Katagum Dailypost

Katagum Dailypost Labarai Da Zarar Sun Faru
(1)

Gwamnati Ta Kashe Naira Biliyan 88 Wajen Gyaran Kayan Wutar Lantarki Da Aka Lalata Tun Daga 2021Gwamnatin tarayya ta kas...
10/08/2025

Gwamnati Ta Kashe Naira Biliyan 88 Wajen Gyaran Kayan Wutar Lantarki Da Aka Lalata Tun Daga 2021

Gwamnatin tarayya ta kashe Naira biliyan 88 wajen gyara da dawo da wuraren samar da wutar lantarki da aka lalata a fadin kasar nan tsakanin shekarar 2021 zuwa yanzu.

Babban mai kula da layukan wutar lantarki na kamfanin Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) reshen Legas, Seyi Onabajo, ne ya bayyana hakan yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar a tashar wutar lantarki ta Odogunyan 132KV, dake Ikorodu, a jihar Legas.

Onabajo ya ce adadin kudin da aka kashe kan gyare-gyaren ya yi matukar yawa, inda ya bayyana cewa maimakon a yi amfani da kudaden da aka samu daga yan kasa da gwamnati wajen inganta hanyoyin samar da wuta, sai ake amfani da su wajen gyara lalacewar da ta biyo bayan ta’addancin wasu bata gari a wuraren samar da wutar lantarki. Ya ce wannan matsala ce ke shafar yunkurin samar da wutar lantarki na tsawon sa’o’i 24 a kowace rana.

Ya yi kira ga al’umma da su taimaka wajen kare kayayyakin samar da wutar lantarki a yankunansu, yana mai jaddada cewa duk wani hari da ake kai wa kayan aikin na rage damar samar da wutar da kuma jinkirta shirin tabbatar da cewa dukkan yan Najeriya sun samu wadatar wutar lantarki yadda ya kamata.

Gwamnati Ta Yi Alkawarin Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Lafiya Kafin Ƙarshen Watan AgustaGwamnatin Tarayya ta tabbatar...
10/08/2025

Gwamnati Ta Yi Alkawarin Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Lafiya Kafin Ƙarshen Watan Agusta

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa likitoci da sauran ma’aikatan kiwon lafiya cewa za ta biya bashin albashin watanni bakwai da suke bi kafin ƙarshen watan Agusta 2025. Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Ali Pate, ne ya bayyana haka a wani taron haɗin gwiwa da shugabannin manyan ƙungiyoyin ma’aikatan lafiya a Abuja.

Wannan mataki ya biyo bayan wa’adin kwanaki 21 da ƙungiyar likitoci ta ƙasa (NMA) ta bai wa gwamnati don magance matsalolin walwala, tare da barazanar yin yajin aiki na ƙasa.

A baya-bayan nan, ƙungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta ƙasa (NANNM) ta dakatar da yajin aikin gargadi bayan shiga tsakani daga masu ruwa da tsaki. Don kauce wa sake samun cikas a fannin kiwon lafiya, ma’aikatar lafiya ta shirya babban taro na musamman da ya haɗa da NMA, NANNM, da ƙungiyar hadin gwiwar ma’aikatan lafiya (JOHESU), tare da wakilai daga Ma’aikatar Harkokin Jin Kai.

Bayan taron, Farfesa Pate ya jaddada kudirin gwamnati na biyan bashin albashin da suke bi, tare da nuna cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirye don magance matsalolin da suke kewaye da tsarin kiwon lafiya a ƙasar. Shugaban NMA, Farfesa Bala Audu, da shugaban JOHESU na ƙasa, Kwamared Kabiru Minjibir, sun bayyana fatan cewa gwamnati za ta cika alkawuranta, domin hakan zai iya hana faruwar yajin aikin da ke tafe.

NYSC ta bada dalilin da ya sa aka riƙe shaidar kammala hidimar ƙasa ta wata ƴar bautar ƙasa, Uguamaye Hukumar  Kula da S...
10/08/2025

NYSC ta bada dalilin da ya sa aka riƙe shaidar kammala hidimar ƙasa ta wata ƴar bautar ƙasa, Uguamaye

Hukumar Kula da Shirin Bautar Ƙasa (NYSC) ta bayyana dalilin da ya sa ta riƙe takardar kammala hidimar ƙasa ta Rita Uguamaye, wata da ya yi sunan kananan bayan ta soki Shugaba Bola Tinubu kan halin da ƙasar ke ciki.

