One News Hausa

One News Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from One News Hausa, Media/News Company, Bauchi.
(4)

ONE NEWS HAUSA Jarida ce dake kawo muku labarai da ɗumi-ɗumi gami da rahotannin gida da na waje a cikin harshen Hausa, daga Kamfanin 5STARS MEDIA PRODUCTION.

-Aikin mu domin al'umma ne.
-Burinmu kasancewa ji da ganin al'umma.

Sheikh Kabiru Gombe ya zama sabon Modibbon Lau.Magirma Hakimin Lau, Alh Abdullahi Ibrahim na chindo, ya naɗa babban saka...
13/08/2025

Sheikh Kabiru Gombe ya zama sabon Modibbon Lau.

Magirma Hakimin Lau, Alh Abdullahi Ibrahim na chindo, ya naɗa babban sakataren Jibwis sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe, a matsayin ‘MODIBBON LAU’ .

A madadin ƙungiyar Izala, muna taya shi murna tare da addu’an Allah bashi ikon sauke nauyin da aka ɗora masa. Amin

Jibwis Nigeria

"Arewa tana matuƙar jin daɗin salon mulkin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi."—Inji Daniel Bwala, hadimin shugaba...
13/08/2025

"Arewa tana matuƙar jin daɗin salon mulkin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi."

—Inji Daniel Bwala, hadimin shugaba Tinubu.

Me Zaku Ce?

Jami'ar Wudil ta yi Allah-wadai da ɗaliban da s**a yi bikin "Ranar Cikin Ƙarya" wato 'Fake Pregnancy Day'Jami’ar Kimiyya...
13/08/2025

Jami'ar Wudil ta yi Allah-wadai da ɗaliban da s**a yi bikin "Ranar Cikin Ƙarya" wato 'Fake Pregnancy Day'

Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano ta yi Allah-wadai da mummunar dabiʼar da wasu ɗalibai mata s**a yi da sunan ʼRanar Cikin Karyaʼ wato “Fake Pregnancy Day” ba tare da izini ba.

Shugaban sashen kula da harkokin dalibai na jami’ar, Farfesa Abdulkadir Muhammad Dambazau, ne ya bayyana haka a wata sanarwar da ya fitar a ranar Laraba 13 ga Agusta 2025.

Sanarwar ta ce wannan abin ya saba ka’idojin ɗabi’ar dalibai kuma ya sabawa ƙa’idojin jami’ar, tare da jawo wa makarantar mummunar illa da ɓata suna da martabarta.

Ta kuma ce jami’ar za ta gano duk wanda ya shirya ko ya taka rawa a wannan abin, tare da ɗaukar matakin ladabtarwa.

Jami’ar ta kuma yi kira ga dukkan dalibai da su kasance jakadu nagari na jami’ar, tare da neman izini kafin gudanar da kowanne irin aiki a nan gaba.

📸 - Arewa Updates

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Tarayya ta sanar da haramta sake ƙirƙirar sabbin jami'o'i, har tsawon shekaru bakwai masu zuwaHa...
13/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Tarayya ta sanar da haramta sake ƙirƙirar sabbin jami'o'i, har tsawon shekaru bakwai masu zuwa

Haramcin ya ƙunshi ƙirƙirar sabbin jami'o'in gwamnatin tarayya, kwalejojin kimiyya da fasaha na gwamnatin Tarayya da kuma kwalejojin ilimi na gwamnatin Tarayya

Ministan Ilimi , Dr. Tunji Alausa ne ya bayyana a majalisar zartarwa wadda Tinubu ya jagoranta a yau Laraba ita ce ta amince da wannan ƙudurin.

ZIYARAR ƘUNGIYAR IZALAHHukumar Tsaro ta Civil Defence ta Jihar Bauchi ta Ziyarci Kungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah wa Iq...
13/08/2025

ZIYARAR ƘUNGIYAR IZALAH

Hukumar Tsaro ta Civil Defence ta Jihar Bauchi ta Ziyarci Kungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah wa Iqamatis Sunnah reshen jihar Bauchi domin haɗin kai wajen yaki da fataucin yara.

-JIBWIS Bauchi State

FARASHIN KAYAN AMFANIN GONA A KASUWAR MAƘARFI – YAU 13/08/2025Masara:Mai aure – ₦32,000 ➡ ₦38,000Mara aure – ₦30,000 ➡ ₦...
13/08/2025

FARASHIN KAYAN AMFANIN GONA A KASUWAR MAƘARFI – YAU 13/08/2025

Masara:
Mai aure – ₦32,000 ➡ ₦38,000
Mara aure – ₦30,000 ➡ ₦34,000

Dawa:
Dawa (g/corn) – ₦32,000 ➡ ₦35,000
Dawa fara – ₦32,000 ➡ ₦35,000

Wake:
Fari manya – ₦70,000 ➡ ₦85,000
Fari ƙanana – ₦70,000 ➡ ₦75,000
Suya silba – ₦70,000 ➡ ₦78,000
Suya idon fara – ₦65,000 ➡ ₦70,000
Suya zafa – ₦68,000 ➡ ₦70,000

