09/08/2026
Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuh.
Manzon Allah ﷺ ya hana yaɗa jita-jita da kuma faɗin abin da ba a tabbatar da gaskiyarsa ba.
Don haka, mene ne manufarku ta yaɗa cewa an kai wani malami gidan yari? Wace hujja sahihiya kuke da ita kan wannan iƙirari?
Idan da gaske ne, ku bayyana mana:
• Wane laifi ne ake zarginsa da aikatawa?
• A wane gidan yari aka tsare shi?
• Wace kotu ce ke sauraron shari'arsa?
• Wane alƙali ne ya bayar da umarnin tsare shi?
Idan ba ku da hujja bayyananniya, to ku ji tsoron Allah, ku guji yaɗa jita-jita da zargin mutane ba tare da dalili ba. Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:
﴿يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِنْ جَاءَكُمْ فَاسِقٌ بِنَبَإٍ فَتَبَيَّنُوا﴾
"Ya ku waɗanda s**a yi imani! Idan mai fasikanci ya zo muku da wani labari, to ku tabbatar da gaskiyarsa." (Suratul Hujurāt: 6)
Allah Ya shiryar da mu baki ɗaya zuwa ga gaskiya, Ya tsaremu daga yaɗa ƙarya da jita-jita. Āmīn.