Katagum Dailypost

Katagum Dailypost Labarai Da Zarar Sun Faru...
(1)

Jirgin MaxAir Dauke Da Alhazan Jihar Nasarawa 560 Ya Taso Daga Jeddah Zuwa AbujaHukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sana...
03/06/2026

Jirgin MaxAir Dauke Da Alhazan Jihar Nasarawa 560 Ya Taso Daga Jeddah Zuwa Abuja

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar da cewa jirgin kamfanin MaxAir mai lamba NGL267 ya tashi daga birnin Jeddah na Kasar Saudiyya zuwa Abuja dauke da Alhazan Jihar Nasarawa guda 560.

Ana ci gaba da shirye-shiryen dawo da sauran alhazan Najeriya daga Kasar Saudiyya cikin tsari da kuma hadin gwiwar hukumomin da abin ya shafa domin tabbatar da tafiyar cikin nasara da aminci.

Jirgin farkon ya bar filin jirgin sama na Jidda da karfe 9:27 na safe agogon Saudiya.

Source: NAHCON Command and Control Center-Makkah.q

KUSAN JAGORORIN KU A KATAGUM DAILYPOST Umar Saleh Burra na daya daga cikin wakilan Katagum Dailypost masu himma wajen ta...
03/06/2026

KUSAN JAGORORIN KU A KATAGUM DAILYPOST

Umar Saleh Burra na daya daga cikin wakilan Katagum Dailypost masu himma wajen tattara labarai daga sassa daban-daban. Yana taka muhimmiyar rawa wajen kawo labarai masu inganci.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayar da umarnin gaggawa ga jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da su cire dukkanin allunan tal...
03/06/2026

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bayar da umarnin gaggawa ga jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da su cire dukkanin allunan talla, tutoci da fastocin kamfen da aka lika a kan fitilun t**i, sanduna da kuma manyan gadoji a birnin Bauchi da sauran manyan biranen jihar.

Umarnin ya fito ne daga haɗin gwiwar Hukumar Kula da Kayayyakin Gwamnati ta Jihar Bauchi (BASIDMA), Hukumar Tsare-tsaren Gine-gine da Ci gaban Birane (BSPPDB), Hukumar Kare Muhalli ta Jihar Bauchi (BASEPA) da kuma Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Bauchi (BAROTA), bayan wata ganawa da s**a yi da shugabannin jam’iyyun siyasa a jihar.

Da yake jawabi a madadin hukumomin, Shugaban BSPPDB, Town Planner Muhammad Ibrahim, ya bayyana cewa an bai wa jam’iyyun siyasa wa’adin mako guda, daga ranar 4 zuwa 11 ga Yuni, 2026, domin cire dukkanin fastoci da allunan talla da aka sanya a wuraren da dokoki s**a haramta.

Ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na inganta kyawun birane, tsaftace muhalli da kuma hana abubuwan da ka iya haddasa rikici a lokacin siyasa.

Muhammad Ibrahim ya yi gargadin cewa hukumomin da abin ya shafa za su cire duk wani talla ko fasta da aka bari bayan cikar wa’adin, tare da ɗaukar matakan doka kan masu karya ƙa’idojin.

Haka kuma, ya buƙaci ‘yan siyasa da al’umma gaba ɗaya su mutunta dokokin gine-gine da ka’idojin amfani da gefen hanya domin tabbatar da tsafta da tsaron muhalli.

Ya jaddada cewa kare muhalli da lafiyar jama’a hakki ne da ya rataya a wuyan kowa, yana mai cewa duk wanda aka samu da laifin karya dokokin zai fuskanci hukunci a gaban kotunan tafi-da-gidanka.

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta AikiGwamnatin Tarayya ta ɗauki...
03/06/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta Aiki

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki gabarar daidaita ayyukan hukumar yaƙi da kwararar hamada ta kasa, wato National Agency for the Great Green Wall (NAGGW), inda ta mayar da babban ofishinta na gudanar da ayyuka daga birnin tarayya Abuja zuwa jihar Kano.

Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ne ya bayyana hakan, inda ya bayyana cewa matakin na kunshe ne a karkashin tsarin 'Renewed Hope Agenda’ na Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Manufar hakan ita ce tallafa wa hukumar don ta gudanar da ayyukanta cikin hanzari da nagarta a jihohin da abin ya shafa.

Shirin na 'Great Green Wall' babban yunkuri ne na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da ya kunshi kasashe 11, da nufin yaki da kwararar hamada, lalacewar kasa, da kuma radadin sauyin yanayi a yankin Sahel da Sahara.

A nan Najeriya, shirin ya karkata ne a kan jihohi 11 na gaba-gaba da hamada ke barazana musamman ga rayuwarsu, wadanda s**a hada da: Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto, Yobe, Zamfara, da kuma Adamawa.

Ministan ya kara da cewa, babban burin hukumar shi ne shimfida dangar bishiyoyi (Green Wall) mai nisan kilomita 15 a fadi, da kuma tsawon kilomita 1,500 domin kare muhalli, rage radadin sauyin yanayi, samar da wadatar abinci, da kuma rage radadin talauci a karkara.

