Bauchi post

Bauchi post Bauchi Post Dan Wallafa Sahihan Labarai Daga Ko Wacce Jaha

DA DUMI-DUMI: Sanata Abdulaziz Yari, ya sayi hannun jari mafi girma a kamfanin lantarki na Geregu Power, wanda ya siya k...
31/12/2025

DA DUMI-DUMI: Sanata Abdulaziz Yari, ya sayi hannun jari mafi girma a kamfanin lantarki na Geregu Power, wanda ya siya kimamin Naira Tiriliyan 1.125.

Abdulaziz Yari, tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma ɗan siyasa mai tasiri a Najeriya, ya zama mai rike da kaso mafi rinjaye a kamfanin Geregu Power, bayan wata babbar yarjejeniya ta dala miliyan $750 wadda ta kawo ƙarshen ikon Femi Otedola akan kamfanin.

MA’AM Energy Limited, kamfanin da Yari ke jagoranta, ya sayi kashi 95% na hannun jari a Amperion Power, wanda shi ne ke rike da yawancin hannun jari na Otedola a Geregu Power. Hakan ya bai wa Yari damar samun kashi 77% na cikakken hannun jari a kamfanin.

Yanzu haka, Abdulaziz Yari ne shugaban rukunin kamfanin Geregu Power — daya daga cikin manyan kamfanonin lantarki da ake bibiya sosai a kasuwar hada-hadar hannun jari a Najeriya.

Kamfanin yana da ƙarfin samar da wutar lantarki har megawatt 435. A watanni uku na ƙarshe zuwa Satumba, Geregu Power ta samu karin ribar har Naira biliyan 11.2 kafin haraji — karin kashi 82%. Hakanan, kudaden shigar kamfanin sun karu da kashi 37% zuwa Naira biliyan 43.8.

Wannan sauyi na nuna sabon salo a kasuwar makamashi ta Najeriya, inda 'yan siyasa ke shiga harkokin kasuwanci na babbar riba

Rahoton African billionaire.

Matasan Bauchi Ta Arewa Sun Roki Siraj Ibrahim Tanko Ya Sake Neman Kujerar Sanata a 2027 Matasan  Bauchi T Arewa sun bay...
22/05/2025

Matasan Bauchi Ta Arewa Sun Roki Siraj Ibrahim Tanko Ya Sake Neman Kujerar Sanata a 2027

Matasan Bauchi T Arewa sun bayyana roƙon su ga tsohon ɗan takarar Sanatan Bauchi Ta Arewa a zaɓen 2023, Siraj Ibrahim Tanko, da ya sake tsayawa takara a babban zaɓen 2027. Wannan ƙiran na zuwa ne sakamakon gazawar Sanata Sama’ila Dahuwa Kaila, wanda ke wakiltar shiyyar a halin yanzu, wajen samar da ci gaba tun daga lokacin da aka rantsar da shi har zuwa yau.

A cikin wata sanarwa da Matasan s**a fitar bayan wani taron gaggawa da s**a gudanar, matasan sun nuna damuwa kan yadda yankin Bauchi Ta Arewa ke fuskantar koma baya a fannoni da dama na rayuwa.

“Muna roƙon Siraj Ibrahim Tanko da ya saurari kiran al’umma, ya sake fitowa takara a 2027. Shi matashi ne mai kwazo da hangen nesa, kuma muna da tabbacin cewa zai wakilci yankinmu da cancanta da gaskiya,” in ji shugaban Matasan, a cikin sanarwar.

Matasan sun bayyana cewa ƙoƙarin da Siraj Ibrahim Tanko ya yi a baya, da irin goyon bayan da ya ke samu daga matasa da dattijon yankin, su ne ke karfafa masu gwiwar neman dawowarsa fagen siyasa. Matasan sun bayyana cewa sun himmatu wajen ganin an dawo da martabar wakilci na gaskiya a yankin, ta hanyar goyon bayan Siraj Ibrahim Tanko a zaɓen mai zuwa.

Muhammad Sani Dattijo Mataimakin Gwamnan CBN, Ya Bayyana ƙoƙarin da suke Don rage Hauhawar Farashin kayayyaki da Inganta...
14/04/2025

Muhammad Sani Dattijo Mataimakin Gwamnan CBN, Ya Bayyana ƙoƙarin da suke Don rage Hauhawar Farashin kayayyaki da Inganta Tattalin Arzikin Najeriya a Taron JP Morgan na 2025

A yayin wani taro mai matukar muhimmanci da aka gudanar karkashin inuwar JP Morgan Forum a shekarar 2025, Muhammad Sani Abdullahi, Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Kan munufofin Tattalin Arziki ya bayyana cikakkun manufofi da tsare-tsaren da za su taka rawa wajen farfado da tattalin arzikin kasar.

