

Ɗan Majen Katagum Ya Karɓi Takardar Wankewa Daga Gwamnatin Jihar Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi ta tsarkake tsohon Hakimin Cikin Garin Azare, Alhaji Bashir Kabir Umar (Ɗan Majen Katagum), daga duk wani zargi da ya haifar da cire shi daga sarauta a lokacin zaɓen 2023.

A lokacin zaben, an dakatar da Ɗan Maje bisa zargin karya dokar hana masu rike da sarauta shiga harkokin siyasa. Sai dai yanzu, gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa babu wani laifi da aka tabbatar masa da shi, inda ta ba shi takardar wanke suna daga ofishin Gwamna, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed.

Wannan mataki ya nuna cewa Ɗan Maje ya samu cikakkiyar ’yanci don tsayawa takara ko neman duk wani mukami na siyasa a ƙasar nan — har ma da na shugaban ƙasa — ba tare da wata tangarda ta doka ba.

Da yake jawabi bayan karɓar takardar, Alhaji Bashir Kabir Umar ya bayyana matuƙar godiyarsa ga Gwamna Bala Mohammed bisa abin da ya kira adalci, gaskiya da kishin ci gaban al’umma.

“Wannan mataki ya sake tabbatar da halin shugabanci na gaskiya da adalci da Gwamnan Bauchi ke nunawa. Gwamna Bala mutum ne mai hangen nesa da jajircewa wajen ganin jihar Bauchi ta ci gaba,” inji shi.

Ɗan Maje ya kuma yaba da shirin gwamnatin jihar wajen kafa sabbin masarautu da ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin jama’ar Bauchi, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki da zaman lafiya.

A wani ɓangare na jawabinsa, ya nuna godiya ta musamman ga Masarautar Katagum da al’ummar yankin:

“Masarautar Katagum ita ce uwa kuma tushenmu. Mu da muke alfahari da ita a kowane lokaci,” in ji Ɗan Maje.

A ƙarshe, Ɗan Maje ya mika godiya ga jama’ar Katagum da Bauchi baki ɗaya bisa goyon baya da addu’o’in alheri da suke masa, yana mai tabbatar da cewa zai ci gaba da ba da gudunmawa wajen ci gaban jihar Bauchi da Najeriya baki ɗaya.

KBC Hausa

30/10/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da sabon babban hafsan sojan ƙasa na Najeriya Lt Gen Wahidi Shaibu yanzu haka a fadar shugaban ƙasa.

Hukumar NELFUND ta raba fiye da Naira biliyan 116 ga dalibai sama da dubu 600 tun bayan kaddamar da shirin lamunin a Naj...
30/10/2025

Hukumar NELFUND ta raba fiye da Naira biliyan 116 ga dalibai sama da dubu 600 tun bayan kaddamar da shirin lamunin a Najeriya

Hukumar bayar da lamunin karatu ta Najeriya (NELFUND) ta ce ta raba sama da Naira Biliyan 116.4 ga dalibai fiye da 624,000 tun bayan kaddamar da shirin lamunin karatu a ranar 24 ga Mayu, 2024.

A cewar rahoton da hukumar ta fitar a shafinta na X (Twitter) a ranar Talata, 28 ga Oktoba, NELFUND ta karɓi fiye da rejistar ɗalibai 929,000, inda sama da 624,000 daga cikinsu s**a amfana da shirin.

Rahoton ya nuna cewa an amince da sabbin masu rejista 12,398, adadin da ya kai ƙarin kaso 1.4 cikin 100 idan aka kwatanta da rahoton baya.

Hukumar ta kuma bayyana cewa daga cikin kudaden da aka rarraba, An biya Naira Biliyan 65.3 kai tsaye ga makarantu 239 a fadin ƙasar a matsayin kudin makaranta, yayin da aka bada Naira Biliyan 51.1 ga dalibai a matsayin kudin walwala da abinci, jimillar kudin ya k**a Naira Biliyan 116.4 zuwa yanzu.

A wani bangare na sanarwar, NELFUND ta bayyana bude sabon shafin neman lamunin karatu domin zangon karatu na 2025/2026, wadda za a bude daga Alhamis, 23 ga Oktoba, zuwa Asabar, 31 ga Janairu, 2026.