Tun lokacin da aka kaddamar da shirin a shekarar 2013, kafin daga bisani a mayar da shi cikakkiyar hukuma a 2015, an samu manyan nasarori k**ar haka:

Kafa dangar kariya daga iska da yashi (shelterbelts) fiye da guda 100.

Gina madatsun ruwa na sola da iskar gas guda 159 don samar da ruwan sha.

Daukar matasa guda 600 a matsayin dogaran daji (forest guards).

Samar da gonakin bishiyoyin itatuwa na (orchards and woodlots) guda 240 don bunkasa kudin shiga.

Malam Balarabe Abbas Lawal ya jaddada cewa, wannan sauyi zai magance kalubalen da hukumar ta dade tana fuskanta na gudanar da ayyuka daga ofishin haya a Abuja, wanda ke nesa da ainihin inda ayyukan suke a Arewa. Komawa Kano, wadda ita ce cibiyar yankunan da ayyukan s**a shafa, zai ba da damar sanya ido, da samar da kyakkyawar alaka tsakanin gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, da al'ummomin yankunansu.

Jihar Kano riga ta saba da irin wadannan ayyuka, domin tana dauke da ofishin tsara shirye-shiryen dashen bishiyoyi (APCU) tun a shekarar 1988, wanda yanzu ba a amfani da shi yadda ya k**ata tun bayan kammala shirin Bankin Duniya na dashen bishiyoyi a yankunan fari (Arid Zone Afforestation Programme) a shekarar 1996. Wannan cigaba a yanzu zai cigaba a hukumar ta NAGGW.

Daga karshe, Ministan ya bayyana yakinin cewa wannan mataki na kusanto da hukumomi kusa da inda suke aiki zai kawo sauyi na gaske ga rayuwar miliyoyin 'yan Najeriya da ke zaune a yankunan da kwararar hamada ke addaba.

KUSAN JAGORORIN KU A KATAGUM DAILYPOSTZaharadeen Mohammed Azare shi ne ke kula da tantancewa, gyarawa da tabbatar da ing...
03/06/2026

KUSAN JAGORORIN KU A KATAGUM DAILYPOST

Zaharadeen Mohammed Azare shi ne ke kula da tantancewa, gyarawa da tabbatar da ingancin labaran da ake wallafawa. Yana tabbatar da cewa masu karatu suna samun sahihan bayanai cikin tsari da ƙwarewa.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta bankado wata haramtacciyar masana’antar kera bindigogi a garin Potiskum tare da k**a ...
03/06/2026

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta bankado wata haramtacciyar masana’antar kera bindigogi a garin Potiskum tare da k**a mutane bakwai da ake zargi da hannu a harkar.

A wata sanarwa da Kakakin Rundunar, SP Dungus Abdulkarim ya fitar, ya bayyana cewa jami’an ‘yan sanda na Potiskum Area Command tare da hadin gwiwar ofishin ‘yan sanda na yankin sun gudanar da samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri.

Jami’an sun kai farmaki wani wajen aikin maƙera da ke Tasha Adua, kan t**in Danchuwa a Potiskum, inda s**a cafke mutane bakwai da ake zargi.

Kayayyakin da aka kwato sun hada da bindigogi biyu da aka ƙera a gida, bututun bindiga guda 24, gindin bindiga guda tara, tsofaffin bindigogin Baushe guda hudu da ba sa aiki, injin goge ƙarfe guda ɗaya da kuma adda guda ɗaya.

Rundunar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi kan wadanda aka k**a domin gano sauran masu hannu a lamarin, masu sayen mak**an da kuma manufar amfani da su.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Yobe, CP Usman Kanfani Jibrin, ya umarci jami’an da ke binciken lamarin da su ƙara himma wajen gano sauran wuraren da ake kera mak**ai ba bisa ka’ida ba tare da tantance barazanar tsaron da irin wadannan ayyuka ke haifarwa.

Rundunar ta kuma gargadi al’umma da kada su bari a yi amfani da gidajensu ko wurarensu wajen gudanar da haramtattun ayyuka, musamman kera mak**ai.

Haka kuma ta bukaci mazauna jihar da su kasance masu lura tare da gaggauta kai rahoton duk wani motsi ko aiki da ke haifar da zargi ga hukumomin tsaro mafi kusa da su.

JIYA BA YAU BA: Lokacin da Marigayi Mai Martaba Sarkin Katagum Alh. Umaru Farouk ya halarci bude makarantar Islamiyya ta...
03/06/2026

JIYA BA YAU BA: Lokacin da Marigayi Mai Martaba Sarkin Katagum Alh. Umaru Farouk ya halarci bude makarantar Islamiyya ta Kantin-Gyada wanda yanzu aka fi sani da Markaz 1967.

Allah ya jikan magabatan mu.

FCE Jama’are Welcomes New Provost, Dr. Yahuza Ishaq Mohammed
03/06/2026

FCE Jama’are Welcomes New Provost, Dr. Yahuza Ishaq Mohammed

The Federal College of Education (FCE), Jama’are, Bauchi State, has welcomed Dr. Yahuza Ishaq Mohammed as its second substantive Provost following his formal assumption of office. Dr. Mohammed officially took over the leadership of the institution from Dr. Abraham Yusuf Gana, who served as the Col...

