TASKAR JAWABAN SAYYID ABDULLAHI ASHURA BAUCHI

TASKAR JAWABAN SAYYID ABDULLAHI ASHURA BAUCHI Domin samun Asrar da fawa'id na makarantar Ahlul Bait (As)

Assalamu Alaika Ya Aba Abdillah.
09/07/2025

Assalamu Alaika Ya Aba Abdillah.

AN GUDANAR DA KHATAMAN ZAMAN JUYAYIN SHAHADAR IMAM HUSAIN (A.S) A ABUJAHarkar Musulunci karkashin jagorancin Sayyid Ibra...
07/07/2025

AN GUDANAR DA KHATAMAN ZAMAN JUYAYIN SHAHADAR IMAM HUSAIN (A.S) A ABUJA

Harkar Musulunci karkashin jagorancin Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H) ta rufe zaman juyayin shahadar jikan Manzon Allah (S), Imam Husain (A.S) a Abuja

Ranar Lahadi, wanda shine ya zama goma ga watan Almuharram, an gabatar da gagarumar majalisul aza, daga bisani, sai aka gabatar da Malam Abdullahi Ashura wanda yayi jawabi har kashi biyu, da yammaci yayi jawabi maudu'i mai taken (Musibar Sayyada Zainab), bayan idar da sallah da dare kuma yayi jawabi, akan shahadar Imam Husain (A.S), Malam Abdullahi Ashura ya saka 'yar uwa da dama kuka a yayin da yake gabatar da jawaban nasa, na yammaci dana dare, bayan kammala jawabin nasa, an mika abun magana gareshi domin rufe taron da Addu'a, wannan shine ya kawo karshen zaman da akayi na kwanaki goma.

Muna fatan Allah ya kaimu na wani shekara lafiya, ya barmu bisa turbar su Imam Husain (A.S) ya karawa Husainin zamaninmu lafiya da Nisan, kwana, tare da kariya ta musamman.

Isa Charis
AliAssajjad Ibn Taheer
7th July/ 2025

Yadda muhalli na zaman Juyayin Shahadar Imam Husain (AS) ya fashe da kuka yayin da ake karanta tarihi na Abdullahi Radi ...
04/07/2025

Yadda muhalli na zaman Juyayin Shahadar Imam Husain (AS) ya fashe da kuka yayin da ake karanta tarihi na Abdullahi Radi jaririn Imam Husain (AS).

4th July, 2025
AliAssajjad Ibn Taheer

04/07/2025
Ash-Sheikh Sayyid Abdullahi Ashura, ya gabatar da jawabin Ashura a garin Sokoto.
02/07/2025

Ash-Sheikh Sayyid Abdullahi Ashura, ya gabatar da jawabin Ashura a garin Sokoto.

💢 عن الإمام الصادق عليه السلام:  وصب الماء البارد على قدميك إذا خرجت، فإنه يسل الداء من جسدك.📚 أمالي الصدوق، ص٤٤٥🔰 لتعدي...
07/05/2025

💢 عن الإمام الصادق عليه السلام:
وصب الماء البارد على قدميك إذا خرجت، فإنه يسل الداء من جسدك.
📚 أمالي الصدوق، ص٤٤٥

🔰 لتعديل حرارة الجسم ينبغي صب الماء البارد على القدمين قبل الخروج من الحمام ومن فوائد ذلك:

🔸الوقاية من الدوالي
🔸الوقاية من الصداع
🔸الوقاية من الزكام.

Daga Imam Sadiq(a.s) yace "kuma ka zuba ruwan sanyi a kafarka idan kazo fitowa (daga bayan gida) domin yin haka yana Zare cuta zarewa daga cikin jikinka, "

Kuma ance domin daidaita zafin jiki yana da kyau a rika zuba ruwan sanyi a kafa,

Daga cikin fa'idodin yin hakan akwai Hana kamuwa da.
(1) Kumburin jijiyoyin jini na qafa.

(2) Wani Nau'in ciwon Kai
(3) Mura.

🆔 Abdullahi Ashura.

02/05/2025

*ME KA SANI GAME DA RUWAN SAMA, WANDA YAKE SAUKA A CIKIN WATAN APRIL?*
Tareda Sayyid Abdullahi Ashura

An rawaito daga wasu sashi na sahabban Manzon Allah (S), su ka ce: "Muna zaune sai ga Manzon Allah (S) ya shigo garemu ya mana sallama, mu ka amsa, sannan ya ce: "Ashe bana sanar daku wani magani ba, wanda mala'ika Jibril (AS) ya sanar dani, wanda hakan yasa na zama bana buqatar likitoti?."

Sai Imam Ali (AS) da Salman (RA) da wasunsu su ka ce: "Wani magani ne wannan ya Manzon Allah?. " sai Manzon Allah (S) ya fiskanci Imam Ali (AS) sannan ya ce: "Za ka debi ruwan sama a watan Naisan (April), sannan ka karanta

suratul Fatihu qafa 70,

Ayatul Kursiyyu 70,

Qulhuwallahu 70

Falaqi 70

Nasi 70

Qul ya ayyuhal kafiroon 70.

Sannan ka sha wannan ruwa safe da yamma na tsawon kwana bakwai.