Shinkafa:
2BC – ₦33,000 ➡ ₦35,000
Jamila – ₦38,000 ➡ ₦40,000
Tsaba ta tuwo – ₦90,000 ➡ ₦100,000
Ta dafawa – ₦100,000 ➡ ₦115,000

Kalwa:
Babban buhu – ₦145,000 ➡ ₦150,000
Ƙaramin buhu – ₦120,000

Barkono:
Ɗan zagade – ₦30,000 ➡ ₦40,000
Ban-ruwa – ₦35,000 ➡ ₦55,000
Kimba – ₦45,000 ➡ ₦60,000
Daurin Lagos – ₦65,000 ➡ ₦80,000 (ya danganta da inganci)

Rogo:
Babban buhu – ₦40,000 ➡ ₦50,000
Ƙaramin buhu – ₦20,000 ➡ ₦25,000

Tumatir bushasshe:
Ƴar Zariya – ₦65,000 ➡ ₦85,000
Ƴar Gamawa – ₦35,000 ➡ ₦45,000
Ƴar Gashuwa – ₦45,000 ➡ ₦50,000

Albasa:
Mai kwara – ₦45,000 ➡ ₦55,000
Yaska – ₦40,000 ➡ ₦50,000
Mai kwara sabuwa – ₦20,000 ➡ ₦25,000
Yaska sabuwa – ₦12,000 ➡ ₦20,000

Tsamiya:
Buhun s**ari – ₦88,000
Buhun masara – ₦150,000
Buhun siminti – ₦60,000

Dankali & Sauran Kayayyaki:
Dankalin Hausa – ₦35,000 ➡ ₦40,000
Walahan gwaza – ₦26,000

Zobo:
Flower – ₦20,000
Gari – ₦40,000

Idan kana buƙatar siye ko sayar da kayan gona kai tsaye daga kasuwar Maƙarfi, tuntuɓi: 0813 103 6034

Takaddama a Ringim: An Zargi Mahukunta a Ƙaramar Hukumar Ringim ta jahar Jigawa da Tauye ’Yancin Matasan Garin—Daga; Mls...
13/08/2025

Takaddama a Ringim: An Zargi Mahukunta a Ƙaramar Hukumar Ringim ta jahar Jigawa da Tauye ’Yancin Matasan Garin

—Daga; Mls. Alasan Maikifi Ringim

A Ƙaramar Hukumar Ringim, wani rikici ya kunno kai bayan rahotanni sun nuna an hana matasa damar bayyana ra’ayoyinsu da korafe-korafensu a gaban jami’an gwamnati a yayin taron hadin gwiwa da al’umma.

Matasan sun bayyana matakin a matsayin take hakkin ’dan kasa, tare da zargin cewa ana kokarin murkushe muryar masu adawa da manufofin gwamnati.

A cewar su, za su fito karara a sabon gangami da za a gudanar a ranar 30 ga Agusta, 2025, bayan ziyarar mai girma gwamna, domin wayar da kan duniya cewa ba za su lamunci keta musu ’yanci ba.

Sun yi kira ga Ƙungiyoyin Kare Hakkin ’dan Adam da sauran al’umma da su mara musu baya wajen tabbatar da adalci da kare dimokuraɗiyya a Ringim.

Addinin Musulunci Zai Samu Cikas Idan Musulmi S**a Bari Tinubu Ya Fadi A zaben Shekarar 2027 — Sheikh Yahaya Jingir.A wa...
13/08/2025

Addinin Musulunci Zai Samu Cikas Idan Musulmi S**a Bari Tinubu Ya Fadi A zaben Shekarar 2027 — Sheikh Yahaya Jingir.

A wani faifan bidiyo da ya yadu sosai, jagoran ƙungiyar Izala, Sheikh Yahaya Jingir, ya roƙi Musulmin Najeriya da su ba da goyon baya ga Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027. A cewarsa, barin Tinubu ya sha kaye ba wai siyasa kaɗai zai shafa ba, har ma zai shafi addini.

Sheikh Jingir ya bayyana cewa shi kansa zai kaɗa kuri’a ga Tinubu, tare da kira ga dukkan Musulmi da su yi haka. Ya gargadi cewa Musulunci na iya samun koma baya idan al’ummar Musulmi ba su tabbatar da nasarar Tinubu ba.

Maganganunsa sun haifar da cece-kuce a shafukan sada zumunta, inda wasu s**a yarda da shi, wasu kuma s**a soki haɗa addini da tallata ‘yan siyasa.

Meye ra'ayin ku?

Addinin Musulunci Zai Samu koma Baya idan Al'ummar Musulmai S**a Bari Bola Tinubu ya faɗi Zaɓe a 2027 — Inji Sheikh Yaha...
13/08/2025

Addinin Musulunci Zai Samu koma Baya idan Al'ummar Musulmai S**a Bari Bola Tinubu ya faɗi Zaɓe a 2027 — Inji Sheikh Yahaya Jingir.

