14/04/2025
Muhammad Sani Dattijo Mataimakin Gwamnan CBN, Ya Bayyana ƙoƙarin da suke Don rage Hauhawar Farashin kayayyaki da Inganta Tattalin Arzikin Najeriya a Taron JP Morgan na 2025
A yayin wani taro mai matukar muhimmanci da aka gudanar karkashin inuwar JP Morgan Forum a shekarar 2025, Muhammad Sani Abdullahi, Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Kan munufofin Tattalin Arziki ya bayyana cikakkun manufofi da tsare-tsaren da za su taka rawa wajen farfado da tattalin arzikin kasar.
A cikin jawabin nasa mai zurfi da hangen nesa, Muhammad Sani Abdullahi ya tabo batutuwa masu sarkakiya da s**a shafi tsarin musayar kudi, hauhawar farashi, da kuma gina tubalin ci gaba mai dorewa. Ya bayyana cewa Babban Bankin Najeriya na daukar matakai masu karfi domin daidaita musayar kudin waje da na gida, tare da saukaka harkokin kasuwanci da janyo hannun jari daga ketare.
“Manufofin da muke aiwatarwa sun mayar da hankali kan daidaita kasuwar musayar kudi da kuma karfafa gwiwar masu saka hannun jari,” in ji shi. Ya kara da cewa, irin wannan sauye-sauyen na nuni da alamar ci gaba, duba da yadda ake samun cigaba a matsalolin da s**a dabaibaye tattalin arzikin kasar a baya-bayan nan.
Dangane da hauhawar farashi, Sani Abdullahi ya jaddada cewa CBN na aiki tare da sauran hukumomin gwamnati domin rage radadin matsin tattalin arziki da ake fama da shi, Musamman ta fuskar abinci da albarkatun yau da kullum. A cewarsa, an dauki matakan gaggawa wajen kara samar da kayayyaki da tabbatar da daidaito a farashin su a kasuwa.
Jawabin nasa ya samu karbuwa sosai daga mahalarta taron, inda aka yaba da irin hangen nesan da ya gabatar, musamman game da bukatar hadin gwiwar bangaren gwamnati da na masu zaman kansu wajen gina ingantaccen tsarin tattalin arziki.
KBC Hausa