TASKAR JAWABAN SAYYID ABDULLAHI ASHURA BAUCHI

TASKAR JAWABAN SAYYID ABDULLAHI ASHURA BAUCHI Domin samun Asrar da fawa'id na makarantar Ahlul Bait (As)

*Cigaban labarin Abdullahi mai itace tareda Hallalul Mashakil*  No. 2Lokacin da Abdullah mai itace ya iso wannan kogo sa...
13/06/2026

*Cigaban labarin Abdullahi mai itace tareda Hallalul Mashakil*
No. 2

Lokacin da Abdullah mai itace ya iso wannan kogo sai ya samu kogon wayam! ba komai, ko kirare kwara daya bai gani ba sai tarin toka wani akan wani. A nan Abdullahi mai itace ya tsaya cikin firgici da damuwa da baqin ciki, bai san me zai yi ba! ya dubu cikin dajin ya ga iskan damina duk ya ture bishiyoyi sun fado sun nutse cikin kwari, ko yadda zai dan kalaci itace babu, ga tsananin sanyi ga shekaru sunja gareshi.

Saboda tsananin abinda ya sameshi na damuwa da bakin ciki, duniya ta yi baqi a idanunsa, yayin da ya tuna iyalansa suna cike da fata na jiran ya dawo musu da abinci. Ya Allah! nan ya shiga damuwa mai tsanani ya fashe da kuka da kururuwa yana cewa: "Ya Rabbi Antal Ladiyfu bi ibadika, wa anta arhamar rahimin" sai ya fara karanta abinda matarsa ta sanar da shi wanda aka ce ta fada masa. Yana addu'a na tawassuli da Annabi (S) da iyalan gidansa (AS), yana addu'an bege na Hallalul Mashakil cikin khusu'i da karyewar zuciya da marairaicewa, yana ta maimaita "Nadi Aliyan Mazharal Aja'ib, Tajidhu Aunanlaka fin nawa'ib, kulli hammin wa gammin sayanjali bi Wilayatika Ya Ali, Ya Ali, Ya Ali"
Yana ta maimaitawa yana kuka har ya fadi sumamme a wurin.

Yana cikin wannan hali ne sai ga wani mahayin doki ya fiskanto shi ta gabar, yana haye akan farin doki, fuskarsa kamar 'Circle' din wata, kumatunsa suna haske, jikinsa yana qamshi da turaren miski da ambar, duk daji ya cike da qamshinsa, sai ya tsaya akan Abdullahi mai itace ya ce masa "Ta shi ya Abdullah" da Abdullahi ya farfado daga suma, sai wannan mahayin doki ya masa sallama shima ya mayar masa da sallama, mahayin doki ya ce masa "Tashi ya Abdullah buqatarka ta biya, (ya nuna masa wani gungumen dutse ya ce masa) dauki wannan kurman dutse ka sayar ka yi amfani da kudi" sai Abdullah ya ce: "Ya sayyadi! wanene kai? sai ya ce masa: "Nine Hallalul Mashakil, ka nemi taimakona ne na zo don na amsa maka, kuma kowace daren juma'a ka riqa tunawa dani kada ka manta dani" sai Abdullah ya ce: "Ya shugabana! shin kai ne Amirul muminin Aliyu bn Abiy Dalib?" ya ce masa: "Eh nine." Daga nan ya bace daga ganinsa.

A nan Abdullahi mai itace ya tashi ya shimfida mayafinsa, a qasa ya dibi wadannan kuramrn duwatsu kamar yadda Hallalul Mashakil ya masa umurni. Sai ya dawo gida bai je kasuwan ba ya ajiye wadannan duwatsu a can gefe, ya ba wa matarsa labari, bayan ya kwanta da daddare bayan dare ya nutsa, sai ya tashi domin biyan buqata (fitsari), nan fa ya fara ganin wani haske, take ya firgita ya gigice, sai ya kula ya tuna ashe fa duwatsun nan ne da aka sa ya debo, sai ya tashi daga biyan buqatarsa ya nufi wurin da ya ajiye mayafin da duwatsun suke ciki, nan zancen shugabansa ta tabbata ya zo wajen mayafin a lokacin nan kuwa wadannan duwatsu sun zama duwatsu masu daraja na daga yaqutu da izinin Allah da albarkar Hallalul Mashakil. Nan fa Abdullahi ya yi godiya ma Allah ya je ya tashi matarsa daga barci ya bata labari ya ce mata Allah Ubangiji ya azurtamu da albarkar Hallalul Mashakil Amirul mumini, ya karanta mata wannan aya "Allah yana azurta wanda ya ga dama ba tareda hisabi ba" haka s**a kwana cikin farin ciki.