Manzon Allah ya cigaba da cewa: "Narantse da wanda ya tayar dani da gaskiya a matsayin Annabi Mala'ila Jibril (AS) ya ce min Allah Ta'ala yana kare wanda ya sha wannan ruwan daga dukkan cuta a jikinsa, zai samu lafiya, cuta za ta fita daga dukkan jikinsa da dukkan gabobinsa, kuma za a shafeta daga lauhul Mahfuz, (ma'ana za a share rashin lafiyarsa daga lauhul mahafuz ta yadda ba zai yi rashin lafiya ba).

Manzon Allah (S) ya ce: "Narantse da wanda ya tayar dani da gaskiya a matsayin Annabi, duk wanda bai da 'da kuma yana so ya samu 'da, to idan yasha wannan ruwan zai samu 'da, (a nan za mu fahimci cewa idan wata matsala ta damu mutum a rayuwa to zai iya shan wannan ruwa da niyar wannan matsala ta gushe).

Manzon Allah ya ce: "Idan mace wacce ba ta haihuwa ta sha daga wannan ruwa da niyar ta sami haihuwa to Allah zai azurta ta da 'da. Idan miji da mata mijin ya zama wanda baya iya saduwa da iyalinsa yadda ya k**ata, sannan ita kuma matar ba ta haihuwa, idan s**a sha wannan ruwan da wannan niyya to Allah Ta'ala zai yaye musu wannan matsala, abinda yake tareda mijin zai gushe, zai iya saduwa da iyalinsa yadda ya k**ata, idan matar ta yi niyyar daukar cikin da namiji ne to za ta samu, idan ta so ta haifi da namiji ko mace ne za ta samu, gasgata wannan yana cikin littafin Allah cewa: "Yana ba wanda yaso 'ya'ya mata ya ba wanda yaso 'ya'ya maza, ko kuma ya gaurayasu maza da mata, ko kuma ya sanya wanda ya ga dama ya zama wanda ba ya haihuwa"

Manzon Allah (S) ya cigaba da cewa "Idan mutum yana fama da ciwon kai ne wanda ya dameshi idan yasha wannan ruwa zai warke, idan yana da ciwon ido ne zai riqa shan wannan ruwa sannan ya riqa digawa a idonsa, sannan kuma ya wanke fuska da ruwan, zai warke da izinin Allah."

Manzon Allah (S) ya ce "Kuma wannan ruwa yana qarfafa dasashi na haqori, sannan yana sanya baki yayi dadi ya daina wari, yana kuma magance dilalan yawu daga baki, yana kuma magance majina, sannan kuma idan mutum ya ci abinci ba zai riqa samun matsalar tashin zuciya ba ko idan ya sha abu, kuma ba zai cutu ba daga dukkan matsalolin kumalli, ba zai samu matsala na raunin gabobi ba, ba zai samu matsala na ciwon baya ba, ba zai samu ciwon ciki ba, kuma ba zai samu mura ba, ba zai ji tsoron ciwon dasori ba, ba zai ji tsoron ciwon ciki ta fiskacin hanji ba, ko tsutsan ciki ba, ko kolanis (kolanis ciwo ne dake sa mutum ya kasa yin bayan gida), sannan ba zai buqaci zuwa ga yin qaho ba, (ma'ana jininsa zai daidaita), kuma ba zai gamu da kuraje ba, ba zai gamu da maruru ko kyazbi ba, ba zai gamu da hauka ba, ba zai gamu da kuturta mai ruwa da mara ruwa ba, ba zai gamu da habo ba, ko motsewar fata ba, ba zai yi makanta ba, ba zai yi kurumta ba, ba zai yi bebenta ba, ba zai yi basir ba, ba zai samu matsalar baqin ruwa a ido ba, ba zai gamu da wani ciwo ba, kuma azuminsa ba zai zama yana baci saboda rashin lafiya ko rauni na lafiya ba, ba zai sami cuturwa daga wasi wasi ba, ba zai samu cutuwa daga aljani ko shaidanu ba.

Manzon Allah (S) ya cigaba da cewa "Jibril (AS) ya ce: "Wanda ya sha daga wannan ruwa alhali yana dauke da dukkan cututtuka da suke samun mutane to wannan ruwa waraka ne daga dukkan wadannan cututtuka" sai na ce: "Ya Jibril! shin wannan ruwa zai iya warkar da cututtukan da ba ka ambata ba?" sai Jibril (AS) ya ce: "Narantse da wanda ya aiko ka da Annabci da gaskiya, wanda ya karanta wadannan ayoyi a wannan ruwa to Allah zai cika zuciyarsa da haske, (wato wannan ruwa yana magance cututtuka 'Ruhiyyan' da 'Jasadiyyan'). Yana kuma ilhama na samun shiriya, kuma wanda yasha zai samu hikima akan harshensa, kuma zai cika zuciyarsa da basira, irin wanda ba a ba wani ba, za a ba shi gafara dubu da kuma rahama dubu, za a cire algus da ha'inci, da giba da hassada da zalunci da girman kai, da rowa da kwadayi, da fushi da adawa da qiyayya da annamimanci, da cin mutuncin muta ne, duk za a cire daga zuciyarsa. A taqaice dai waraka ne daga dukkan cututtuka."