Uguamaye ta shiga cikin labarai bayan ta soki Gwamnatin Tarayya kan jinkirin biyan kuɗin alawus da aka ƙara ga masu hidima daga N33,000 zuwa N77,000.

A cikin wani faifan bidiyo da ya yadu, Uguamaye ta ce jinkirin biyan kuɗin ya jefa abokan hidimarta cikin ƙuncin rayuwa marar amfani.

Daily Trust ta rawaito cewa a halin yanzu, rahotanni na cewa an riƙe mata takardar kammala hidima na haifar da cece-kuce.

“Rita na daga cikin ‘yan hidimar ƙasa 131 da aka dakatar da takardunsu na kammala hidima (CNS) saboda dalilai na ladabtarwa da s**a dace. Musamman, an ƙara mata watanni biyu a shekarar hidimarta saboda rashin halartar tantancewa na watan Afrilu 2025, wanda ya yi daidai da dokokin NYSC.

“Ya kamata a lura cewa wannan ƙarin lokaci hanya ce ta yau da kullum, ba kuma ta musamman a nata lamarin ba, kuma an yi hakan ne bisa tsarin adalci daidai ga kowa.”

NYSC ta ce ko kadan riƙe shaidar kammala hidimar ƙasa ta Rita bashi da gami da kalaman da ya yi a baya.

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Sama da Naira Biliyan 80 Ga Dalibai 400,000 — NELFUNDShugaban Hukumar Lamunin Dalibai ta Kasa ...
09/08/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Sama da Naira Biliyan 80 Ga Dalibai 400,000 — NELFUND

Shugaban Hukumar Lamunin Dalibai ta Kasa (NELFUND), Akintunde Sawyerr, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta riga ta raba fiye da naira biliyan 80 ga cibiyoyin ilimi daban-daban a Najeriya domin tallafa wa dalibai da lamunin biyan kudin makaranta. Ya bayyana cewa kimanin dalinai 745,000 ne s**a nemi lamunin, inda a yanzu fiye da dalibai 400,000 s**a amfana da lamunin. Wasu daga cikin daliban suna samun biyan kudin makaranta kai tsaye zuwa jami’o’in su, sannan masu neman tallafin kashe kuɗi suna karɓar N20,000 a kowane wata cikin zangon karatu.

Sawyer ya bayyana cewa duk lamunin da ake bayarwa ba su da kudin ruwa a kansu. Ya ce akwai nau’i biyu na lamuni, na biyan kudin makaranta wanda ake turawa kai tsaye ga makaranta, da kuma na tallafin kudin kashewa ga ɗalibi.

A cewar Sawyer, shirin NELFUND na taimaka wa dalibai yana rage yawan masu daina zuwa makaranta a matakin gaba da sakandare saboda ƙarancin kuɗi. Ya ce hukumar tana ci gaba da karɓar sabbin masu rejista, inda cikin sa’o’i 24 da s**a wuce kadai aka samu sama da 2,700 daga sabbin dalibai sun nema.

Presidency In Nigeria Should Be Five-Year Single Tenure — Obi
08/08/2025

Presidency In Nigeria Should Be Five-Year Single Tenure — Obi

Peter Obi, 2023 Presidential candidate of the Labour Party (LP), has advocated for a five-year single term for President in Nigeria.Advertisement Obi stated this in Bauchi on Friday when he paid a courtesy visit on Governor Bala Mohammed of Bauchi State. According to him, there shouldn’t be any se...

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samu...
08/08/2025

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya ta haɗa gwiwa da Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya domin wayar da kan ‘yan Nijeriya kan sababbin ƙa’idojin neman bizar Amurka tare da tabbatar da bin ƙa’ida yayin neman.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka a taron manema labarai da ya gudana tare da Jakaden Amurka a Nijeriya, Richard M. Mills Jr., a Abuja ranar Juma’a.

