Albarka Reporters Hausa

Albarka Reporters Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Albarka Reporters Hausa, Broadcasting & media production company, Bauchi.

RAYUWA KENANAnyi jana'izar Shugaban Sojojin Nigeria LT Gen. Taoreed Lagbaja bisa karantarwan addininsa na Kirista a maka...
15/11/2024

RAYUWA KENAN

Anyi jana'izar Shugaban Sojojin Nigeria LT Gen. Taoreed Lagbaja bisa karantarwan addininsa na Kirista a makabartan Sojoji dake Abuja karkashin jagorancin Shugaban Kasa Tinubu

Allah Ka sa mu gama da duniya lafiya

12/08/2024

Daga Ina Kuke Bibiyar Ƙafar Albarka Reporters Hausa ?

Masha Allah: Musulunci ya samu karuwaTun ba yau ba wannan matashiya 'yar kabilar 'Igbo'  ke son komawa addinin musulunci...
11/05/2024

Masha Allah: Musulunci ya samu karuwa

Tun ba yau ba wannan matashiya 'yar kabilar 'Igbo' ke son komawa addinin musulunci amma mahaifiyarta ta ki amincewa. Cikin ikon Allah, yanzu haka mahaifiyarta ta amince da hakan wadda tuni har ta karbi kalmar shahada kuma aka gabatar da ita ga al'ummar da ke barikin sojoji na Ojo da ke jihar Lagos, inda take da zama.

Albarka Reporters Hausa

HAJJIN BANA: Wata Maniyyaciyar kasar INDONESIA ta rushe da kuka tare da yin Sujjadar godiya ga Allah da ya bata damar ha...
11/05/2024

HAJJIN BANA: Wata Maniyyaciyar kasar INDONESIA ta rushe da kuka tare da yin Sujjadar godiya ga Allah da ya bata damar halarta kasar mai tsarki don gudanar da aikin Hajjin bana.

maniyyaciyar tana sauka daga cikin Jirgi a filinbJirgin sama na Madinah, ta fara kwalla, daganan kuma tayi sujadar godiya ga Allah madaukakin sarki.

Albarka Reporters Hausa

HUMAN RIGHTS STUDENT ACTIVISTS OF NIGERIA Kungiya Mai suna a sama Dake da ofishinta a cikin garin bauchi Wanda comr Abba...
12/02/2024

HUMAN RIGHTS STUDENT ACTIVISTS OF NIGERIA

Kungiya Mai suna a sama Dake da ofishinta a cikin garin bauchi Wanda comr Abbas Umar Yusuf, ke jagoranta ta shirya wani shiri na musammam domin daliban makarantun sakandare na jihar bauchi, kan wayar musu dakai akan muhimmmancin ilimi, da tallafa musu Da dukkanin karfin da kingiyar ke dashi was dalibai masu kwazo na tsawon sati daya (one week).

Za'a fara gabatar da shirin ne (Program) na sati guda a ranar:

Alhamis: 15_2_2024
Zuwa tsawon sati

Sign:
Journalist Sulaiman Ahmad Sulaiman
PRO Bauchi human righ student activists

INTEGRATED ROYAL ACADEMY ALKALERIDaliban makarantar “integrated royal academy alkaleri” kenan s**a fito domin tsaftace m...
11/10/2023

INTEGRATED ROYAL ACADEMY ALKALERI

Daliban makarantar “integrated royal academy alkaleri” kenan s**a fito domin tsaftace muhallin bayan makarantar su domin assasa hidiman tsafta

Daliban Wanda s**a samu jagorancin malamansu, sun gudanar da aikin tsaftar muhallin ne a safiyar yau a bayan makarantar, Inda ciyawa ke tsirowa a Duk lokacin da ake yanayin damuna.
Sashin tallace tallace
______________________
ADMISSION! ADMISSION!! ADMISSION!!!

Makarantar INTEGRATED ROYAL ACADEMY ALKALERI dake unguwar RAILWAY a cikin Karamar hukumar Alkaleri, Tana sanar da iyaye da masu kula da tarbiyyar yara cewa tana cigaba da daukan sabin dalibai na zangon karatun 2023/24 a matakan NURSERY, PRIMARY 1-5 da kuma SECONDARY SCHOOL (JSS 1-3 & SS1-3)

Wannan makaranta tana da kwararrun malamai da ma’aikata wanda suke kula da Ilimi, Tarbiyya da kuma Tsaftar dalibai.