An rawaito a cikin wata riwaya cewa Manzon Allah (S) ya fada cikin abinda za a karanta a wannan ruwa na April har da 'Inna Anzalnahu 70, sannan ayi kabbara 70, La' ilaha illallah 70, sannan salatin Annabi da iyalan gidansa 70.

(Muhjid Da'awat shafi 444 zuwa 447, Biharul Anwar 63/476-478)

Qarin haske:
*Ya fi qarfi idan an tari ruwan saman kai tsaye ba ba wanda ya zuba akan rufi ba.*

✍️Huzaifa Bauchi

Sheikh Sayyid Abdullahi Ashura ya gabatar da jawabi, a wurin taron mu'utamar na qasa dake gudana a Kano, ya tattauna mau...
13/04/2025

Sheikh Sayyid Abdullahi Ashura ya gabatar da jawabi, a wurin taron mu'utamar na qasa dake gudana a Kano, ya tattauna maudu'i mai taken 'Alamomin bayyanar Imam Mahadi (AF) a wannan lokaci'.

23/03/2025

*SHARHIN DU'A'U ABI HAMZATAS SUMALIY*
Tareda Sayyid Abdullahi Ashura.

Zama na uku (3).

*BUQATUWAR DAN ADAM ZUWA GA ALLAH TA'ALA CIKIN DUKKAN SHA'ANONINSA NA DUNIYA DA LAHIRA*

Abinda ya k**ata mutum ya ce shi ne, ni bawan Allah ne, ni gajiyayye ne ban mallaki komai ba, ya Allah kana so ka ladaftar dani ne da azaba ina zan iya daukar wannan?.

Abinda ya k**ata mu fada kenan ba wai mu ce ya Allah ka kashe 'dana idan ka so ba, ko ka rusomin daki a kaina ba, ko ka saukarmin da dukkan bala'in da ka saukar akan Annabi Ayub (AS) ba, ko kuma ka jarabceni k**ar yadda ka jarabci Annabi Yaqub (AS) ba. 'Kallah! Kallah!!' a'a, mu nemi abinda yake qasa qasa sosai da irin wannan azaba, tunda mu za ka ga ko sauro ne ta zo idan ta so yin wasa da mu a cikin dare sai ka ga wannan dare ta zamo mana k**ar wuta, babu saqat, ba za ta barmu mu yi barci ba har zuwa asubah.

Inda a ce sauro ko quda guda daya za ta zo ta fara damun mutum, sai ka ga ya kai mata duka, ta tafi ta dawo, sai ka ga wannan kawai ya gajiyar da shi, yana ta tunani ya ya za a yi ya kori wannan quda?, ko ya za a yi ya k**ata ya kashe?, da ya yi qoqarin dukarta sai ka ga ta gudu, kuma shi bai mallaki fuka fukai ba ballantana ya ce zai bita, to sai ka ga mitum ya zama raunanne gaba ga sauro, ko gaba ga quda, saboda mu ba mu mallaki kowani irin dabara ko qarfi ba, ba zamu iya juran komai ba.

Imam (AS) da kansa yana cewa Ba zan iya juran uqubarka ba. Kuma wannan shi ne haqiqa.
Ya Allah mu bayinka ne kuma muna buqata daga gareka, duk abinda muke da shi naka ne, ba mu da komai ballantana mu ce ga wani abu namu muna neman ka ba mu wanda ba mu da shi.

Da wannan (kyakkaywan tarbiya) sai ka ga al'amuranmu na duniya sun zama da kyau, mu kuma nemi al'amarinmu na lahira, mu nemi gafara a wurin Allah sai ka ga rayuwarmu ta yi kyau, idan mu ka zama haka sai ka ga hatta duniyarmu ta gyaru, sai ka ga kasuwancin mu ta yi kyau.

Inda mutum zai ce duniya kam ta samu Alhamdulillah Allah ka ba mu lahira, kuma ya zama sosai hakan yake nufi ga Allah to me kake ganin zai faru? to tabbas zai bayyana qarya yake yi, ta ya ya?, ta inda zai rasa wani abu a wannan duniya, kai ko da digon ruwa ne aka hana shi (bai samu ba) to yanzu za ka ga ya fara kururuwa, saboda kawai bai samu kurbin ruwa ba.

Saboda haka komai kake da shi kana da buqata a wajen Allah, wannan shi ne tarbiya, saboda haka ba daidai ba ne mu riqa tunanin cewa al'amuran duniya ba muhimmai ba ne, wannan kuskure ne, a she ba mu buqatar ruwa? ba mu buqatar iskan shaqa ne? su ma ai duniya ne saboda haka kada ka rudi kanka da tunanim wai kai a duniya ba ka buqatar komai saboda tunanin kana tarbiya ko kana suluki, wannan wauta ne.

Duk da cewa shi iskan da ake shaqan ba saya ake yi ko a yi kwadago a samo ba kyauta ne, to amma bai da muhimmanci ne?, dukkan abubuwan da s**a zama mana lalura na dole a rayuwa to muna buqata, muna buqatar wannan iska da muke shaqa daga wajen Allah, kuma yana da kyau mu tabbatar a zuciyar mu cewa Allah yana ba mu.

