24/09/2025
KIRANYE TARE DA NEMAN GOYON BAYA....
Hakika Mu Al'ummar Yankin Bauchi Ta Tsakiya Munjima Muna Samun Koma Baya A Bangaren Wakilci A Majalisar Dattawan Nijeria
Hakan Kuma Bai Rasa Nasaba Da Samo Asali Ba A Saboda Tura Wakilan Da Basu Chanchanci A Tura Su Majalisar Dattawa Ba Da Mukeyi
Me Ake Kira Da Majalisar Dattawa
Majalisar Dattawa Wurine Na Wakilcin Da Ake Son A Tura Mutum Jajirtacce, Mai Ilimi, Kuma Mai Son Cigaban Al'ummarsa, Wanda Zai Kutsa Ya Nemo Wa Al'ummarsa Cigaba
Amma Mu A Bauchi Central Kusan Kullum Idan Muka Tura Wakili Mukan Tsinci Kammu A Yanayin Gwanda Jiya Da Yau
A Saboda Wannan Dalilin Yasa Muka Ga Ya Dace Muma Mu Samar Wa Kammu Mafita A Matsayin Mu Na Matasa Manyan Gobe
Hakan Yasa Mukaga Dacewar Mu Nemo Matashi Haziki Mai Halin Dattaku Wanda Yayi Fice A Harkokin Gwagwarmaya A Fannoni Da Dama, Domin Mu Mara Masa Baya Domin Ya Kawo Mana Cigaban Da Muke Gani A Sauran Yankuna
Hakan Yasa Mukayi Nazari Mai Zurfi Tare Da Tunani Mai Zurfi A Wannan Lokacin Domin Ganin Cigaban Yankin Mu
Saboda Wadan Nan Dalilan Da Muka Duba Yasa Muka Ga Babu Wanda Ya Dace A Wannan Lokacin Da Mu Masa Kiranye Domin Yazo Ya Cire Mu A Halin Da Muke Tsintar Kammu Sai Barrister Ahmed Yarima Misau (BAWU)
Barrister Ahmed Yarima Matashi Ne Haziki Wanda Yake Da Kishin Al'umma Tun Tasowan Sa, Sannan Ya Nuna Bajinta Masu Yawan Gaske Da Ba Zasu Irgu Ba, Duk Wanda Ya Sanshi Yasan Irin Kokarinsa Da Yakeyi Na Jibantar Lamarin Al'umma
A Saboda Haka Muke Masa Kira Da Ya Daure Yazo Ya Tsaya Mana Takarar Kujerar Sanatan Bauchi Ta Tsakiya A Shekarar 2027
Sako Daga
Amb. Hashim M Haruna Ningi 09075025321
( Co-ordinator Youth Ambassadors Central Zone)