A wani faifan bidiyo da ya yadu sosai, jagoran ƙungiyar Izala, Sheikh Yahaya Jingir, ya roƙi Musulmin Najeriya da su ba da goyon baya ga Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027. A cewarsa, barin Tinubu ya sha kaye ba wai siyasa kaɗai zai shafa ba, har ma zai shafi addini.

Sheikh Jingir ya bayyana cewa shi kansa zai kaɗa kuri’a ga Tinubu, tare da kira ga dukkan Musulmi da su yi haka. Ya gargadi cewa Musulunci na iya samun koma baya idan al’ummar Musulmi ba su tabbatar da nasarar Tinubu ba.

Maganganunsa sun haifar da cece-kuce a shafukan sada zumunta, inda wasu s**a yarda da shi, wasu kuma s**a soki haɗa addini da tallata ‘yan siyasa.

Meye ra'ayin ku?

Duk Hannun da ya Ƙirga Riba; Dole Wataran Zai Ƙirga Faɗuwa.Mun roƙi Allah kuma Ya amsa, Ya kawo mana saukin kayan abinci...
13/08/2025

Duk Hannun da ya Ƙirga Riba; Dole Wataran Zai Ƙirga Faɗuwa.

Mun roƙi Allah kuma Ya amsa, Ya kawo mana saukin kayan abinci, saura mu gode masa bisa wannan ni'imar.

Alhamdulillah.

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Ta Bada Kuɗi Naira Miliyan 14.3 Wa Makarantar Abubakar Tatari Polytechnic Don Tallafa Wa Dalibai...
13/08/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Ta Bada Kuɗi Naira Miliyan 14.3 Wa Makarantar Abubakar Tatari Polytechnic Don Tallafa Wa Dalibai 289

Abubakar Tatari Polytechnic da ke Jihar Bauchi ta bayyana cewa ta samu tallafin kudi na Naira 14,379,211 daga Asusun Tallafin Dalibai na Kasa (NELFUND) domin biyan kudin makaranta na dalibai 289 da ke karatu a zangon shekarar 2024/2025.

Rejistaran makarantar, Lawal Sambo, ne ya bayyana hakan a cikin wata takarda da ya aikawa Shugaba kuma Babban Daraktan NELFUND, inda ya nuna cewa wannan tallafi zai taimaka wajen rage wa dalibai nauyin biyan kudin makaranta tare da basu damar ci gaba da karatunsu ba tare da tangarda ba.

Ya yaba da wannan taimako daga NELFUND, yana mai cewa ya dace dalibai su ci gaba da yin amfani da damar da gwamnati ta samar don tabbatar da cewa ilimi ya kasance abin samu ga kowa da kowa. Ya kara da cewa makarantar na fatan ci gaba da hadin gwiwa da NELFUND wajen inganta walwalar dalibai a nan gaba.

A Najeriya ne kawai har yanzu ake alakanta duk wani abu da ya danganci Imamu Hussain (as) da Shi’anci. Da zarar mutum ya...
13/08/2025

A Najeriya ne kawai har yanzu ake alakanta duk wani abu da ya danganci Imamu Hussain (as) da Shi’anci. Da zarar mutum ya je Karbala sai a kira shi dan Shia.

Amma a zahirin gaskiya akwai wadanda ba Shia ba ne amma su na zuwa ziyara Haramin Imam Hussain (as) duk shekara, wasu ma ba Musulmi ba ne karewar ta. Wasu ma ba su yarda da addini ba kwata-kwata.

Amma baki daya sun yarda da sadaukarwar sa, da tasirin sauyin da ya samar a tarihi, sannan su na kallon sa a matsayin wani jigo kuma madubin dubawa wajen yaki da zalunci da tabbatar da adalci.

Kusan duk wata gwagwarmayar kawo sauyi da kawar da zalunci ta na jingina kan ta da ‘saura’ irin na Imam Hussain (as). Al’amarin Aba Abdullahil Hussain ya shallake duk wani shinge da yake katange al’umma.

Sauyin da Imam (as) ya samar wata makaranta ce mai zaman kan ta, kowa ya na shiga ya koyi abun da zai koya ya fita, ya bar saura. Kuma ta kowacce fuska ta rayuwa ka duba, to al’amarin Imam Hussain (as) ya na nan! Rashin wayewa ne zai sa mutum ya iyakance al’amarin Imam Hussain (as) da Shi’anci kawai.

Hoton da ke kasa shugaban kasar India ne, Narendra Modi da kuma (tsohon Shugaban) Pakistan, Imran Khan- ke jaddada jinjina ga Imam Hussain (as)- (kar mu manta, Narendra ba Musulmi ba ne). Daya hoton kuma jikan Nelson Mandela ne, Mandla Mandela a wata ziyara da ya kai Karbala.

Al’amarin Imam Hussain (as) al’amari ne na duniya baki daya (global phenomenon). Kuma zai ci gaba da habaka ne har sai wannan sakon ya mamaye dukkan duniya baki daya Inshaa Allah!

—Daga Dr. Najeeb Maigatari

Me Zaku Ce?

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when One News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to One News Hausa:

Share