Allah yajiqan Alhaji Hadi Al-Abhary ya ce: "Watarana a shekarun baya na zo zan yi tafiya zuwa Qazwin, sai ban samu mota ba, ko dana rasa mota sai na zauna a gaban wata babban mota (na diban kaya), a gefena kuma akwai wani mutum yana zaune, lokacin da mu ka isa mararrabar zuwa garin Karaj, kawai sai motar ta juya ta kifa cikin wani kogi mu ka nutse, sai numfashin mu ya dauke, ba don sun zo sun cece mu ba ana dan qara wani lokaci to da mun mutu, to a wannan hali ni ban mutu ba, amma ina jin irin kururuwan da mutumin dake gefena yake yi.

Tana iya yuwa mutum ya kalli wannan iska da ake numfashi ake shaqa a matasayin ba ta da wata kima, to amma inda zai fada cikin irin wannan yanayi da mu ka shiga, to zai san wani irin kima wannan iska take da shi, domin ita wannan iska dake bugawa tana raya matattu, domin idan ba ta buga ba to mutane za su mutu."

Sayyid Muhammad Muhsin ya ce: "Muna tsananin buqata zuwa ga wannan iska dake bugawa daya bayan daya, *shin yanzu kun yi la'akari sosai da fakrar wannan addu'a 'Ilahiy La Tuaddabniy Bi Uqubatika'? kun gane?*

✍️Huzaifa Bauchi

20/03/2025

*SHARHIN DU'A'U ABI HAMZATAS SUMALIY*
Tareda Sayyid Abdullahi Ashura

Zama na biyu (2)

Gazawar mutum wurin ya iya jure azabar Allah Ta'ala. Mu bayi ne shi kuwa bawa bai da iko akan komai, bai da juriya na iya daurewa ko da da soka allura a jikinsa ne, (ko da allura za a soka wa mutum za ka ga sai ya canja ya daddage, ballantana kuma azaban Allah Ta'ala.

A cikin Diwanin Ibn Farid yana cewa: "Ya Allah ka yimin azaba da duk abinda ka ga dama amma banda 'Bu'ud' (wato banda nisantani da kai)."

Wannan magana ta kebance shi ne, ba namu ba ne mu furta wannan, shi da yake furta wannan daidai ne da haqiqanin yadda yake rayuwa, ta yadda yake a wannan yanayi inda za a masa dukkan na'o'in azaba banda nesanta shi da Allah to zai gamsu da hakan, (saboda zamowarsa bawa ya yi fana'i). Ko an yanka shi gunduwa gunduwa ba zai ma ji ba.
Haka yake dangane da abinda Amirul muminin (AS) ya fada.

Wannan shi ne abinda ake cewa zancen da ya dace da haqiqanin halin da ake ciki.
Idan mutum bai mallaki wannan hali ba to bai dace ya yi irin wannan magana ba, domin idan bai kai wannan hali ba sai kuma ya ce 'Ya Allah saukarmin da azaba, to nan zai fara ganin azabar.

Sayyid Muhammad Muhsin ya ce: "Nakasance ina ziyartar Sayyid Jamaluddin a sati sau daya ko sau biyu, yakan min wa'azi idan naje, mutum ne mai yawan tsawatarwa akan barin yin sabo, ya kasance yana cewa "Shi abinda ya shafi tafiya zuwa ga Allah kacokaf dinsa ya dauru ne akan barin sabo"

Ya ce: "Watarana naje wajen Sayyid Jamaluddin a lokacin tsananin zafi, yana kwance a dakinsa hawa na sama, a lokacin an jarabce shi da musibu da bala'o'i daban daban, a ganganr jikinsa yana dauke da cututtuka guda biyu, daya daga ciki ita ce 'Burusta' an sanya masa wani bututu na roba ta wurin yake fitsari, an sanya wani kwantena a qasar gado ta wurin fitsarin yake zuba. Ciwo na biyu da yake jikinsa shi ne ciwon zuciya, kuma a lokacin ya wuce shekara casa'in a duniya, sannan a kansa akwai nauyi na basuss**a da yawa, ta yadda yake wuraren da yake cin bashin ma yanzu ba zai iya zuwa ya ci ba shi ba, kuma ya jinginar da gidansa akan dinare dari hudu saboda ya yi jinya ga wani dansa na wani ciwo da dan yake fama da shi, duk bayan wannan akwai wasu matsaloli da yake fama da su, a daidai wannan yanayi matarsa tana ta hayaniya domin tana so ta yi tafiya zuwa Iran ziyarar Imam Ridha (AS).

Amma duk da irin wadannan musifu da yake ciki na rashin kudi ga tsananin zafi da sauransu, amma ko dana shiga dakinsa sai na sameshi yana karanta Sahifa Sajjadiyya yana kuka, (dama shi mai yawan karanta Sahifa ne), yana ganina sai ya ce: "Zo ka zauna a nan" sannan ya yi dariya, ya ce min "Ya sayyid Muhammad shin ka sani ne ko ba ka sani ba?" sai na ce: "Ya sayyadi! menene kuma?" sai ya ce: "Duk abinda ka gani yana faruwa dani din nan to amma sai dai ni ina jin dadi da kwanciyar hankali da nutsuwa *Duk mutumim da ba shi da irfani to lallai ba shi da duniya da lahira."* ya ce abinda yasa ya fadamin wannan magana shi ne saboda yasan nasan musifun da yake ciki ne.