A cikin jawabin nasa mai zurfi da hangen nesa, Muhammad Sani Abdullahi ya tabo batutuwa masu sarkakiya da s**a shafi tsarin musayar kudi, hauhawar farashi, da kuma gina tubalin ci gaba mai dorewa. Ya bayyana cewa Babban Bankin Najeriya na daukar matakai masu karfi domin daidaita musayar kudin waje da na gida, tare da saukaka harkokin kasuwanci da janyo hannun jari daga ketare.

“Manufofin da muke aiwatarwa sun mayar da hankali kan daidaita kasuwar musayar kudi da kuma karfafa gwiwar masu saka hannun jari,” in ji shi. Ya kara da cewa, irin wannan sauye-sauyen na nuni da alamar ci gaba, duba da yadda ake samun cigaba a matsalolin da s**a dabaibaye tattalin arzikin kasar a baya-bayan nan.

Dangane da hauhawar farashi, Sani Abdullahi ya jaddada cewa CBN na aiki tare da sauran hukumomin gwamnati domin rage radadin matsin tattalin arziki da ake fama da shi, Musamman ta fuskar abinci da albarkatun yau da kullum. A cewarsa, an dauki matakan gaggawa wajen kara samar da kayayyaki da tabbatar da daidaito a farashin su a kasuwa.

Jawabin nasa ya samu karbuwa sosai daga mahalarta taron, inda aka yaba da irin hangen nesan da ya gabatar, musamman game da bukatar hadin gwiwar bangaren gwamnati da na masu zaman kansu wajen gina ingantaccen tsarin tattalin arziki.

KBC Hausa

A Yaune 17/March 2025 Cikin Hukunchin Allah Hon. Nura Usman Ganaru Yasamu Damar Assasa Tubalin Ginin Masallaci A Garin K...
17/03/2025

A Yaune 17/March 2025 Cikin Hukunchin Allah Hon. Nura Usman Ganaru Yasamu Damar Assasa Tubalin Ginin Masallaci A Garin Katuri dake Madara District Katagum Local Government a Madadin Dr Bala Maijama'a Wunti.

Hon Nura Usman Ganaru Yayi Alkawarin Gina Masallacin Ne Shekara Biyu Das**a Wuce Yau Cikin Ikon Allah Yacika Alkawari Kamar Yadda Yadauka Ansadaukar Dawannan Ginin A Alh Bala Wunti Maijama'a.

Allah Yakara Bada Ikon Cigaba Da Ayyukan Alkhairi A Kasa Baki Daya.

Masu Ruwa da tsaki na kudancin Kaduna Zone 3 Sun Yabawa Gwamna Uba Sani bisa Gudanar da mulki ba tare da nuna kabilanci ...
26/08/2024

Masu Ruwa da tsaki na kudancin Kaduna Zone 3 Sun Yabawa Gwamna Uba Sani bisa Gudanar da mulki ba tare da nuna kabilanci ba.

A Ranar 24 ga Agusta, 2024, Masu Ruwa da tsaki daga kananan hukumomi takwas (LGAs) na yankin Kudancin Kaduna sun hallara a karamar hukumar Jema’a, Kafanchan, Domin tattauna ci gaban al’ummarsu Tattaunawar ta ta'allaka ne kan muhimman fannoni kamar ilimi, kiwon lafiya, noma, da bunkasa jarin bil'adama.

Babban mataimaki na musamman (SSA) kan hulda da masu ruwa da tsaki na 1 ga Gwamnan Jihar Kaduna, MS Ustaz ne ya kira taron. Taron ya samu halartar wakilan JNI, CAN, Shugabannin jam’iyya, ƙungiyoyin kasuwa, da kungiyoyin tallafawa matasa da mata.

Masu ruwa da tsaki daban-daban sun yi bi-bi-bi-da-bi don tantance manufofi da ayyukan da s**a shafi jama'a da aka fara a karkashin Gwamnatin Sanata Uba Sani a shiyyar. Sun yabawa Gwamnan bisa salon jagorancin sa, Tare da amincewa da wasu ayyuka na musamman na inganta rayuwar al’ummar Kudancin Kaduna.

Taron ya samar da wani dandali na mu’amala da masu ruwa da tsaki domin bayyana damuwarsu a fili game da al’amuran da s**a shafi al’ummarsu. MS Ustaz ya amsa a madadin Gwamnati, yana ba da cikakkun bayanai kan tsare-tsare da ayyukan da mutane ke aiwatarwa.

An kammala ziyarar Kafanchan da Ziyartar mai Martaba Sarkin Jama’a, Alhaji Muhammadu Isa Muhammadu domin neman Tabbarraki.

Za a ci gaba da gudanar da wadannan ayyuka a fadin jihar Kaduna domin tabbatar da ingantaccen tsarin amsa tambayoyi da kuma ci gaba da huldar jama’a a matsayin babban ginshiki a Gwamnatin Sanata Uba Sani.