Da gari ya waye sai ya dauki jauhari daya ya kai ga masu sayar da zinare ya sayar da ita a farashi mai yawa na kudi, ya saya wa iyalinsa da 'ya'yansa abinci da sabbin tufafi, ya dawo gida cike da farin ciki da fara'a, sannan ya gina sabon gida ya yalwata ma iyalansa. Fakirai da raunana da miskinai duk wanda ya zo yana ba su, har wanda bai zo ya koka masa ba, idan ya samu labari sai ya je ya taimaka masa. (To kaima mai karatu ka dau darasi lokacin da Allah ya buda maka to talakawa da miskinai su riqa samu a wurinka, kamar yadda Abdullahi mai ita ce ya ke yi).

A wannan yanayi nan da nan labarin Abdullahi mai itace ya cika gari ko ina zancensa ake, ya kasance duk daren juma'a yana karanta yabon Hallalul Mashakil, ya kuma yi sadaka mai yawa hadiya ga Amirul muminin (AS), ga baitotin ta yake yi👇

لـيـس يـدري بـكـنه ذاتـك ماهـو يـابـن عـم الـنـبـي إلا الله
لك معنى أجلى من الشمس لكن خبط العارفـون فيه وتاهو
قـلـت لـلقـائـلـيـن فـي انـك الله افــيـقــوا فـالله قـد ســواه
هـو مـتـشـكاة نـوره و الــتجـلـى سر قـدس جهـلتموا معناه
أظــهـــر الله ديــنــه بــعـلــي أيـن لا أيـن دـينـه لــو لاه
كــانـت الـنـاس قــبـلـه تـعــبــد الطاغوت ربا والجبت فيه إله
ونـبي الـهـدى إلى الله يـدعــوا هـم ولا يسـمـعـون منـه دعـاء
سله لما هـاجـت طغـاة قريــش مـن وقـاه بـنـفـسـه مـن فـــداه
لـو رأى مـثـلـه الـنـبي لـمـا وا خـاه حـيـا وأمـده وصـاه
قـام يـوم الـغدير يدعوا ألا من كنت مولى له فهـذا مولاه
مارتضاه الـنبي من قبل النفس ولـكـنـمـا الإلـه إرتـضـاه
نـاد عـلـيا مـظهـر العـجائـب تجـده عـونا لك في الـنوائـب
كـل هـم و غــم ســيـنـجـلـي بولايتك ياعلي ياعلي ياعلي
نـاد عـلـيا مـظهـر العـجائـب تجـده عـونا لك في الـنوائـب
كـل هـم و غــم ســيـنـجـلـي بولايتك ياعلي ياعلي ياعلي
اللهم بحق محمد المصطفى وعلي المرتضى وفاطمة الزهراء والحسن المجتبى والحسين الشهيد بكربلاء والتسعة المعصومين من ذرية الحسين اكشف عنا وعن كل مؤمن ومؤمنة كل ضر وبلاء وفاقة وكل هم وغم انك على كل شيء قدير وبالإجابة جدير وصلى الله على محمد وآله الطيبين الطاهرين
لي خمسة أهل العـبـا اطـفي بهم حـر الـوبا
المصطفى والمرتضى وفاطم وابنيهما النجبا

Bai gushe ba yana a haka har lokacin aikin hajji ya zo, sai wasu daga cikin abokansa da jama'arsa su ka yi niyar tafiya aikin hajji, shima sai ya yi niyar ya tafi tareda su, lokacin da zai tafi sai ya tara iyalansa ya ce musu "Zan yi tafiya domin sauke farali na musilunci don haka ina muku wasiya duk daren juma'a kada ku manta yabon Hallalul Mashakil, domin yana da hakki akanmu." sannan Abdullah ya yi tafiya tareda mutanensa.