Dayyid Muhammad Mushin ya ce: "Duk lokacin da mutum yakai wani matsayi ga Allah duk bala'o'in da ke zuwa masa, baya ganin wani ne ya ke yi, abinda yake kallo kawai Allah ne yake saukar masa da wannan abu, kuma saboda tausayi da jinqai da rahama ne Allah yake yi masa haka.

*BALA'O'I DA JARABAWOWI DA SUKE SAUKA GA MATAFIYI ZUWA GA ALLAH KASHI BIYU NE:-*
Na farko shi ne. Ladaftarwa wanda ya ta'allaqa da azaba, k**ar yadda idan ana so mutum ya tsaya da kyau za a bugi qeyarsa, idan ya sake sunkuyar da kansa ko ya juya sai a sake dukan qeyarsa har sai ya tsayar da kansa yadda ake so.

Misali k**ar yadda za ka ga Jaki ko Doki an sanya masa abinci a gabansa amma sai ya daga kai ya je ya shiga gonar mutane, har sai an yi amfani da bulala an dawo da shi, idan ya dawo zuwa jimawa kadan sai ya sake kaucewa ya je ya shiga gonar mutane, sai an sake amfani da bulala an dawo da shi. Wannan misali ne na yadda ake ladaftar da mutum da azaba.

Na biyu shi ne ladaftarwa wanda bai da alaqa da uquba (wanda shi ne ake magana cikin wannan addu'a), misali idan mutum ya juyar da fuskarsa daga yadda ake so ya fiskanta, sai ya ji wani tattausar murya daga sama tana cewa masoyina meyasa ka karkatar da fuskarka? dawo da shi. To nan sai ka ga mutum ya fadaka ya juyo ya ce 'Astagfirullah'. (To ko a nan duk wanda aka ce masa masoyina to ai akwai tausasawa a ciki).

A irin wadannan darare na watan Ramadhan Mala'iku fa s**an yi ta kira har zuwa asubah suna cewa yaku masu sabo ku zo, qofofin rahama fa a bude suke, kada ku zama cikin gafalallu, ku zo garemu.
(Wannan yana daga cikin lokutan da Allah Ta'ala yake tarbiyan bayinsa).

Hakanan dararen juma'a ta yadda Mala'iku su ke kaiwa da komowa tundaga farkon dare har zuwa ketowar alfijir, suna masu kira, shin akwai mai neman gafara ne?, akwai mai addu'a ne da yake so a amsa masa?, za mu amsa addu'arsa. Ya ku masu sabo ku zo ana yin wannan.

Wannan ma ladaftarwa ne sai dai ba ladaftarwa ne na uquba ba, ladaftarwa ne da tausasawa, kuma shi ne abinda yafi dacewa da bayi, domin bawa bai isa ya jure wa azaban Allah ba, idan ba haka ba wa ya isa ya ce "Ya Allah ka daidaitani da azaba?."

Sayyid Jamaluddin matafiyi ne a hanyar Allah na shekaru masu yawa, kuma tsayayye ne a wannan hanya, ya dauki hawalwalu da yawa a wannan tafarki, amma shi kansa sai da ya koma wurin Amirul mumini (AS) yana kiran ya yi kuskure.

To kasan Imam Sajjad (AS) ya yi matuqar sani da wannan matsalar a bayyane take gareshi k**ar hasken rana, shi yasa yake addu'a da wannan kalma.

*Zamu ci gaba*

✍️Huzaifa Bauchi

20/03/2025

*SHARHIN DU'A'U ABI HAMZATAS SUMALIY*
Tareda Sayyid Abdullahi Ashura

Zama na daya (No. 1)

*GABATARWA:*
Bismillahir Rahmanir Raheem, mun dauki sharhin da Ayatullah Sayyid Muhsin Hussain Daharani ya yi, za mu yi karatu cikinsa, saboda ya qunshi abubuwa muhimmai,

marawaicin wannan addu'a shi ne Abi Hamzata.

*WANENE ABU HAMZATA?*
Sunansa Sabit Ibn Dinar, ya rayu da A'imma (AS) Imam Sajjad (AS), Imam Baqir (AS), Imam Sadiq (AS), a wasu riwayoyin ma har da Imam Kazim (AS), saboda haka ya rayu da A'imma (AS) kuma shi siqah din su ne daga cikin manyan marawaita, wanda A'imma (AS) suke da aminci da shi, mutum ne wanda ya kai qololuwa na daraja wajen kusanci da Allah ta yadda hatta Imam Sadiq (AS) yana fada dangane da Abu Hamzata cewa: "Abu Hamzata a zamaninsa k**ar Salmanul Farisi ne a zamaninsa." Mutum zai ga ne girman maganar ne idan yasan wanene Salmanul Farisi a zamaninsa, wurin kusanci da Allah, da abin da ya ba shi matsayi a wurin Amirul muminin (AS) da Sayyida Zahra (AS), wannan tundaga Mamzon Allah (S).

