13/06/2026
*Cigaban labarin Abdullahi mai itace tareda Hallalul Mashakil*
No. 2
Lokacin da Abdullah mai itace ya iso wannan kogo sai ya samu kogon wayam! ba komai, ko kirare kwara daya bai gani ba sai tarin toka wani akan wani. A nan Abdullahi mai itace ya tsaya cikin firgici da damuwa da baqin ciki, bai san me zai yi ba! ya dubu cikin dajin ya ga iskan damina duk ya ture bishiyoyi sun fado sun nutse cikin kwari, ko yadda zai dan kalaci itace babu, ga tsananin sanyi ga shekaru sunja gareshi.
Saboda tsananin abinda ya sameshi na damuwa da bakin ciki, duniya ta yi baqi a idanunsa, yayin da ya tuna iyalansa suna cike da fata na jiran ya dawo musu da abinci. Ya Allah! nan ya shiga damuwa mai tsanani ya fashe da kuka da kururuwa yana cewa: "Ya Rabbi Antal Ladiyfu bi ibadika, wa anta arhamar rahimin" sai ya fara karanta abinda matarsa ta sanar da shi wanda aka ce ta fada masa. Yana addu'a na tawassuli da Annabi (S) da iyalan gidansa (AS), yana addu'an bege na Hallalul Mashakil cikin khusu'i da karyewar zuciya da marairaicewa, yana ta maimaita "Nadi Aliyan Mazharal Aja'ib, Tajidhu Aunanlaka fin nawa'ib, kulli hammin wa gammin sayanjali bi Wilayatika Ya Ali, Ya Ali, Ya Ali"
Yana ta maimaitawa yana kuka har ya fadi sumamme a wurin.
Yana cikin wannan hali ne sai ga wani mahayin doki ya fiskanto shi ta gabar, yana haye akan farin doki, fuskarsa kamar 'Circle' din wata, kumatunsa suna haske, jikinsa yana qamshi da turaren miski da ambar, duk daji ya cike da qamshinsa, sai ya tsaya akan Abdullahi mai itace ya ce masa "Ta shi ya Abdullah" da Abdullahi ya farfado daga suma, sai wannan mahayin doki ya masa sallama shima ya mayar masa da sallama, mahayin doki ya ce masa "Tashi ya Abdullah buqatarka ta biya, (ya nuna masa wani gungumen dutse ya ce masa) dauki wannan kurman dutse ka sayar ka yi amfani da kudi" sai Abdullah ya ce: "Ya sayyadi! wanene kai? sai ya ce masa: "Nine Hallalul Mashakil, ka nemi taimakona ne na zo don na amsa maka, kuma kowace daren juma'a ka riqa tunawa dani kada ka manta dani" sai Abdullah ya ce: "Ya shugabana! shin kai ne Amirul muminin Aliyu bn Abiy Dalib?" ya ce masa: "Eh nine." Daga nan ya bace daga ganinsa.
A nan Abdullahi mai itace ya tashi ya shimfida mayafinsa, a qasa ya dibi wadannan kuramrn duwatsu kamar yadda Hallalul Mashakil ya masa umurni. Sai ya dawo gida bai je kasuwan ba ya ajiye wadannan duwatsu a can gefe, ya ba wa matarsa labari, bayan ya kwanta da daddare bayan dare ya nutsa, sai ya tashi domin biyan buqata (fitsari), nan fa ya fara ganin wani haske, take ya firgita ya gigice, sai ya kula ya tuna ashe fa duwatsun nan ne da aka sa ya debo, sai ya tashi daga biyan buqatarsa ya nufi wurin da ya ajiye mayafin da duwatsun suke ciki, nan zancen shugabansa ta tabbata ya zo wajen mayafin a lokacin nan kuwa wadannan duwatsu sun zama duwatsu masu daraja na daga yaqutu da izinin Allah da albarkar Hallalul Mashakil. Nan fa Abdullahi ya yi godiya ma Allah ya je ya tashi matarsa daga barci ya bata labari ya ce mata Allah Ubangiji ya azurtamu da albarkar Hallalul Mashakil Amirul mumini, ya karanta mata wannan aya "Allah yana azurta wanda ya ga dama ba tareda hisabi ba" haka s**a kwana cikin farin ciki.