Dauka Nauyi Babban Mataimaki na Musamman kan Hulda da Jama'a na Gwamnan Jihar Kaduna Mal Uba Sani,M S Ustaz Mesittin

Hon Siraj Ibrahim Tanko Ya Miƙa Taaziyyar sa Ga Ilahirin Al'ummar Jihar Bauchi Bisa Rashin Alh Yarima Aliyu Giade (Ajiya...
03/08/2024

Hon Siraj Ibrahim Tanko Ya Miƙa Taaziyyar sa Ga Ilahirin Al'ummar Jihar Bauchi Bisa Rashin Alh Yarima Aliyu Giade (Ajiyan Giade)

Alh Sirajo Ibrahim Tanko Ɗan Takarar Sanatan Bauchi Ta Arewa a jam'iyyar APC a zaɓen da ya Gabata na 2023. Ya mika sakon Taaziyyar sa bisa Rashin ɗaya Daga cikin Dattawan jihar Bauchi Mai Girma Alh Yarima Aliyu Giade Wanda Allah ya Karɓi Rayuwarsa a Ranar Alhamis ɗaya ga watan Agusta 2024 a ƙasar Egypt

Siraj Ibrahim Tanko Ya bayyana Yarima Aliyu Giade a matsayin Dattijo wanda ya bada gudummawa Wajen ciyar da jihar Bauchi da kasa baki ɗaya, Ya kwashe tsawon shekaru yana hidima wa al'umma ba tare da nuna Gajiyawa ba. Yana Rokon Allah Yajikan sa da Rahama Yasa aljanna ce makomar sa Amiin summa Amiin.

Sa hannu Alh Sirajo Ibrahim Tanko Dan Takarar Sanatan Bauchi Ta Arewa A zaɓen da Ya Gabata na 2023

Kungiyar Matasan Arewa Ta janye Daga Zanga-Zangar da ake yi a faɗin ƙasar nanKungiyar Matasan Arewa a ƙarƙashin Jagoranc...
03/08/2024

Kungiyar Matasan Arewa Ta janye Daga Zanga-Zangar da ake yi a faɗin ƙasar nan

Kungiyar Matasan Arewa a ƙarƙashin Jagorancin AMB Abdul Hameed Danbature. a Hukumance ta bayyana cewa ta janye Daga zanga-zangar da ake yi a faɗin ƙasar Saboda shawarwari da s**a samu Daga Malamai da fastoti kan mahimmanci tattaunawa da Gwamnati a maimakon Zanga-Zangar da ake yi

"Kungiyar Matasan Arewa Youth Assembly for Good Leadership ta umurci kodinetocin na jihohi 19 da su dakatar da Gudanar da zanga-zangar lumana da ake yi a fadin kasar nan. "A maimakon haka, Ƙungiyar Matasan ta ba da shawarar yin tattaunawa mai ma'ana da Gwamnatin tarayya don magance matsalolin da ke faruwa a halin yanzu.

Sa Hannu Ambassador Abdul Hameed Danbature Shugaban Ƙungiyar Arewa Youth Assembly for Good Leadership

Dujiman Giade Ya Tallafawa Marayu da Marasa Galihu Kimanin 400 da Tallafin Naira  Dubu 10,000 Domin Su Dogara da kansu A...
30/07/2024

Dujiman Giade Ya Tallafawa Marayu da Marasa Galihu Kimanin 400 da Tallafin Naira Dubu 10,000 Domin Su Dogara da kansu A ƙaramar Hukumar Giade

A Jiya ne Alh Zahraddeen Aminu Abubakar Dujiman Giade Ya Tallafawa al'umma marayu da Marasa Galihu Domin Ganin sun Dogara da kansu Duba da halin da ake ciki Na Yau Da kullum

A nasa Jawabin Alh Zaharaddeen Aminu Abubakar (Dujiman Giade) Ya shawarci waɗanda s**a rabauta da Tallafin dasuyi Amfani dashi Ta Hanyar da Yadace Domin dogaro da kansu.