A wani riwaya Imam Ridha (AS) yana cewa: "Abu Hamzata a zamaninsa k**ar Lukmanul Hakim ne a zamaninsa."

Imam Sajjad (AS) ya kasance yana karanta wannan addu'a a dararen ramadan a lokacin sahur, (amma ana iya karantawa ko da ba lokacin).

*TARJAMA:*

*بسم الله الرحمن الرحيم*
*Da sunan Allah mai rahama mai jinqai*

*إلهي لاتؤدبني بعقوبتك*
*Ya Ubangijina kada ka ladabtar dani da azabarka*

*ولاتمكربي في حلتك*
*Kada kamin talala a cikin hilarka*

*من أين لي الخير يارب ولايوجد إلا من عندك؟*
*A ina zan samu alheri ya ubangiji, bayan kuma babu wurin da ake samunsa sai a wurinka?*

*ومن أين لي النجاة ولا استطاع إلا بك؟*
*A ina zan samu tsira (bayan) kuma babu wurin da ake samunta sai da kai?*

*لا الذي أحسن استغنى عن عونك ورحمتك*
*Wanda ya kyautata aiki ya zama nagartacce ko shi bai wadata ba daga barin neman taimakonka da rahamarka*

*ولاالذي أساء واجرأ عليك, ولم يرضك خرخ عن قدرتك.*
*Kuma ko wanda ya saba maka ya yi maka jur'a (tsaurin ido) bai fita daga cikin ikon ka ba, (bai fi qarfinka ba).*

*SHARHI:*
Kalmar *'Ilahiy'* wanda aka fara addu'ar da ita tana da banbanci da 'Allahumma' da 'Ya Allahu' domin 'Ilahiy' ta fi 'Ya Allahu da 'Allahumma' taushi, ta fiskacin nuna damfaruwar bawa da Ubangiji, ba kawai ya kira Ubangiji ba ne a'a, ya damfara kansa da shi, wato yana cewa "Ubangijina" ba cewa ya yi Ubangiji ba a'a, cewa ya yi Ubangijina, ko kuma Abin bautana, akwai tausasawa sosai a ciki.

Shi yasa za mu ga a cikin Du'a'u Kumail Amirul muminin (AS) ya yawaita fadin 'Ilahiy wa Maulay wa Sayyadi'.

Ko mutum za ka kira akwai banbanci tsakanin ka ce masa wane da kuma ka ce masa wanena, akwai shu'uri na cewa wanda ka kira naka ne, shi yasa ya fara wannan addu'a da Ilahiy.

*'La tuaddabniy bi uqubatika'* Kada ka ladaftar dani da uqubarka, ma'ana ya Ubangijina kada ka min tarbiya (horo) ta hanyar azaba, kada ka sanya azaba ya zama shi ne salon da za ka yi amfani da shi wajen tafiyantar dani.
(Kamar yadda mu ka sani Allah Ta'ala yana da hanyar ladaftarwa na azaba da hanyar da ba azaba ba, idan mutum ya saurari wa'azi ya ji nasiha ya gyaru ya ladaftu, to wannan hanya ne na ladaftarwa, akwai kuma hanya wanda mutum zai hawala ya gamu da musibobi da bala'o'i, sai hakan ya sanya shi ya ladaftu, ita ma wannan wata hanyar ce).

To shi Imam (AS) a nan yana roqon a ladaftar da shi ne amma ba da azaba ba.

*'Wala Tamkurbiy fiy hilatika'*
Ma'ana kada kamin talala saboda abinda yake wajenka na gwaninta da kuma zurfafa biyayya gareni.

Abinda za mu iya fahimta daga nan shi ne, Allah Ta'ala yana iya ladaftar da mutum da azaba, kuma zai iya yi wa mutum talala domin ya k**ashi cikin talala da ya yi masa, akwai buqatar mu fahimci menene ake nufi da talalan, mu kuma ga menene uquba na Allah Ta'ala da yake ladaftar da dan adam da ita.

Idan mu ka lura bai ce kada ka ladaftar dani ba kawai, cewa ya yi, kada ka ladaftar dani ne ta hanyar azabanka, a nan sai ya bayyana mana Allah Ta'ala yana da salo guda biyu na ladaftarwa, daya daga cikinsu shi ne ladaftarwa ta hanyar uquba, dayan kuma ba da uquba ba, shi yasa Imam (AS) yake roqon Allah Ta'ala ya ladaftar da shi amma ba da uquba ba, (idan muka lura ladaftarwan Allah Ta'ala yana tarbiyantarwa ne ga mutum, k**ar yadda yazo a hadisi cewa "Ubangijina ya tarbiyantar dani kuma ya kyautata ladaftarwan).

Sayyid Muhsin ya ce: "Wannan jumla tana da ban mamaki, kuma tana nuni zuwa ga wani abu mai girma, kenan tana iya yuwa Allah ya yi wa mutum ladabi ta hanyar uquba?. Abinda ake fahimta da ladaftawa shi ne, daidaita mutum a dawo da shi kan hanya madaidaiciya, da fadaka da farkawa, sabanin wadanda ba su samu tarbiya ba, lallai kowani muhalli yana da irin ladabinsa da ake buqata.