Ya ce wannan yekuwar wayar da kan ta zama dole saboda Amurka tana ci gaba da zama ɗaya daga cikin wuraren da ‘yan Nijeriya suke yawan ziyarta.

Idris ya ce a tsawon shekaru ‘yan Nijeriya suna tafiya Amurka saboda dalilai daban-daban, ciki har da yawon buɗe ido, kasuwanci, karatu, da kuma neman magani.

Ya ce: “An san Nijeriya a duniya a matsayin ƙasar da ‘yan ƙasar ta suke yawan yin tafiya zuwa ƙasashe daban-daban, suna hulɗa da ƙasashen duniya ta fuskar harkar kasuwanci, ilimi, yawon buɗe ido, da sauran muhimman fannoni. Amurka na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin wuraren da ‘yan Nijeriya s**a fi ziyarta, abin da ke nuna zurfin dangantaka mai tsawo tsakanin ƙasashen biyu.

“Yawancin ‘yan Nijeriya suna zuwa Amurka ne domin karatu, aiki, neman magani, ziyartar ‘yan'uwa, yawon buɗe ido, da damar zuba jari.

"Wannan mu’amala mai ƙarfi tana ci gaba da bunƙasa al’ummomin biyu.

"Sababbin abubuwan da Ofishin Jakadancin Amurka ya bayyana game da sauye-sauye a ayyukan ofishin jakadancin da hanyoyin neman bizar sun jima suna cikin labarai kwanan nan.

“Waɗannan sauye-sauyen, kamar yadda Ofishin Jakadancin Amurka ya bayyana, wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta bayar da sabis, ƙara saurin aiki, da mayar da martani ga sauye-sauyen buƙatun ayyukan jakadanci.”

Ministan ya yaba wa gwamnatin Amurka bisa ƙoƙarin yin bayani kai-tsaye ga ‘yan Nijeriya a wannan taro tare da tabbatar da samun sahihan bayanai na zamani ga kowa.

Haka kuma ya jaddada girmamawa da haɗin gwi

Peter Obi Donates N15m to Bauchi Health, Qur’anic Schools
08/08/2025

Peter Obi Donates N15m to Bauchi Health, Qur’anic Schools

Peter Obi, Presidential candidate of Labour Party (LP) in the 2023 presidential election has donated N15 million to Malikiya College of Nursing Sciences and Intisharu Taufizul Quranic School in Bauchi.Advertisement Obi made the donations to the two schools on Friday in Bauchi when he paid them a vis...

Shugaba Tinubu Ya Raba Naira Biliyan 493 Ga Gidajen Talakawa Miliyan 5 A Fadin Najeriya Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ...
08/08/2025

Shugaba Tinubu Ya Raba Naira Biliyan 493 Ga Gidajen Talakawa Miliyan 5 A Fadin Najeriya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya cire takunkumin da aka saka kan asusun Hukumar Shirin Zuba Jarin Jin Kai ta Ƙasa “National Social Investment Programme Agency (NSIPA)”, wanda ya kai ga sakin sama da Naira biliyan 493 domin tallafawa gidaje miliyan biyar a fadin ƙasar. Tun a ranar 8 ga Janairu, 2024 ne aka dakatar da Ministar Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Dr Betta Edu, tare da umartar Hukumar Yaƙi da Laifukan Tattalin Arziki da Kuɗi (EFCC) ta gudanar da bincike kan duk wasu harkokin kuɗi na ma’aikatar da hukumomin da ke karkashinta. Haka kuma, Shugaban Ƙasa ya kafa kwamiti karkashin jagorancin Ministan Kudi, Wale Edun, domin duba tsarin kuɗi na shirin jin kai da inganta shi don amfanin talakawa.

