One News Hausa

One News Hausa DOMIN TALLATA:
Kasuwancin Ku
Ra'ayoyinku
Korafi ga yan Siyasa

08064672794 (WhatsApp Only)
(3)

ONE NEWS HAUSA Jarida ce dake kawo muku labarai da ɗumi-ɗumi gami da rahotannin gida da na waje a cikin harshen Hausa, ƙarƙashin Kamfanin 5STARS MEDIA PRODUCTION.

09/09/2025

"Ban yadda komai lalacewar Musulmi yafi wanda ba Musulmi ba" —Sheikh Nuru Khalid

WATA SABUWA: Ganduje ko mabiya masu idanu bashi dasu ballantana makafi irin na Kwankwaso - Sheik Ibrahim Khalil
09/09/2025

WATA SABUWA:

Ganduje ko mabiya masu idanu bashi dasu ballantana makafi irin na Kwankwaso - Sheik Ibrahim Khalil

DA ƊUMI-ƊUMI FiraMinistan Nepal, Khadga Prasad Sharma Oli, ya yi murabus kwana guda bayan zanga-zangar da ta yi sanadiyy...
09/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI

FiraMinistan Nepal, Khadga Prasad Sharma Oli, ya yi murabus kwana guda bayan zanga-zangar da ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 19 kan zargin cin hanci da rashawa a gwamnatin sa.

Najeriya Ina Mafita?

One News Hausa
0 9 — 0 9 — 2 0 2 5

Melaye ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kasance ta gidan talabijin na ARISE a ranar Litinin, inda ya zargi gwamnati d...
09/09/2025

Melaye ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kasance ta gidan talabijin na ARISE a ranar Litinin, inda ya zargi gwamnati da jefa ‘yan Najeriya cikin mummunar yunwa duk da samun bilyoyin daloli ta hanyar rance.

Ya ce: “Akwai mummunar yunwa a ƙasar nan. Me ya sa shugaban ƙasa zai karbo rancen dala biliyan 1.7 daga Babban Bankin Duniya? Me ya sa majalisar dattawa ta amince da rancen dala biliyan 21 zuwa yanzu, tare da wasu da dama da ake jiran amincewa?”

Ya ƙara da cewa: “Wannan gwamnati na daga cikin gwamnatoci mafi sakarci a tarihin ƙasar nan. Shugaban ƙasa da ya ce ya zo domin rage ɓarnar kuɗi ya sayi jirgin ruwa. Wannan jirgin da ya siya ba ta taɓa zuwa cikin iyakokin ruwa na Najeriya ba—tana yawo ne tsakanin Monaco da Paris. To, me muke buƙatar jirgin ruwa da zai ciwo mana kuɗi a lokacin da ake fama da talauci da yunwa?”

Melaye ya ce: “Tinubu ya karbo rance fiye da duk wani shugaban ƙasa a tarihin Najeriya. Idan ana samun ƙarin kuɗi, to me ya sa ake ta rance? Ba za mu yi mamaki ba idan shugaban ƙasa ya fara neman rance daga Opay da Moniepoint nan gaba kaɗan", kamar yadda Albarka Radio ta Naƙalto.

Najeriya Ina Mafita?

One News Hausa
0 9 — 0 9 — 2 0 2 5

Ƙorafin Canjin Miji Bayan Aure Yawancin mata suna cewa: “Mijina ya canza tun bayan da muka yi aure, ba irin yadda yake d...
09/09/2025

Ƙorafin Canjin Miji Bayan Aure

Yawancin mata suna cewa: “Mijina ya canza tun bayan da muka yi aure, ba irin yadda yake da ni kafin aure ba.” Amma gaskiya ita ce, sau da yawa ita matar ma ta canza ba tare da ta lura ba.

Da farko kafin aure, miji ya saba zuwa ya same ki a gida cikin tsafta, sanye da kaya masu kyau, ƙamshi yana tashi, kin yi ado kin yi shigar mace ta musamman. Amma bayan aure, musamman bayan haihuwa, abubuwa suna sauyawa.
• Adon da kika saba yi, sai ya ragu.
• Tsafta ta gida sai ta fara samun matsala saboda gajiya ko sakaci.
• Kiran suna mai daɗi da kika saba yi masa kafin aure (“Honey, Sweetheart, Ango na”) sai ya canza zuwa “Kai”, ko kuma kawai idan kina buƙatar kuɗi.
• A maimakon murmushi da nishaɗi, kullum sai kuka da korafin “ba kudi, ba wane abu, ba wane abu.”