Yayin da tafiyarsa ta cika kwanaki uku, sai yar Abdullah Makiyya ta ce wa mahaifiyarta "Ina so naje bayan gidan wanka (bayan gida ne kamar ka ce swimming pool)" sai mahaifiyar ta ce mata kina iya zuwa duk inda k**e so, nan kuwa wannan budurwar yarinya Makiyya ta tafi bayan gidan wanka na kudi, tareda da qawayenta.

Lokacin da ta shiga bayan gidan ta ga mata da yawa, a cikinsu sai ta hangi wata yarinya budurwa kyakkyawa mai kyan sura, sai ta tambayi wasu daga cikin matan cewa wacece wancen?........

Za mu cigaba.

Daga Taskar Sayyid Abdullahi Ashura

✍️Huzaifa Bauchi

Wallahi na yi kuka a daidai wannan wurin😭😭😭An rawaito cewa wani bawan Allah da ake kira Abdullahi me itace, ya kasance m...
11/06/2026

Wallahi na yi kuka a daidai wannan wurin😭😭😭

An rawaito cewa wani bawan Allah da ake kira Abdullahi me itace, ya kasance mumini ne amma talaka ne sosai, aikinsa kullum yakan tafi jeji kan duwatsu ya yo itace iya abinda zai iya, sannan ya dauko itacen ya kai kasuwa ya sayar a farashin Dirhami da bai kai goma ba. (Mu auna rayuwarmu da wannan bawan Allah mai sana'ar yankar itace ta yadda ba ya iya ciyarda iyalansa kullum sai ya shiga daji ya yo itace yaje kasuwa ya sayar a farashi mai sauki sannan ya kawo abinda za a ci a gidansa. Shin tsananin rashinka ya kai na wannan bawan Allah?).

A haka Abdullahi yana mai 'Qana'a' da kuma yarda d iya arzikin da Allah ya yi masa, tattare da cewa yana da tarin iyalai wadanda sun kai 7 ko sama da haka, dukkansu maza da mata ne wadanda ba su girma sun kawo qarfi ba, a haka yake gudanar da rayuwarsa da wannan aiki.

Matarsa ta yi Bakance akan duk juma'a sai ta zo zauren gida tana addu'ar Allah ya nuna mata wani daga cikin waliyansa domin ta roqi wannan waliyi ya musu addu'an Allah ya rabasu da wannan qunci ya ba su mafita, ta na yin haka har sai da ta kai juma'a arba'in (wato sati 40).

Watarana tana tsaye a zauren gida tana roqon Allah tana tawassuli da Manzon Allah (S) da iyalan gidansa (AS), sai ta hango wani mutum daga nesa dogo yana da furfura, ko da ya zo daidai da ita sai ya ce mata: "Idan mijinki Abdullahi ya dawo ki fada masa cewa duk lokacin da wani tsanani ya sameshi to ya yi tawassuli da Manzon Allah (S) da iyalan gidansa (AS), kuma ya yi addu'a na bege da kewa na 'Hallalul mashakil' (mai warware miskiloli), ki ce ya riqa karanta 👇

*"Nadi Aliyan Mazharal Aja'ib, Tajidhu Aunanlaka fin Nawa'ib, Kullu Hammin wa Gammin Sayanjali Bi Wilayatika Ya Aliy Ya Aliy Ya Aliy"*
Wannan ita ce addu'a na kewa na 'Hallalul mashakil' (Amirul muminin).

"Ki ce masa ya yi ta maimaitawa da yawa buqatarsa za ta biya" daga nan sai wannan mutum ya bace daga ganinta.
Lokacin da mijinta ya dawo sai ta ba shi labarin siffofin mutumin da ya zo, sai Abdullah mai itace ya ce mata: "Ke! wannan fa Khidir (AS) ne, shin ya fada miki wani abu ne?" sai ta ce eh, sai ta ba shi labarin abinda ya fada mata, daganan sai Abdullah mai itace ya kiyaye wannan addu'a.