Karamin Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Dr Yusuf Sununu, ya bayyana farin cikinsa game da wannan mataki a taron manema labarai, inda ya ce gwamnatin tarayya na da kasafin kuɗi sama da Naira biliyan 500 da aka ware don aiwatar da shirye-shiryen tallafi kamar Shirin Ciyar da Dalibai a Makarantu na Ƙasa (National Homegrown School Feeding Programme), Shirin Ba da Kuɗi ga Talakawa (Conditional Cash Transfer), Shirin Ƙarfafa Matasa da Horas da su na N-Power, da kuma Tallafin Kuɗi ga Manoma (FarmerMoni). Ya ce umarnin Shugaban Ƙasa ya ba da damar bude asusun NSIPA don fara aiwatar da Shirin Tallafawa Ƙananan Ƙungiyoyi da Ƙarfafa Harkokin Kasuwanci “Government Enterprises and Empowerment Programme (GEEP)” da kuma wasu shirye-shirye masu muhimmanci.

Dr Sununu ya kara da cewa, ana shirin kaddamar da Tallafin Kuɗi ga Ƙungiyoyin da ke Cikin Ƙalubale “Grant for Vulnerable Groups (GVG)” a nan gaba kadan. Ya ce ma’aikatar ta dauki kamfanoni 53 da za su taimaka wajen sabunta rajistar NIN ga wadanda ke cikin “National Register” da ba su da lambar asusun banki, Lambar Shaidar Ƙasa (NIN) ko Lambar Tantancewar Asusun Banki (BVN), domin su samu damar amfana da tallafin gwamnati cikin gaggawa.

Gwamna Bala Muhammad ya buƙaci Peter Obi da ya dawo PDP Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya yi kira ga dan takarar s...
08/08/2025

Gwamna Bala Muhammad ya buƙaci Peter Obi da ya dawo PDP

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya yi kira ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, da ya koma jam’iyyar PDP domin hadin kan jam’iyyun adawa kafin zaben 2027.

PUNCH ta rawaito cewa Bala, wanda shi ne shugaban gwamnonin PDP, ya bayyana haka yayin da ya tarbi Obi a gidan gwamnati na Bauchi, inda ya ce dole ne jam’iyyun adawa su hada kai don fitar da tsari daya da zai ciyar da kasa gaba.

Peter Obi, a nasa bangaren, ya ce ziyararsa ta yi nufin tattaunawa da matasa a makarantu da kuma Almajirai, tare da yin kyautar N15m ga wasu makarantu biyu a jihar.

Ya kuma jaddada bukatar hadin kai tsakanin jam’iyyun siyasa domin kawo cigaba, ba wai kawai neman mulki ba.

NAHCON ta sanya N8.5 Miliyan a matsayin kuɗin aikin Hajji na 2026Hukumar kula da aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta ayyana ...
08/08/2025

NAHCON ta sanya N8.5 Miliyan a matsayin kuɗin aikin Hajji na 2026

Hukumar kula da aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta ayyana cewa kudin aikin Hajji na shekarar 2026 zai kasance Naira miliyan 8.5 a matsayin kuɗin da maniyyata za su fara ajiyewa.

A cewar sanarwar da Mataimakiyar Daraktar Sashen yaɗa Labarai ta NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta fitar, an bayyana kudin ne bayan taron bitar aikin Hajjin 2025 da aka yi tare da shugabanni da sakatarorin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi.

Ta ce za a daddale cikakken kuɗin aikin Hajji na badi bayan kammala tattaunawa kan dukkan kwangilolin ayyuka.

Usara ta kara da cewa Saudiyya ta sake bai wa Najeriya guraben alhazai 95,000 kamar yadda aka saba, kuma rabon kujeru ga hukumomin jin dadin alhazai na jihohi ya tsaya yadda yake a bara.

Ta rawaito Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, na gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa goyon bayansa ga alhazai da kuma hukumar.

GWAMNATIN TARAYYA ZA TA GINA LAYIN DOGO A TSAKIYAR BIRNIN KANO DA YA KAI NAIRA TIRILIYAN 1.5Gwamnatin Tarayya ta sanar d...
08/08/2025

GWAMNATIN TARAYYA ZA TA GINA LAYIN DOGO A TSAKIYAR BIRNIN KANO DA YA KAI NAIRA TIRILIYAN 1.5

Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin gina sabon layin dogon jirgin kasa na haske a cikin birnin Kano da kudinsa ya kai Naira tiriliyan 1.5. Shugaban Kwamitin Kidaya Kudin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai, Hon. Abubakar Kabir Abubakar (Bichi) ne ya bayyana hakan a tattaunawarsa da manema labarai a Kano. Ya ce wannan aiki zai rage matsalolin sufuri a cikin birnin Kano, inda ya kara da cewa irin wannan aikin ana ganinsa a kasashen Turai da yankin Asiya, kuma yana da matukar amfani wajen bunkasa tattalin arzikin jihar bayan kammalawa.