Wadannan da ba su sami tarbiya ba, ba zai zama suna kan hanya madaidaiciya ba sai ka ga sun wuce iyaka, ko sun gaza, ko sun yi gaggawan wani abu ko sun yi jinkirin yi, ko ya zama ba sa kiyaye ladabin wurin da s**a sami kansu a ciki, ko su kasance gafalallu dangane da al'amarin Allah Ta'ala, suna masu jahiltarsa su wadannan marasa tarbiya ba su da iddila'i akan sharidodin bauta da kuma hakkin ubangijiyanka na Allah Ta'ala.

Amma bawa mai ladabi shi ne wanda yasan wadannan abubuwa ya fahimce su, kuma ba zai buya ba dole ne bawa ya zama ya siffantu da ladabi datarbiya a hanyar bautar Allah, domin ba a ba da dama ga mara ladabi ya shiga cikin haramin Allah Ta'ala.

Idan Allah Ta'ala ya dubi bayinsa da rahama sai ya ladaftar da wadanda yake son su domin su sami damar shiga cikin haraminsa, domin wanda bai da ladabi ba ya shiga cikin haramin, (ka ga kenan bawa yana buqatar wannan ladabi daga Allah), sai ya bude musu qofa domin shiga wata duniyar da albarkar sunansa Rahamaniyyah.

Bayan wadannan ba yi sun zama masu tarbiya to zai zama akwai alaqa da ubangijisu a bisa asasi na ubudiyya sai ka ga bawa ya wayi gari ya yi nutso a cikin cancanta na tsayuwa a hanyar Allah da munajatinsa, sai ya samu dama wajen samun matsayi a haramin Allah Ta'ala.

Samun wannan matsayi baiyuwa, rabo ne kawai na bawan da ya lataftu, amma wadanda ba su samu wannan ladaftarwan ba su suna nesa ne da rahamar Allah. Ba sa cikin abinda za mu tattauna a karatun mu.

Ka ga kenan daga nan za mu fahimci cewa wannan ladaftarwan muhimmin al'amari ne ta yadda za mu ga Imam Sajjad (AS) yana cewa "Ya Allah kayimin ladabi, amma kada ka ladaftar dani da azabarka."
Kenan wajibi ne a samu wannan ladaftarwa, rashin ladaftarwan mummunae abu ne, shi yafi komai muni ga mutumin da yake suluki yake so ya isa zuwa ga Allah, domin idan bawa ya fita daga hanyar ladaftarwa ba zai kai zuwa ga haske da kishi na Allah ba, sai bawa ya fado daga dukkan muqamominsa, saboda haka wannan ladaftarwayana nufin tsayuwa daidai a matsayi ta yadda mutum ba zai yawaita magana ba, ba kuma zai qaranta magana ba, zai yi shi daidai ne, kuma ba zai taba siffanta ubangijinsa da wata siffa wanda ubangijin baya so ba, amma zai siffanta Allah Ta'ala ne da abinda yake daidai babu ragi babu qari.

Saboda haka a ladabi mutum ba zai ce 'Ilahiy Nafsi lakal fidha' ba, domin idan ya ce haka to Allah zai iya ce masa to zo ka sadaukar da kanka din a matsahin fansa gareni, saboda haka shi bawa mai ladabi yasan matsayinsa kuma zai tsaya ne akan matsayinsa wanda ya tabbata shi ne iyakarsa.

Akwai Sayyid Jamaluddin Golfagani (RH) yana daga cikin malaman Najaf kuma Marji'i ne, masani kuma ya sifffantu da tarbiya, kuma salihi ne. Ayatullah Sayyid Muhsin ya ce nakasance ina zuwa wurinsa

Watarana Sayyid Jamaluddin Golfagani yana fada wa Sayyid Muhsin cewa: "Wani lokaci nakan je na k**a jikin raga raga na kabarin Amirul muminin (AS) sai in girgiza da hannuna sannan na ce "Ya Imam! ka saukarmi da kowani irin bala'i, ka kawomin duk wani musiba da ka ga dama, amma ni dai ka biyamin buqatana kaza, na kan tafi a lokacin hunturu cikin tsananin sanyi, kafin kiran sallah da awa daya ko biyu, na tsaya a qofar wurin na jingina jikina da wannan qofa har sai an bude qofar sai na zama nine na farko da zan shiga, sai naje ina kuka ina cewa, a jarabceni da kowani irin talauci da kowani irin tsanani da kome ka ga dama, amma ni dai ka bani abinda nake nema"

Wannan magana da Sayyid Golfagani yake roqa dagaske yake fada ba qarya yake yi ba ko kuma yana fada ne saboda halin da ya sami kansa a ciki, misali yana cewa Ka yi min komai k**ar dutse ta fadomin a kai, ko a daddatsani gunduwa gunduwa, ko kuma talauci ya lullubeni, ko na rasa duk iyalina, ko kuma ka kawomin kowani irin bala'i da ya sauka akan Annabi Ayuba (AS), da duk wani bala'i da ya sauka akan Annabi Yaqub (AS) ko wasu Annabawa, amma ni dai ka bani buqatana.

sai kuwa alamomin wadannan abubuwa s**a fara zuwa sannu dannu, taqaitacciyar muqaddima sai ta zo ta fiskacin talauci, aka jarabce mu da qarancin kudi, babu abinda muke samu na kudi duk abinda muka taba baya yuwa.