Washe gari sai ya cigaba da sana'arsa kamar yadda ya saba na zuwa daji yana saran itace yana zuwa ya sayar, amma a lokacin an shiga zafi, sama ta fara alamun damina na saukan ruwan sama.

Abdullahi ya ta fi daji yana saran itace sai ya yi tunani ya fada a ransa cewa "Da alama fa za a fara damina (ruwan sama yana hanya) nan da wasu 'yan kwanaki, idan ruwan sama ta sauka ta jiqe itatuwa ya zan yi da aikina, a ina zan sami busassun itatuwa da zan sayar?, ga shi kuma shekaruna sun ja jiki ya yi rauni, to mai zai hana na tara wasu itatuwa na ajiye a cikin kogon wannan dutse ta yadda ko ruwa ya zo ba zai jiqa itacena ba?, ga shi lokacin zai zama itace ya yi daraja saboda ba a samun bushash'she.

Saboda haka sai Abdullahi ya tara itace mai yawa, ya boyesu a cikin wani kogo saboda ruwan sama, ya kuma sanya alama a wurin, ya debo wasu a ciki ya kai kasuwa ya siyo abinci ya dawo gida, ya ba wa matarsa labarin abinda ya yi, sai ta yi farin ciki ta ce wallahi ka yi dabara.

Ai kuwa bayan yan wasu kwanaki kadan sai ga iska alamar ruwan sama ya fara sauka wuri ya yi sanyi, sai kuwa ga manya manyan hadirin ruwa ta yadda mutane ba su samun daman fita aiki saboda saukan ruwa, amma shi Abdullah yana, zaune a gida (cikin nutsuwa) sakamakon yana da dan wasu itace da ya debo, to shi ma sai wanda ya debo ta qare.

Ruwan sama ya dauke babu ruwa hadiri ya tafi, gari babu busassun itatuwa duk sun jiqe jagam!, saboda haka dole ana neman busassun itace, nan fa Abdullah cikin farin ciki ya ce wa matarsa "Yanzu zanje kogon dutse na debo abinda na tara na boye saboda ruwan sama, don na kawo shi kasuwa, 😍 sai ya fita yana mai alqawari wa iyalansa cewa yanzu zanje na dawo da abinci😍😍😍

*YA ALLAH!*
Cikin kaddarar Allah da hukuncin Allah wanda shi Abdullah bai sani ba shi ne, cikin wadannan kwanaki da aka yi ruwan sama na sauka ashe watarana hanya ta biyo da wasu ayarin matafiya zuwa ta jikin wannan dutse wanda Abdullah ya boye itatuwansa a ciki, suna neman mafaka saboda ruwa, saboda haka sai s**a shiga cikin wannan kogo, nan fa s**a farmaki itacen nan suna qonawa don su ji dumi, suna dafa ruwa, ba su bar komai ba sai da wannan itatuwa s**a qare kakakaf!.

Lokacin da Abdullahi mai itace ya iso wannan kogo....

Za mu cigaba

Daga Taskar Sayyid Abdullahi

✍️Huzaifa Bauchi

Sheikh Sayyid Abdullahi Ashura ya ziyarci Darur Rahamah.
04/06/2026

Sheikh Sayyid Abdullahi Ashura ya ziyarci Darur Rahamah.

19/03/2026

*ABU NA FARKO DA MUTUM ZAI YI AMFANI DASHI RANAR IDI DA SAFE SHINE TURBA HUSSAINIYYA; DOMIN TANA MAGANCE DUKKAN CUTUTTUKA NA ZAHIRI DA BAƊINI DA SAMUN ARZIKI*
Daga TASKAR SAYYID ABDULLAHI ASHURA
.. A lokacin da mutum yayi niyyar tafiya masallacin idi anso yaci wani abu, to kuma abincin da ake so mutum ya fara dashi shine TURBATU HUSSAINIYYA.

Kafin ka sanya a bakin naka anso ka karanta wannan addu'ar "Bismillahir Rahmanir Raheem. Allahumma Rabbi Hazihi Turbatul Mubaraka Aɗɗahira, Wa Rabbu Nurillazi Unzala fihi, Wa Rabbu Jasdil Lazi Sakana Fihi, Wa rabbul Mala'ikati Muwakkilina Bihi, Salli Ala Muhammad Wa Aali Muhammad Waj'al Hazad diyn Fi Amanan Min Kulli Kaufin Wa Shifa'an Min Kulli Da'in Kaza Wa Kaza (sai mutum ya lissafo matsalolinsa na cuwuka wanda s**a dameshi da damuwowi sai ya ambato su)".