A hankali, miji ma yana jin kamar abubuwa sun canza a wurin ki. Idan ya rasa nishaɗi, tsafta, da kulawar da ya saba samu a wurin ki, ba abin mamaki bane idan shima ya sauya halayya ko kuma ya rage ƙoƙarinsa.

Mata na da muhimmiyar rawa wajen riƙe da gidan aure. Eh, gaskiya akwai wahalar haihuwa, akwai gajiya, akwai rashin kuɗi, amma idan mace ta yi ƙoƙari ta kiyaye tsafta, ta ci gaba da nuna soyayya da mutunci, aure yakan yi daɗi sosai.

Miji baya buƙatar abu mai tsada kullum, wani lokaci kalaman kirki, kallo da murmushi, da ɗan shigar ado mai kyau, shi kaɗai ya isa ya sa zuciyarsa ta huce.

Idan kina so mijinki ya kasance kamar yadda yake kafin aure, to ke ma ki ci gaba da kasancewa irin matar da ya gani kafin aure. Aure ba ya tafiya da soyayya kawai; yana tafiya da ƙoƙari, fahimta, da kula da juna.

A ƙarshe: Mata ku daina sa ran mijin ku ya kasance cikakke, ku ma ku yi ƙoƙarin zama cikakkun abokan tafiyarsa. Idan kowa ya gyara nasa gefe, gida ya kan zauna lafiya.

—Rubutun; Maryam Ibrahim Bununu

Muna son Mafi Karacin Albashi Ya Tashi Daga 70k Ya koma duhu 350 ko 500 A Najeriya, cewar Ma'aikatan 'Yan Kwadagon Najer...
09/09/2025

Muna son Mafi Karacin Albashi Ya Tashi Daga 70k Ya koma duhu 350 ko 500 A Najeriya, cewar Ma'aikatan 'Yan Kwadagon Najeriya.

Sakataren tsare-tsare na Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya, NLC, Kwamared Nasir Kabir ne ya yi wannan kira a hirarsa da BBC inda ya ce albashi mafi ƙanƙanta na naira dubu 70 ba ya wadatar da ƙaramin ma’aikaci.

Najeriya Ina Mafita?

One News Hausa
0 9 — 0 9 — 2 0 2 5

TUC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 14 Kan Janye Harajin Mai na Kashi 5%Kungiyar Ƙwadago ta Najeriya (TUC) ta ...
09/09/2025

TUC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 14 Kan Janye Harajin Mai na Kashi 5%

Kungiyar Ƙwadago ta Najeriya (TUC) ta bayyana adawarta da shirin Gwamnatin Tarayya na ƙara harajin kashi 5% akan mai, tana mai bayyana matakin a matsayin wata babbar barazana ga tattalin arzikin ƙasa da jin daɗin 'yan ƙasa.

A wata sanarwa da shugabancin kungiyar ya fitar, TUC ta ce shirin ƙara harajin zai ƙara wa talaka nauyi, duba da yadda hauhawar farashin kayayyaki da matsin rayuwa ke ci gaba da addabar 'yan Najeriya. Kungiyar ta ce wannan ƙara haraji zai shafi dukkan ɓangarorin rayuwa – daga sufuri, abinci, zuwa kayayyakin masarufi.

TUC ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta janye wannan mataki cikin kwanaki 14, tana mai gargadi cewa rashin janye wannan haraji zai tilasta mata ɗaukar matakin da ya dace, wanda ka iya haɗa da tafiya yajin aiki ko zanga-zanga.

“Bai kamata gwamnati ta ƙara wa jama’a nauyi a irin wannan lokaci mai wuya ba. Maimakon ƙarin haraji, ya kamata a mayar da hankali wajen rage ɓarna da satar kudaden gwamnati,” in ji TUC a cikin sanarwar.

Har zuwa yanzu, Gwamnatin Tarayya ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da wannan gargaɗi daga TUC, sai dai ana sa ran za a samu martani a cikin kwanakin nan.

—Ahmed Tijjani Ramalan

In Zaku Bani Har Ƙarshe Wa'adin Mulkin Tinubu, 2027 Bazan Janye Kalamai na ba” — Sowere ga DSS’Yan Sanda na farin kaya w...
09/09/2025

In Zaku Bani Har Ƙarshe Wa'adin Mulkin Tinubu, 2027 Bazan Janye Kalamai na ba”
— Sowere ga DSS

’Yan Sanda na farin kaya wato DSS sun baiwa Sowore wa’adin mako guda ya janye kalaman da ya yi na s**ar Shugaba Tinubu, inda s**a ce sun bashi wa'adin mako guda.