Da gari ya waye sai ya dauki jauhari daya ya kai ga masu sayar da zinare ya sayar da ita a farashi mai yawa na kudi, ya saya wa iyalinsa da 'ya'yansa abinci da sabbin tufafi, ya dawo gida cike da farin ciki da fara'a, sannan ya gina sabon gida ya yalwata ma iyalansa. Fakirai da raunana da miskinai duk wanda ya zo yana ba su, har wanda bai zo ya koka masa ba, idan ya samu labari sai ya je ya taimaka masa. (To kaima mai karatu ka dau darasi lokacin da Allah ya buda maka to talakawa da miskinai su riqa samu a wurinka, kamar yadda Abdullahi mai ita ce ya ke yi).
A wannan yanayi nan da nan labarin Abdullahi mai itace ya cika gari ko ina zancensa ake, ya kasance duk daren juma'a yana karanta yabon Hallalul Mashakil, ya kuma yi sadaka mai yawa hadiya ga Amirul muminin (AS), ga baitotin ta yake yi👇
لـيـس يـدري بـكـنه ذاتـك ماهـو يـابـن عـم الـنـبـي إلا الله
لك معنى أجلى من الشمس لكن خبط العارفـون فيه وتاهو
قـلـت لـلقـائـلـيـن فـي انـك الله افــيـقــوا فـالله قـد ســواه
هـو مـتـشـكاة نـوره و الــتجـلـى سر قـدس جهـلتموا معناه
أظــهـــر الله ديــنــه بــعـلــي أيـن لا أيـن دـينـه لــو لاه
كــانـت الـنـاس قــبـلـه تـعــبــد الطاغوت ربا والجبت فيه إله
ونـبي الـهـدى إلى الله يـدعــوا هـم ولا يسـمـعـون منـه دعـاء
سله لما هـاجـت طغـاة قريــش مـن وقـاه بـنـفـسـه مـن فـــداه
لـو رأى مـثـلـه الـنـبي لـمـا وا خـاه حـيـا وأمـده وصـاه
قـام يـوم الـغدير يدعوا ألا من كنت مولى له فهـذا مولاه
مارتضاه الـنبي من قبل النفس ولـكـنـمـا الإلـه إرتـضـاه
نـاد عـلـيا مـظهـر العـجائـب تجـده عـونا لك في الـنوائـب
كـل هـم و غــم ســيـنـجـلـي بولايتك ياعلي ياعلي ياعلي
نـاد عـلـيا مـظهـر العـجائـب تجـده عـونا لك في الـنوائـب
كـل هـم و غــم ســيـنـجـلـي بولايتك ياعلي ياعلي ياعلي
اللهم بحق محمد المصطفى وعلي المرتضى وفاطمة الزهراء والحسن المجتبى والحسين الشهيد بكربلاء والتسعة المعصومين من ذرية الحسين اكشف عنا وعن كل مؤمن ومؤمنة كل ضر وبلاء وفاقة وكل هم وغم انك على كل شيء قدير وبالإجابة جدير وصلى الله على محمد وآله الطيبين الطاهرين
لي خمسة أهل العـبـا اطـفي بهم حـر الـوبا
المصطفى والمرتضى وفاطم وابنيهما النجبا
Bai gushe ba yana a haka har lokacin aikin hajji ya zo, sai wasu daga cikin abokansa da jama'arsa su ka yi niyar tafiya aikin hajji, shima sai ya yi niyar ya tafi tareda su, lokacin da zai tafi sai ya tara iyalansa ya ce musu "Zan yi tafiya domin sauke farali na musilunci don haka ina muku wasiya duk daren juma'a kada ku manta yabon Hallalul Mashakil, domin yana da hakki akanmu." sannan Abdullah ya yi tafiya tareda mutanensa.
Yayin da tafiyarsa ta cika kwanaki uku, sai yar Abdullah Makiyya ta ce wa mahaifiyarta "Ina so naje bayan gidan wanka (bayan gida ne kamar ka ce swimming pool)" sai mahaifiyar ta ce mata kina iya zuwa duk inda k**e so, nan kuwa wannan budurwar yarinya Makiyya ta tafi bayan gidan wanka na kudi, tareda da qawayenta.
Lokacin da ta shiga bayan gidan ta ga mata da yawa, a cikinsu sai ta hangi wata yarinya budurwa kyakkyawa mai kyan sura, sai ta tambayi wasu daga cikin matan cewa wacece wancen?........
Za mu cigaba.
Daga Taskar Sayyid Abdullahi Ashura
✍️Huzaifa Bauchi