Teenager Arrested Over Alleged Drowning of 17-Year-Old in Bauchi
03/06/2026

Teenager Arrested Over Alleged Drowning of 17-Year-Old in Bauchi

The Bauchi State Police Command has commenced an investigation into a suspected culpable homicide case following the alleged drowning of a 17-year-old boy in Kari Village, Darazo Local Government Area. According to a statement issued by the Police Public Relations Officer, SP Nafiu Habib, the incide...

Wani mai neman takarar kujerar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar mazabar Ningi/Warji a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, Khalid Bar...
03/06/2026

Wani mai neman takarar kujerar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar mazabar Ningi/Warji a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, Khalid Barau, ya bayyana cewa idan aka zaɓe shi, abin da zai fi mayar da hankali a kai shi ne kyakkyawar wakilci da gudanar da mulki, ba raba kuɗaɗe don ɗaurin aure ko bikin suna ba.

Barau ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a tashar talabijin ta S24, inda aka wallafa wani ɓangare na hirar a shafinsa na Facebook a ranar Talata.

Dan takarar ya ce yawaitar tsammanin da ake yi wa ‘yan majalisa na ba da tallafin kuɗi don bukukuwan aure da na suna yana karkatar da hankalinsu daga ainihin nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora musu.

A cewarsa, ya k**ata a riƙa auna nasarar ‘yan majalisa ne ta yadda suke kawo ci gaba, samar da dokoki masu amfani ga jama’a, da kuma inganta rayuwar al’umma ta hanyar kyakkyawan shugabanci.

Ya ce: “Kun zaɓe ni ne domin in samar da dokokin da za su ƙarfafa shugabanci da ci gaban al’umma, ba domin in mayar da hankali wajen tallafa wa bukukuwan aure ko suna ba.”

Ya ƙara da cewa: “Idan na je Majalisar Tarayya, ba na sa ran mutanena za su zo suna gaya min maganar bukukuwa. Ina sa ran za su gaya min babu wutar lantarki, babu ruwa, babu hanyoyi, babu cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko, babu makarantu. Wannan shi ne abin da nake tsammani.”

Barau ya bayyana cewa tsawon shekaru ‘yan siyasa suna “amfani da talauci a matsayin makami” ta hanyar sa mutane su dogara da tallafin hannu, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da ƙoƙarin sauya yadda mutane ke kallon siyasa da shugabanci.

Ya ce: “Zan ci gaba da ƙoƙarin sauya tunanin mutane da yadda suke kallon siyasa. Ba zan taɓa gajiyawa da wannan ƙoƙari ba.”

Da yake magana kan shigar matasa da mata cikin harkokin mulki, Barau ya ce har yanzu ana amfani da su ne wajen yaƙin neman zaɓe da tara magoya baya, maimakon ba su damar jagoranci mai ma’ana.

Ya ce: “Ana amfani da su ne wajen yaƙin neman zaɓe.”
Ya kuma bayyana cewa idan aka ba matasa dama, za su iya bayar da kyakkyawan shugabanci.

A cewarsa: “Na yi imani cewa tsarata idan aka ba ta dama, za ta kasance ɗaya daga cikin mafi kyawun tsararraki. Muna da matasa masu ƙwazo da buri, amma buri daban yake da hangen nesa.”

Sai dai ya lura cewa da zarar matasa sun shiga cikin tsarin siyasa, da yawa daga cikinsu kan rungumi irin tsohuwar al’adar siyasar da suke son canzawa. Don haka ya ce dole ne a samar da damammaki na musamman ga sabbin shugabanni masu tasowa.

Ya kuma yaba wa wasu matasan ‘yan siyasa daga Arewa da ya ce suna gudanar da aiki mai kyau, musamman waɗanda ke tallafawa ilimi da bunƙasa rayuwar jama’a.

Game da ilimi kuwa, Barau ya bayyana cewa a halin yanzu yana bayar da tallafin karatu ga ɗaliban da ke karatu a makarantun gwamnati, kuma zai ci gaba da yin hakan idan aka zaɓe shi.

Ya ce: “A yanzu haka ina bayar da tallafin karatu da sauran taimakon ilimi ga ɗaliban da ke karatu a cibiyoyin gwamnati a Najeriya. Amma idan kana makaranta mai zaman kanta, ba na bayar da irin wannan tallafi.”

A ƙarshe, Barau ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su rika haskaka matasan ‘yan siyasa masu kyakkyawan aiki domin su zama abin koyi ga al’umma tare da ƙarfafa gyare-gyare da ɗaukar alhaki.

Ya ce: “Kafafen yaɗa labarai za su iya taimakawa wajen samar da zaman lafiya da haɗin kai ta hanyar nuna matasa shugabanni masu nagarta. Ya k**ata su zama fuskar kyakkyawar siyasa da irin gyaran da Arewa ke buƙata.”

Address

Kasuwar Kaji Azare
Bauchi

Telephone

+2347086806558

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katagum Dailypost posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katagum Dailypost:

Share