A cewar darektan sadarwa na hukumar, Oseyemi Oluwatuyi, sabbin masu neman lamuni za su iya amfani da lambar shiga jami’a (admission number) ko lambar JAMB wajen cikawa, maimakon lambar dalibi (matric number).

Hukumar NELFUND dai an kafa ta ne bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar kafa shirin lamunin dalibai a watan Afrilu 2024. Shirin yana bai wa daliban da ke karatu a makarantu na gwamnati damar samun lamuni ba tare da ruwa ba, domin biyan kudin makaranta da kuma samun kuɗin abinci yayin karatu.

Manufar shirin ita ce rage cikas na kudi da ke hana matasa shiga manyan makarantu da kuma bunkasa damar ilimi ga ‘ya’yan talakawa.

Ana sa ran daliban da s**a ci gajiyar shirin za su fara biyan lamunin bayan sun sami aikin yi da zarar sun kammala karatunsu.

Hukumar da ke kula da ayyukan Hukumar Tsaron Ƙasa, Hukumar Gidan Gyaran Hali, Hukumar Kashe Gobara, da Hukumar Shige da ...
30/10/2025

Hukumar da ke kula da ayyukan Hukumar Tsaron Ƙasa, Hukumar Gidan Gyaran Hali, Hukumar Kashe Gobara, da Hukumar Shige da Fice (CDCFIB) ta fitar da jerin sunayen waɗanda s**a cancanci rubuta jarabawar na’ura mai ƙwaƙwalwa (CBT) domin daukar sabbin ma’aikata a hukumomin tsaron da ke ƙarƙashinta.

A cikin wata sanarwa da sakataren hukumar, Manjo Janar Abdulmalik Jubril (mai ritaya) ya fitar a Abuja ranar Laraba, ya bayyana cewa, hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Hukumar Kula da gidan gyaran hali ta Ƙasa, Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa, Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa da kuma Hukumar Tsaron Cikin Gida ta Civil Defence.

Sanarwar ta ce duk masu neman gurbin aiki a ɗaya daga cikin waɗannan hukumomi su ziyarci shafin hukumar na yanar gizo wato https://recruitment.cdcfib.gov.ng daga ranar Alhamis, 30 ga Oktoba, domin tantance ko sun samu gurbin zuwa mataki na gaba.

Hukumar ta kuma gargadi masu nema da su tabbatar da amfani da shafin da aka bayar kawai domin gujewa fadawa hannun ’yan damfara.

Daukar sabbin ma’aikatan dai yana daga cikin ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa hukumomin tsaro da kuma samar da damar aikin yi ga matasa a fadin ƙasar.

Bauchi Assembly Approves Creation of 29 New LGAs
30/10/2025

Bauchi Assembly Approves Creation of 29 New LGAs

The Bauchi State House of Assembly has passed into law a bill providing for the creation of 29 new Local Government Areas (LGAs) across the state.Advertisement According to the document signed by Musa Yerima, Acting Deputy Clerk of the House, and addressed to Senator Barau Jibrin, Chairman of the Se...

Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta amince da ƙirƙirar sababbin ƙananan hukumomi guda 29 daga cikin guda 20 da ake da su a...
30/10/2025

Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta amince da ƙirƙirar sababbin ƙananan hukumomi guda 29 daga cikin guda 20 da ake da su a halin yanzu.

Wannan kuduri tuni majalisar ta karanta shi daga karatu na farko zuwa na ƙarshe, sannan ta tura shi zuwa kwamitin da ya dace domin duba yiwuwar aiwatar da shi.

Farashin abinci na ƙara sauƙi a Najeriya yayin da gwamnati ke samun cigaba a fannin tattalin arzikiRahotanni daga jihohi...
29/10/2025

Farashin abinci na ƙara sauƙi a Najeriya yayin da gwamnati ke samun cigaba a fannin tattalin arziki

Rahotanni daga jihohin Arewa maso Yamma na nuna cewa farashin kayan abinci ya fara raguwa a kasuwanni sak**akon girbin damina mai albarka da manoma s**a samu a bana. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnati ke ci gaba da aiwatar da manufofin tallafawa harkar noma da kuma tabbatar da wadatar abinci a ƙasar.