Daga Muhammad Sarkin Yaƙi

Attaijirinnan na nahiyar Africa dan asalin jihar Kano Alh. Aliko Dangote, Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, yayi mart...
27/07/2024

Attaijirinnan na nahiyar Africa dan asalin jihar Kano Alh. Aliko Dangote, Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, yayi martani akan Rashin ingancin Sabuwar matatar man sa da NNPCL tace

Wanda Manema labarai s**a zanta da ɗaya Daga cikin Babban jami'in rukunin Dangote Rabiu Umar Abdullahi. Jami'i mai kula da hadahadar cinikayya kuma me mai Wakiltar Matatan man ta Dangote

Rabiu Umar Abdullahi Ya bayyana Ainihin Abinda ma'aikatar take ciki a halin Yanzu

"Matatar man Dangote ita ce Mafi girma a Afrika sannan ta kasance tana da Kayan aiki na zamani Wanda ta fara aiki tun watan Fabrairu na wannan shekara da muke ciki "inda ta ke sayar da mai Ga Kasashen Duniya da dama sannan matatar ta sami duk wata sahalewa da ake bukata domin fara aiki Sannan ko lita ɗaya bata fita saida sa hannun gwamnati "Amma kuma abin mamaki sai kwatsam muka ji hukumar (NMDPRA) tana s**ar matatar mu da cewa wai man da take tacewa bashi da inganci kasancewar kwararru sun tabbatar da ingancin matatar hakan ne ma yasa take tsawon watanni sannan sun mun mallaki duk lasisin da ake buƙata

Rabiu Umar Abdullahi Ya warware jitajitar da ake Yadawa dangane da cewa Matatar bata samu lasisi Daga Hukumar (NMDPRA) domin fara aiki

"Wannan Hukuma ta (NMDPRA) ita ce ta bayar da wannan lasisin, to Abin tambayar? shine ita da ta bayar da lasisi Sannan ko lita ɗaya bata fita sai da sa hannun ta amma kuma ta dawo tace bata yadda da ingancins ba abin akwai daure kai Duk mai hankali bazai yarda da hakan ba.

"Sannan wannan matatar ta kasance tana aiki wajen tace mai nau'i nau'i sannan tana sa ran fara tace man fetur a wannan wata na Agusta da za mu shiga Insha Allah inji Jami'in

Rabiu Umar Abdullahi Ya bayyana Cewa Dangote Ya Gina Matatar ne domin Ganin an kawo karshen fita da mai da ake zuwa ƙasashe domin tace wa.

"Burin Dangote na gina wannan matata shine wajen ganin an tsaida shigo da mai daga ƙasashen ketare kasancewar ƙasar Najeriya tana da arzikin mai amma sai anje an siyar da Danyen mai sannan a siyo tacacc

Dangote ya zargi kamfanonin mai na kasa da kasa (IOCs) da yin magudin farashin danyen mai tare da ƙoƙarin hargitsa matat...
24/06/2024

Dangote ya zargi kamfanonin mai na kasa da kasa (IOCs) da yin magudin farashin danyen mai tare da ƙoƙarin hargitsa matatar mansa da gangan.

Devakumar Edwin, Mataimakin Shugaban Kamfanin Mai da Gas na Kamfanin Dangote Industries Limited (DIL), ya yi zargin cewa IOCs da ke aiki a Najeriya na yin zagon kasa ga ci gaban aikin matatar mai da man fetur na Dangote.

Edwin ya bayyana haka ne da taron Editocin Makamashi yayin wani taron bita na yini daya da kungiyar Dangote ta shirya.

Yayi nuni da cewa da gangan IOCs na kawo cikas Ga yunkurin da matatar ta ke yi na siyan danyen mai ta hanyar yin tsadar farashi sama da farashin kasuwa. Wannan lamarin ya tilasta matatar da shigo da danyen mai daga ƙasashe masu nisa kamar Amurka, wanda hakan ya haifar da tsadar kayayyaki.

Edwin ya ce, “Yayin da Hukumar Kula da Man Fetur ta Najeriya (NUPRC) ke kokarin ganin ta ware mana danyen man fetur, da gangan IOCs na kawo cikas ga kokarin da muke na sayen danyen mai a cikin gida.

“Ya kamata a tuna cewa a kwanan baya NUPRC ta gana da masu hako danyen mai da masu matatun mai a Najeriya domin tabbatar da cikakken bin Domestic Crude Oil Supply Obliging (DCSO), kamar yadda aka bayyana a karkashin sashe na 109 (2) na dokar masana’antar man fetur (PIA). Da alama manufar IOCs ita ce tabbatar da cewa matatar man mu ta gaza.

"Ko dai suna neman kari mai yawa ko kuma suna da'awar cewa ba a samun danyen mai. A wani lokaci, mun biya $6 sama da farashin kasuwa.

"Wannan ya tilasta mana rage kayan da muke hakowa da shigo da danyen mai daga kasashe har zuwa Amurka, wanda hakan ya kara tsadar kayayyakin da muke samarwa."

KBC Hausa

Sheikh Sudais ya jagoranci kammala sauke Alkur'ani  a sallar tarawihi a daren yau tare da yin doguwar addu'a - Allah ya ...
08/04/2024

Sheikh Sudais ya jagoranci kammala sauke Alkur'ani a sallar tarawihi a daren yau tare da yin doguwar addu'a - Allah ya karawa Annabi daraja.

Address

Ran Road Bauchi
Bauchi

Telephone

+2348169230178

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bauchi post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share