Makarantar tayi fice gurin koyarda English language, Mathematics da Science.

Akwai kayayyakin koyo na zamani masu inganci harma da tanadin gurin wasan dalibanta.

Baya ga haka, kudin makarantar an saka shi daidai yanda masu karamin karfi zasu iya biya.

Daliban wannan makaranta suna samun ingantaccen ilimi yayin da iyaye suke biyan kudi me sauki.

Ga bayanin kudin makarantar kamar haka
- Nursery 1-3 N4000
- Primary 1-5 N4350
- Secondary N5350

Baya ga haka, akwai rangomin kudin makarantar dalibi 1 ga iyaye da yaransu s**a kai adadin mutum 5

Domin karin bayani za’a iya kiran wannan lamba
08101648653
0706 609 0995

Sanarwa daga hukumar Makarantan

👌Journalist Sulaiman Ahmad Sulaiman

09/10/2023

Daga ina kuke bibiyar wannan kafar ta Albarka Reporters Hausa a fadin najeriya?

BARNAR RUWAN SAMA: ruwa ya yi barna a ƙaramar hukumar Misau Dake jihar Bauchi, da iska maikarfi da  akalla gidajen kusan...
21/05/2023

BARNAR RUWAN SAMA: ruwa ya yi barna a ƙaramar hukumar Misau Dake jihar Bauchi, da iska maikarfi da akalla gidajen kusan dari ko fiye da haka da shaguna ne su ka rushe sakamakon wannan ruwa.

Ma'ajiyar mu ta shaida mana cewa ruwan yazo da ƙarfi inda ya yaye rufin gidaje dakuma shaguna da gine-ginen da ba'a kammala gina wa ba duk a cikin garin na misau.

Majiya: Aliko Muhammad misau

Jerin Sunayen Manyan ‘Yan Siyasa 16 Da Ake Tunanin Tinubu Zai Nada Ministoci In Aka Rantsar DashiWani rahoto da jaridar ...
18/05/2023

Jerin Sunayen Manyan ‘Yan Siyasa 16 Da Ake Tunanin Tinubu Zai Nada Ministoci In Aka Rantsar Dashi

Wani rahoto da jaridar Nigerian Tribune ta wallafa na nuni da cewa zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya fara duba tsarin majalisar ministocinsa da kuma ta masu kula da tattalin arziki.

Ga jerin sunayen su kamar haka;

1, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje (Kano) Ministan harkokin noma da raya yankunan karkara

2, Gwamna Nyesom Wike (Ribas) - Ministan harkokin cikin gida.

3, Dakta Kayode Fayemi - Ministan harkokin kasashen waje.

4, Farfesa Peter Okebukola - Ministan Ilimi.

5, Malam Nuhu Ribadu Ministan harkokin 'yan sanda.

6, Sanata Aisha Binani - Ministar wutar lantarki.

7, Babatunde Ogala - Ministan shari'a.

8, Wale Edun - Ministan kudi, kasafi da tsare-tsare.

9, M**o Boyo - Ministan mai.

10, Ayo Abina - Karamin ministan tsare-tsare.

11, Femi Gbajabiamila - Shugaban ma'aikata.

12, Yewande Sadiku - Ministan masana'antu.

13, Farfesa Yemi Oke

14, Iyin Aboyeji

15, Dayo Israel

16, Uju Ohanenye

Kamar dai yadda majiyar wacce ba a bayyana sunanta ba ta bayyana, wadannan su ne sunayen manyan ‘yan siyasar da ake tunanin Tinubu zai ba ministoci, da kuma ma'aikatun da za a tura su:

Sai dai jaridar The Guardian ta wallafa cewa akwai wasu daga cikin ministocin gwamnatin Buhari da s**a aika kokon bararsu zuwa ga Tinubu. Ta ce wasunsu tun kan ya dawo daga tafiyar da ya yi zuwa Faransa s**a rika aika masa da sakonni na neman a sanyasu cikin wadanda za a yi tafiyar da su.