Bayan an sa TURBA a baki an kurɓi ruwa an haɗiye to sai akaranta wannan addu'ar "Bismillahi Wa Billahi, Allahummaj'alhu Rizƙan Wasi'an Wa Ilman Nafi'an Wa Shifa'an Min Kulli Da'in Wa Subnin Innaka Ala Kulli Shai'in Ƙadir. Allahumma Rabbi Hazihil Turbatul Mubaraka Wa Rabbul Wasiyyil Lazi Waradhu, Salli Ala Muhammad Wa Aali Muhammad Waj'al Hazal Dini li Shifa'an Min Kulli Da'in Wa Amanan Min Kulli Kaufin Wa Izzan Min Kulli Zillin Wa Aafiyatin Min Kulli Su'in Wa Ginin Min Kulli Fakrin".

Imam Sadik (As) yace "Wanda ya sa a baki amma bai karanta wannan addu'ar to lallai zaiyi wuya ta masa tasiri, don haka yana da kyau a karanta su duka baki ɗaya".

Idan mukayi la'akari wanann aikin zai baka arziki na dindindin da Ilimi da waraka na har abada, don haka muyi kokari sosai wajen ganin mun aikata su akan lokaci.

Allah ya datar damu ya mana muwafaƙa ya karɓi ibadunmu ya gafarta mana zunubbanmu baki ɗaya bi haƙƙi Muhammad wa Aali Muhammad.

-Saifullah Ningi ne ya naƙalto muku daga jawabin Sayyid Ashura da yayi akan ayyukan Ƙaramar Salla na shekarar 2022 a zaurem WhatsApp na Taskar Sayyid Ashura.

مِّنَ الْمُؤْمِنِينَ رِجَالٌ صَدَقُوا مَا عَاهَدُوا اللَّهَ عَلَيْهِ ۖ فَمِنْهُم مَّن قَضَىٰ نَحْبَهُ وَمِنْهُم مَّن يَن...
19/03/2026

مِّنَ الْمُؤْمِنِينَ رِجَالٌ صَدَقُوا مَا عَاهَدُوا اللَّهَ عَلَيْهِ ۖ فَمِنْهُم مَّن قَضَىٰ نَحْبَهُ وَمِنْهُم مَّن يَنتَظِرُ ۖ وَمَا بَدَّلُوا تَبْدِيلًا

SANARWA!Assalamu Alaikum. In sha Allah gobe Asabar 28/02/2026 za a fara haska live na KARATUN HAQA'IQ MINAL QUR'AN wanda...
27/02/2026

SANARWA!

Assalamu Alaikum.
In sha Allah gobe Asabar 28/02/2026 za a fara haska live na KARATUN HAQA'IQ MINAL QUR'AN wanda Sayyid Abdullahi Ashura ke gabatarwa kullum ƙarfe 3:30 zuwa 5:30 A SHAFUN TELEGRAM.

Ga link ɗin da zaku samu karatun kai tsaye in sha Allah https://t.me/+c_xuJdyJ-Tc0YmM0

Allah ubangiji ya amfanar da mu da abubuwan da muke ji.

*Ilimi Haske Ne, Allah Ya Na Jefa Wannan Haske A Zuciyar Wanda Ya So*....العلم نور، يقذفه الله في قلب من يشاء

27/02/2026

Idan wani abu naka ya bata...

Daga muhallin karatun littafin Haqa'iqu Minal Kur'anPhoto by Hamisu Ladan
27/02/2026

Daga muhallin karatun littafin Haqa'iqu Minal Kur'an

Photo by Hamisu Ladan

25/02/2026
25/02/2026

Wani yanki na karatun littafin Haqa'iqu Minal Kur'an

Address

Bauchi

Telephone

+2347069140703

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TASKAR JAWABAN SAYYID ABDULLAHI ASHURA BAUCHI posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share