A jihohin Kaduna, Kano da Katsina, manoma sun tabbatar da cewa an samu kyakkyawan girbi na hatsi, tumatir, dawa, gero da shinkafa, abin da ya janyo farashin kayan abinci ya ragu sosai idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

A kasuwannin Kaduna misali, buhun shinkafa na kilo 50 da ake sayarwa a kan Naira 100,000 a baya, yanzu ya koma tsakanin Naira 50,000 zuwa Naira 63,000. Haka kuma farashin kwandon tumatir ya sauka daga Naira 120,000 zuwa Naira 35,000.

Wani ɗan kasuwa a Dawanau, Alhaji Bala Ali, ya tabbatar da cewa “yawan amfanin gona daga kauyuka ya ƙaru sosai, abin da ya taimaka wajen daidaita farashin abinci da kuma tabbatar da wadatar kayan masarufi a kasuwa.”

A jihar Kano, rahotanni sun ce yawancin manoma sun samu gagarumin girbi saboda yanayin ruwan sama da ya yi daidai da lokacin noma. Wasu manoma ma sun yaba da shirin Special Agro-Industrial Processing Zone (SAPZ) da s**a ce ya taimaka wajen samun iri da dabarun noma na zamani.

Wani manomi a Bebeji, Malam Audu Muzammil, ya ce, “Ruwan sama ya yi wadata kuma kwari sun yi ƙasa matuƙa. Daman abinda ya rage mana shi ne adana kayanmu yadda ya k**ata. Amma girbi ya yi albarka sosai.”

A jihar Katsina kuwa, duk da cewa wasu manoma sun koka da tsadar takin zamani, suna murna da cewa farashin kayan abinci ya ragu, abin da ya sa mutane da dama ke iya siyan abinci cikin sauƙi.

Malam Kabir Sabiu, wani manomi daga Katsina, ya ce “duk da cewa mun yi asara saboda farashi ya fadi, muna godewa Allah saboda jama’a da dama yanzu suna iya siyan abinci cikin rahusa. Wannan ma wata ni’ima ce.”

Masana tattalin ar

Shugaba Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni tare da mayar da ofishin kwamitin bada afuwa zuwa ma’aikatar shari’aShugaba...
29/10/2025

Shugaba Tinubu ya yi afuwa ga wasu fursunoni tare da mayar da ofishin kwamitin bada afuwa zuwa ma’aikatar shari’a

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan takardun bada afuwa da sassauci ga wasu mutane da aka yanke wa hukunci bisa laifuka daban-daban, a wani mataki na aiwatar da ikon sa na yin afuwa bisa kundin tsarin mulkin Najeriya.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, shugaban kasar ya ce ya dauki matakin ne bayan tuntubar majalisar koli ta kasa da kuma bayan samun ra’ayoyin jama’a kan batun.

Sai dai bayan sake duba jerin sunayen wadanda za su ci gajiyar afuwar, an cire wadanda aka samu da manyan laifuka irin su garkuwa da mutane, safarar miyagun kwayoyi, cinikin mutane, zamba, da mallakar mak**ai ba bisa ka’ida ba.

A cewar fadar shugaban kasa, wannan matakin ya zama dole saboda laifukan da s**a shafi tsaro da tasirin su ga al’umma, da kuma bukatar kare hakkin wadanda aka zalunta da karfafa gwiwar hukumomin tsaro.

Sanarwar ta kara da cewa an tura sabuwar takardar sunayen wadanda s**a cancanci afuwa zuwa hukumar kula da gidajen gyaran hali domin aiwatar da shi.

Shugaba Tinubu ya kuma bayar da umarnin mayar da ofishin sakateriyar kwamitin bada afuwa daga ma’aikatar ayyuka na musamman zuwa ma’aikatar shari’a ta tarayya.

Bugu da ƙari, ya umarci babban lauyan kasa, da ya fitar da sabbin ka’idoji da zasu jagoranci tsarin bada afuwa nan gaba, ciki har da shawarwari da hukumomin shari’a kafin daukar mataki.

Shugaban kasar ya gode wa jama’a da masu ruwa da tsaki bisa shawarwari da s**a bayar, tare da tabbatar da kudirin gwamnatinsa na inganta tsarin shari’a da tabbatar da adalci a Najeriya.

Allah Ya Tabbatar Mana
29/10/2025

Allah Ya Tabbatar Mana

Address

Kasuwar Kaji Azare
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katagum Dailypost posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katagum Dailypost:

Share