✍️ Comr Abba Sani Pantami

Wato duk ranar da akace babu Najeriya a duniya to lallai duniya za ta yi rashin yan sharholiya😅Ga fa Mutuwa Boys 🤔~ Alba...
18/05/2023

Wato duk ranar da akace babu Najeriya a duniya to lallai duniya za ta yi rashin yan sharholiya😅

Ga fa Mutuwa Boys 🤔

~ Albarka Reporters hausa

Wannan Shi Ne Karen Da Ya Fi Kowane Kare Tsawo A Duniya, Sunansa Zeus Dake Michigan A Ƙasar Amurka Kuma Tuni Kundin Tari...
18/05/2023

Wannan Shi Ne Karen Da Ya Fi Kowane Kare Tsawo A Duniya, Sunansa Zeus Dake Michigan A Ƙasar Amurka Kuma Tuni Kundin Tarihin Duniya Na Guinness Ya Ba Shi Wannan Kambun

AN GUDANAR DA TARON RANTSAR DA ƊALIBAI DA BADA SAKAMAKON WAƊANDA S**A KAMMALA DIPLOMA A MAKARANTAN KAZAURE SCHOOL OF HEA...
18/05/2023

AN GUDANAR DA TARON RANTSAR DA ƊALIBAI DA BADA SAKAMAKON WAƊANDA S**A KAMMALA DIPLOMA A MAKARANTAN KAZAURE SCHOOL OF HEALTH TECHNOLOGY A ALAKALERI.

A safiyar Ranar asabar ne makarantan 'kazaure school of health technology' reshen karamar hukumar Alkaleri ta gudanar da taron rantsar da dalibanta (matriculation) dakuma bada satifiket ma ɗalibai ashirin da biyar waɗanda s**a kammala karatun diploma a ƙarƙashin Director sulaiman sani kusa a filin makarantan dake Alkaleri.

Taron ta samu halartar manyan baƙi daga wurare mabanbanta wanda s**a zo don taya ɗaliban murnan gama karatun su na diploma da kuma waɗanda aka rantsar dasu, kuma sun samu kyakkyawar tarba daga hukumomar makarantan wanda Director sulaiman sani ƙusa ke jagoranta.

A jawabin godiya malam Suleiman Sani Kusa ya yaba ma ɗauka cin malamai da ɗaliban Makarantan bisa nuna ƙwazo wajen bayar da ilimi dakuma ƙoƙarin fahimta da ɗaliban ke yi kuma ya karrama wasu daga cikin waɗan da s**afi nuna ƙwazo tareda bada satifiket ma waɗanda s**a kammala.

Shugaban ƙaramar hukumar Alkaleri wanda uwargidansa Hajiya safiya ta wakilceshi a wurin taron ta yaba da
irin kokari da daraktan makarantan yake wajen tallafawa matasa ta fannin ilimi da biya musu karatu kyauta a makarantamun lafiya, inda tace 'gwamnatin su zata haɗa kai dashi wajen cigaba da samar da hanyoyin tallafawa ɗaliban Alkaleri wajen rage musu raɗaɗin Jahilci.

Shima a nasa ɓangaren Sarkin Alkaleri Alh abdulƙadeer Muhammad wanda ɗan sa yariman Alkaleri ya wakilta ya yi ƙira ga ɗaliban da suke cin gajiyar ilimi kyauta a makarantar da su dage suyi karatu mai kyau don taimakon wasu na baya dasu masu bukatar taimako, inda yace "idan an taimaka maka kaima kayi ƙoƙari ka taimaki wasu da daman da Allah ya baka".

Muna fata tareda addu'ar Allah Ubangiji ya ƙara daɗa taimakawa sulaiman sani kusa shugaban wannan makaranta ta (North Eastern college of Medical and health sciences Alkaleri) don cigaba da taimakawa marayu da marasa ƙarfi a faɗin ƙaramar hukumar.

Daga: Journalist sulaiman Ahmad sulaiman
Alkaleri

Address

Bauchi

Telephone

+2348101648653

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Albarka Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share