Jounalist groups by sadeeq action

Jounalist groups by sadeeq action Public relationship

28/10/2025

Yadda 'yanbindiga daga jahar Katsina ke tsallakawa suna kai hare-hare a jahar Kano

Mazauna yankin ƙaramar hukumar Shanono da ke jihar Kano sun koka game da yadda 'yanbindiga ke kai musu hare-hare tare da sace mutane da dabbobinsu.

A ranar Alhamis ne wata ƙungiyar mazauna ta yi taron manema labarai domin shaida wa duniya yadda s**a ce 'yanbindigar na tsallakawa daga Katsina domin kai musu hare-hare.

Yayin taron manema labaran a ranar Alhamis, shugaban al'ummar Farin-Ruwa Alhaji Yahaya Bagobiri ya nemi gwamnatin taayya da ta jihar su kawo musu ɗauki.

"Muna neman Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da Gwamna Abba Kabir Yusuf su kawo mana ɗauki saboda tuni wasu mazauna yankin s**a fara barin gidajensu zuwa birnin Kano da maƙwabtan garuruwa," in ji shi.

Bagobiri ya ce wasu hare-hare da 'yanfashin s**a kai musu ranar Talata da Laraba sun yi sanadiyyar raunata mutane da kuma sace shanu da dama.

Taskar Hausa News
Taskar Hausa Nws
Bauchi city
Arsenal

28/10/2025

Mataimakin shugaban kasar Amurka zai gana da Netanyahu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Gaza

Mataimakin shugaban Amurka, JD Vance, zai gana da firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu don tattauna matakan ci gaba da yarjejeniyar zaman lafya a Gaza.

Bayan ya isa ƙasar a ranar Talata, Vance ya ce an samu ci gaba fiye da yadda ake tsammani.

Ana sa ran zai matsa wa shugabannin Isra'ilar lamba don su ci gaba da tattaunawa game da batun.

Amurka dai na son a ci gaba da shirin kafa rundunar tabbatar da zaman lafiya ta kasa da kasa da kafa sabuwar gwamnati a Gaza da kuma kwance ɗamarar Hamas.

Taskar Hausa News
Arsenal
Taskar Hausa Nws

28/10/2025

Ana fargabar rikici a kasar Kamaru yayin da ake shirin sanar da sakamakon zaɓe

Ana zaman ɗarɗar a Kamaru yayin da kwamitin tsarin mulkin ƙasar ke shirin sanar da sakamakon ƙarshe na zaben shugaban ƙasa a ƙarshen wannan mako.

Shugabannin cocin Katolika sun yi kira ga yanayi na lumana saboda tsoron ɓarkewar rikici sakamakon saɓani kan sakamakon.

Ana sa ran kwamitin tsarin mulkin ƙasar zai saurari hujjoji a ƙarshen wannan mako kan jerin ƙorafe-ƙorafe da ake yi na soke zaɓen saboda zargin rashin gaskiya.

Taskar Hausa News
Arsenal
Bauchi city
Taskar Hausa Nws
Sarkin Yakin Muhammad Na'eem

28/10/2025

Waɗanne matakai ake bi wajen zaɓo manyan hafsoshin tsaron kasar Najeriya?

A ranar Juma'a ne Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naɗa sababbin hafsoshin rundunar sojin ƙasar.

Tinubu ya ce ya amince da naɗin sababbin hafsoshin ne "domin ƙarfafa tsaron ƙasa da kuma kyautata aikin" rundunar sojin.

An sauke Babban Hafsan Tsaro Janar Chris Musa da sauran hafsoshi ne bayan shekara biyu da wata huɗu bayan Tinubu ya naɗa su a watan Yunin 2023.

Sababbin hafsoshin tsaron da Tinubu ya naɗa su ne:

Janar Olufemi Oluyede - Hafsan hafsoshi (mafi girman muƙami)
Manjo Janar W Sha'aibu - Hafsan sojojin ƙasa
Air Vice Marshall S.K Aneke - Hafsan sojin sama
Rear Admiral I. Abbas - Hafsan sojin ruwa
Manjo Janar E.A.P Undiendeye - Shugaba sashen tattara bayanan sirri na soji
Ko waɗanne matakai ake bi wajen naɗa hafsoshin tsaro a Najeriya?

Taskar Hausa News
Arsenal
Bauchi city
Taskar Hausa Nws

28/10/2025

Shugaban Jam'iyar ADC na Jahar Bauchi ya kirayi al-umma birni da kyauye da su fito Dan Su yanki Katin Zabe.

Alhaji Hassan Haruna ya kirayi Al-umma ne dan su fita suyi katin zabe dan tunkaran zabe mai zuwa 2027 Wanda hakanne dai bada daman zaben shugaban da Al-umma takeso dan kawo sauyi a Kasan mu da cigaban kasa.

Taskar Hausa News
Arsenal
Bauchi city
Taskar Hausa Nws

21/09/2025
Alhamdulillah......Cikin Hukuncin Allah Yau Allah Ya Tsaga Da Rabona Mai Gidanmu Engr. Shasudeen Bala Muhammad (Cigarin ...
24/08/2025

Alhamdulillah......

Cikin Hukuncin Allah Yau Allah Ya Tsaga Da Rabona Mai Gidanmu Engr. Shasudeen Bala Muhammad (Cigarin Duguri) sanatan mu 2027 Bisa Kyautar Sabuwar Mota Daya bani zaiyi Fiye Da Haka Domin Halinsa Ne...

Tsaban Murna Bansan Mema zance Ba Allah ya saka Da Alkairi Ya Biya Maka Bukatunka na Alkairi.....

Senato sai kuma Minister irin yanda Baba yayi daman ance duk abun da ka gada dolene kaima kayi abun da yayi Sanator 1years Minister 7year Governor 8 years president 8year total 24years kana mulki

15/01/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Blessing Moses, Love Maya Abang

25/12/2023
01/07/2023

ECOWAS ta yi Allah wadai da kisan sojoji 30 a kasar Burkina Faso

Kungiyar ECOWAS ta yi Allah wadai kan wasu hare-hare da masu ikirarin jihadi s**a kai wa jami'an tsaro a Burkina Faso, lamarin da ya haddasa mutuwar aƙalla sojoji 30.

Hukumar gudanarwar ƙungiyar ta yi kira ga gwamnatin ƙasar da ta gaggauta gudanar da bincike domin gurfanar da waɗanda suke da hannu a lamarin, tare da miƙa sakon ta'aziyya ga iyalan mamatan.

Hare-haren sun auku ranar Litinin da Talata a yammaci da arewacin ƙasar.

Burkina Faso na fama da hare-haren masu iƙirarin jihadi waɗanda ke fitowa daga makwabciyar ƙasar Mali tun shekarar 2015.

Fiye da mutum 10,000 ne s**a mutu, yayin da kusan mutum miliyan biyu s**a rasa muhallansu sakamakon rikice-rikicen.

Yayin da Majalisar Dinkin Duniya ke kawo ƙarshen aikin dakarunta da ke wanzar da zaman lafiya a Mali, masana na gargaɗi kan ƙaruwar ayyukan masu ikirarin jihadi a yammacin Afirka.

Address

Ahmadu Bello Way Bauchi
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jounalist groups by sadeeq action posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jounalist groups by sadeeq action:

Share