Sai dai Omoyele Sowore ya ce ba gudu ba ja da baya ko zai mutu bazai janye kalaman nasa ba domin bai aikata laifi ba akan kalaman.

“Ko da kun bani wa’adi har zuwa karshen wa’adin mulkin Tinubu a 2027, ba zan janye kalaman da na yi ba.”

—Daga Ahmed Tijjani Ramalan

Najeriya Ina Mafita?

One News Hausa
0 9— 0 9 — 2 0 2 5

“Idan munafukai zasu kwana 1,000 suna fadawa Kwankwaso laifina, sai dai kawai ya kalle su. Nima haka, ba a kawo min muna...
08/09/2025

“Idan munafukai zasu kwana 1,000 suna fadawa Kwankwaso laifina, sai dai kawai ya kalle su. Nima haka, ba a kawo min munafincin Madugu, kuma ko anyi munafincin sai ya fada min, nima sai na fada masa. Kaga kenan an yi ba a yi ba.”

— A cewar Gwamnan Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf

Me Zaku Ce?

One News Hausa
0 8 — 0 9 — 2 0 2 5

08/09/2025

KA JI RABO: Shahararren Malamin Izala Sheikh Nuru Khalid ya Gabatar da Jawabin Haɗin Kai a wajen Taron 'Ƴan Shi'a A Abuja

Sheikh Nuru Khalid ya shahara wajen kokarin haɗin kan al’umma a Najeriya, a yau ya gabatar da jawabi ne kan "Muhimmanci Haɗin Kai Da Baiwa Juna Uzuri" a wajen taron makon Haɗin Kai wanda Harƙar Musulunci ƙarƙashin Sheikh Zakzaky s**a shirya a Abuja.

Me Zaku Ce?

One News Hausa
0 8 — 0 9 — 2 0 2 5

Kansila mai wakiltar unguwar Kinkiba a ƙaramar hukumar Soba, jihar Kaduna, Sunusi Hashim, ya naɗa masu ba shi shawara na...
08/09/2025

Kansila mai wakiltar unguwar Kinkiba a ƙaramar hukumar Soba, jihar Kaduna, Sunusi Hashim, ya naɗa masu ba shi shawara na musamman 18 don ƙarfafa harkokin mulki a matakin ƙasa-ƙasa.

An rantsar da waɗannan sabbin masu ba da shawara a ranar Lahadi, a bikin da aka gudanar a makarantar firamare ta L.E.A Kinkiba, tare da halartar jagororin jam’iyyar APC, sarakunan gargajiya, shugabannin addini da al’umma.

Hashim ya bayyana cewa an zaɓi waɗanda aka naɗa ne saboda aminci da jajircewarsu wajen bunƙasa unguwar Kinkiba, ya kuma yi kira gare su da su yi aiki da gaskiya, mutunci, da tausayi ga jama’a.

Ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa tallafin da yake bayarwa ga ’yan majalisa a fadin jihar, musamman samar da taki ga manoma, tare da alkawarin cewa tawagarsa za ta yi aiki tare da gwamnan don bunƙasa al’umma da raya jam’iyya.

Me Zaku Ce?

One News Hausa
0 8 — 0 9 — 2 0 2 5

"Duk abun da muka ce zamu yi da gaske muke yin shi. Lokacin da muka ce zamu yaƙi ƴan ta’adda mun yaƙe su da karfin mu, y...
08/09/2025

"Duk abun da muka ce zamu yi da gaske muke yin shi. Lokacin da muka ce zamu yaƙi ƴan ta’adda mun yaƙe su da karfin mu, yanzu kuma tunda sun ji wuta sun nemi ayi Sulhu, to zamu yi sulhu, amma na tsakani da Allah." —Cewar Gwamna Dikko Radda.

Gwamna ya ƙara da jaddada cewa, za su taimaka ma waɗanda Ta'addancin ya shafa, sannan za su taimaki waɗanda s**a yadda aka yi sulhun da su.

Gwamna Radda ya ci gaba da bayyana cewar yanzu haka ya kafa Komiti da zai duba ɓarnar da yan ta'adda s**a yi a wasu Kananan hukumomin, sannan za su duba makarantu da asibitocin da za su fara gyarawa.

Najeriya Ina Mafita?

One News Hausa
0 8 — 0 9 — 2 0 2 5

Address

Federal Low Cost Housing Estate, Bauchi
Bauchi
740102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when One News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to One News Hausa:

Share