Lokacin da muke a Najaf wurin neman ilimi ba abinda yake zuwa mana na tsawon watanni ba abinda muke samu, mu kanje mu ci bashi ne har sai da masu abinci s**a daina ba mu bashi, har muma kanmu mu ka ji kunyar zuwa mu ci bashi, ga kudin gidan haya na watanni ba mu biya ba, sai ga mai gida yazo ya yi fatali da kayan mu a waje, mu ka dibi kayanmu muka tafi wani daki a masallacin kufa muka sanya kayanmu mu ka mai da shi dakin mu, muna rayuwa ni da iyali a wajen, kuma wurin yana da nisa da makaranta, sai ya zamo ina zuwa Najaf da asuba na yi karatu, sannan na komo masallaci kufa cikin wannan tsanani na nisa.
(Shi Sayyid Golfagani mutum. ne lafiyayye).

Ya ce "A wannan hali sai matana ta fara raki tana cewa, wannan wani irin rayuwa ne, wannan wani irin musulunci ne wani irin addini ne ka ke yi? wannan wani irin mazhaba ne?, shin Allah ne ya umurceka da wannan quntatawa da ka shiga, ka tashi ka je ka nemi abin yi.

Sai ya ce mata "Ki tashi muje hadaran Amirul muminin (AS) ki fada masa duk wannan damuwar naki, a lokacin ana tsananin zafi, sai mu ka fita daga masallacin kufa zuwa Najaf, sai na nemi wani waje a gefe na zauna, ita kuma sai ta shiga haramin domin ta koka lamarinta ga Amirul muminin (AS), lokacin da ta dawo wurin ajiye takalma sai ta samu an sace takalminta (ya bata), tana tafiya qafarta babu takalmi, sai ta ce "A wajen Amirul muminin din ma ga abinda ya faru dani" a taqaice dai kawai hanyoyin mu sun gama toshewa, to yanzu ya za mu yi?, talauci ya yi mana yawa ya mamaye mu har zuwa wani matakin da ina zuwa (ina komawa) jikin raga raga na kabarin na girgiza na ce ya Amirul muminin na yi kuskure cikin abin da na roqa yanzu na janye maganata, ban mallaki kowani irin iko ba, ba za mu iya tabuka komai ba lallai na yi kuskure"

Sayyid Muhsin ya ce: "Lokaci da mutum yazo ya ce lallai na yi kuskure ya Allah, to a nan ne za a ce masa ya yi kyau tunda ka yi i'itirafi da kuskurenka.

Tattare da cewa wannan ba wani abin damuwa ba ne, kawai an dan toshe musu arziki ne.
To a nan abinda za mu fahimta shi Allah yakan bayyanar ne ga mutum cewa shin abinda ka fada dagaske ne kana so a saukar maka da bala'in?, za ka ga muna karantawa a cikin du'a'ul Kumail cewa: "Ya Ubangiji a qaddara na jure azabanka to ya zan yi na jure zafin rabuwa da kai, ya Ubangiji a qaddara na jure zafin wutarka to ya zan jure zafin rashin kallon karamcinka, Ya ubangiji qaddara yayin da ka saukarmin da azabarka ka jefani cikin jahannama ni zan yi haquri amma ya zan iya suranta kaina alhali na nesanta da kai, qaddara ka jefani a wuta ka jarabceni da azabobinka da zafin wutarka, to amma ya zan iya haquri da rashin kallo da za ka yi min na jinqai"

Shin dagaskw ne wannan abinda muke fada cikin wannan addu'a?

Imam Ali yana yin wannan addu'a muma sai ka ga mun zo muna yi muna cewa: "Ya Allah Aljannah na yara ne, mu munfi qarfin mu roqeka aljannah ko Hurul iyn, ko wasu bishiyoyi, mu abinda ya dace mu roqeka shi ne k**ala.
Haka abin yake dangane da tsoron wuta, muna cewa "Wannan na wadanda ba su samu wusuli ba ne, amma mu zababbu mun wuce wadannan matakai, mu yanzu Husuli zuwa ga Allah mu ke nema, amma dangane da azaban jahannama bai damemu ba"
To ba kunga abinda Imam Ali (AS) yake fada a cikin Du'a'u Kumail ba, to amma sai ka ga mun bude shafi daya biyu uku mun rufe mu ce mun karanta Du'a'u Kumail (cikin qanqanin lokaci), mun dauka abin ya qare a kalmomi ne na magana kawai, to Allah Ta'ala zai ce 'Tafaddhal' yanzu za a yi maka tambaya akan abinda ka roqa, wadannan da rusa da ka roqa yanzu za mu yi maka jarabawa, mu ga zuwa wani mataki ka ke.

*Zamu ci gaba*

✍️Huzaifa Bauchi

Address

Bauchi

Telephone

+2347069140703

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TASKAR JAWABAN SAYYID ABDULLAHI ASHURA BAUCHI posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share