Hon. Bichi ya musanta rade-radin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya sanya ayyuka a Arewa, inda ya bayyana cewa shugaban kasa ya kaddamar da muhimman ayyuka a fannoni daban-daban kamar su gine-gine, lafiya, noma, ilimi da tsaro a yankin. Ya ce daga cikin ayyukan akwai aikin hanyar Kaduna–Zaria–Kano wanda ya kusa kammaluwa, da aikin Kaduna–Abuja mai tsawon kilomita 400 da aka sake bai wa wani kamfani wanda yanzu aikin ya fara tafiya cikin sauri, tare da burin kammala shi kafin karshen zangon farko na shekara mai zuwa. Haka kuma, akwai aikin hanyar Kano–Hadejia mai tsawon kilomita 200 da aka kammala, da kuma hanyar Kano Northern Bypass da ta kai sama da Naira biliyan 250.

Ya bayyana cewa ziyararsu a Kano ta yi daidai da taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC domin tsara dabarun samun nasara a zaben 2027. Ya tunatar da cewa a zaben 2023, Kano ta bai wa Shugaba Tinubu kuri’u sama da 500,000 — mafi girma a duk fadin kasar. Haka kuma, taron ya kasance na nuna goyon baya ga tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya samu nasarar sauya jihohin PDP da dama zuwa hannun APC.

GWAMNATIN TARAYYA ZA TA KAMMALA GYARAN ALAU DAM AKAN KUDI NAIRA BILIYAN 80 NAN DA 2027, DON INGANTA NOMAN RANI DA SAMAR ...
08/08/2025

GWAMNATIN TARAYYA ZA TA KAMMALA GYARAN ALAU DAM AKAN KUDI NAIRA BILIYAN 80 NAN DA 2027, DON INGANTA NOMAN RANI DA SAMAR WUTAR LANTARKI

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa aikin gyare-gyare da fadada Alau Dam da ke jihar Borno, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 80, zai kammala nan da shekarar 2027. Ministan Ruwa da Tsabtace Muhalli, Farfesa Joseph Utsev, ya bayyana haka ne a lokacin ziyarar aiki da ya kai wurin aikin a garin Alau, kusa da Maiduguri. Ya ce an fara aikin ne da amincewar Shugaba Bola Ahmed Tinubu karkashin shirin Renewed Hope Agenda, domin Dan din ya zama mai amfanarwa sosai, ciki har da ban ruwa don bunkasa noman rani da kuma shirin samar da wutar lantarki a nan gaba.

Ministan ya bayyana cewa aikin ya kasu kashi biyu, inda kashi na farko zai kare a watan Satumba na wannan shekara, domin rage hadarin ambaliyar ruwa a wannan damina. Kashi na biyu kuma zai fara a watan Oktoba kuma ya kammala a watan Maris 2027, wanda zai kai ga kammala sake ginawa da fadada Dam din. Ya ce, bayan kammala aikin, Dam din zai kara inganta samar da ruwan sha ga Maiduguri da kewaye, ya tallafa wa noman rani, tare da bai wa yankin damar samar da wutar lantarki ta hanyar ruwa.

Farfesa Utsev ya gode wa Shugaba Tinubu da Gwamna Babagana Umara Zulum bisa jajircewa wajen ganin aikin ya tabbata, yana kuma kira ga manoma a yankin su daina shuka amfanin gona a gefen Dam din domin kauce wa matsaloli yayin aikin. Ya kuma shawarci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu kan yiwuwar ambaliya, yana mai bayyana cewa aikin na da matuƙar muhimmanci wajen magance matsalolin ruwa da inganta harkokin noma a Borno da ma kasa baki daya.

Address

Kasuwar Kaji Azare
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katagum Dailypost posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katagum Dailypost:

Share