Alpu-Hausa24

Alpu-Hausa24 wannan shafin jaridar hausa24.com
(226)

06/08/2026

HIDIMAR DSP. DR. Barau I. Jibrin PHD. CFR. (MALIYA) GA AL'UMMAR SA DA YAKE WAKILTA A ZAUREN MASALISSA.

KYAKKYAWAN WAKILCI NA AUNA SHUGABA DA AIKINSA

A duk lokacin da ake maganar wakilci nagari, ana kallon irin ayyukan da shugaba ya aiwatar domin amfanin al'umma. A Kano Ta Arewa, da dama na ganin Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, ya taka rawa wajen aiwatar da ayyukan ci gaba a fannoni daban-daban.

A bangaren ilimi, an gudanar da ayyukan tallafawa makarantu, samar da kayan koyo da kuma buɗe damar karatu ga matasa. A noma kuma, dubban manoma sun amfana da rabon takin zamani kyauta domin ƙarfafa noma da bunƙasa samar da abinci.

Haka kuma, an aiwatar da shirye-shiryen tallafawa matasa da 'yan kasuwa, tare da wasu ayyukan da s**a shafi inganta harkokin lafiya da raya al'umma.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na bayyana cewa irin waɗannan ayyuka na ci gaba su ne ke ƙara fito da bambancin shugabanci mai amfani ga jama'a, domin a cewarsu, kyakkyawan wakilci ana ganinsa ne a aikace, ba a magana kaɗai ba.

Allah Ya ci gaba da ba shugabanni hikima da ƙarfin guiwar yi wa al'umma hidima.

Allah kalli Barau Maliya

GINA ILMI TUN DAGA TUSHE: YADDA SANATA BARAU YA SAKE FASALTA ILIMIN FIRAMARE DA SAKANDARE A KANO TA AREWAIlimi shi ne gi...
05/08/2026

GINA ILMI TUN DAGA TUSHE: YADDA SANATA BARAU YA SAKE FASALTA ILIMIN FIRAMARE DA SAKANDARE A KANO TA AREWA

Ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban kowace al'umma, kuma gina shi tun daga tushe na daga cikin manyan hanyoyin tabbatar da kyakkyawar makoma ga matasa. Wannan ne ya sa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, , ya mayar da hankali wajen bunƙasa ilimin firamare da sakandare a faɗin Kano ta Arewa.

A cikin shekaru da s**a gabata, makarantu da dama sun amfana da manyan ayyukan inganta ilimi da s**a haɗa da gina sabbin ajujuwa domin rage cunkoso da samar da ingantaccen yanayin koyo. Haka kuma, an samar da kujerun zama ga ɗalibai da malamai, lamarin da ya ƙara wa makarantu karsashi wajen gudanar da ayyukan koyarwa.

Baya ga haka, dubban ɗalibai sun amfana da rabon littattafan karatu, yayin da hukumomin ilimi s**a samu kayan aikin koyarwa domin ƙarfafa ingancin tsarin ilimi.

Shugabannin makarantu ma ba a bar su a baya ba, domin an samar musu da injunan aiki da za su sauƙaƙa gudanar da harkokin makarantu. Haka kuma, hukumomin ilimi sun samu motoci domin inganta sa ido da gudanar da ayyukansu, yayin da malamai s**a amfana da wayoyin Android domin amfani da fasahar zamani wajen koyarwa.

Waɗannan ayyuka sun nuna cewa zuba jari a ilimi ba kawai gina gine-gine ba ne, har ma da samar da kayan aiki da hanyoyin da za su inganta koyarwa da koyo.

Masu lura da al'amuran ilimi na ganin irin waɗannan shirye-shirye na taimakawa wajen ɗora ilimin Kano ta Arewa a kan ingantacciyar turba, tare da gina kyakkyawar makoma ga al'umma ta hanyar ƙarfafa ilimi tun daga matakin farko.

Lallai, gina ilimi tun daga tushe na nufin gina makomar al'umma, kuma wannan na daga cikin muhimman ayyukan da ake dangantawa da Sanata Barau I. Jibrin a Kano ta Arewa.

HIDIMAR DA SANATA BARAU YAYIWA MAKARANTUN FIRAMARE DA SAKANDIRE NA FAƊIN KANO TA AREWA (GINA ILMI TUN DAGA TUSHE) Mu leƙ...
05/08/2026

HIDIMAR DA SANATA BARAU YAYIWA MAKARANTUN FIRAMARE DA SAKANDIRE NA FAƊIN KANO TA AREWA (GINA ILMI TUN DAGA TUSHE)

Mu leƙa Makarantun firamare da sakandare dake faɗin Kano ta Arewa domin ganin irin hidimar da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Sanata mai wakiltar Kano ta Arewa, Alhaji Dakta Barau I. Jibrin PhD. Cfr. Yayi k**a daga kan Principal's, Headmaster's Malaman Makarantar da Ɗaliban Makarantar sannan su kansu Makarantun yadda ya dawo dasu cikin hayyacin su a faɗin Kano ta Arewa.

Gina Ajujuwa (Block's a Makarantun Primary da Sakandare

Raba Kujerun Zama na Ɗalibai da Malamai a dukkanin Makarantun Firamare da Sakandare dake Kano ta Arewa.

Raba Littattafai ga Dukkanin Ɗaliban Makarantun Firamare da sakandare na Kano ta Arewa.

Rabawa Hukumar Ilimi kayan Aikin koyarwa

Raba Mashina ga Hedimastoci
Raba Motoci ga Hukumomin Ilmi
Rabawa Malamai Wayoyin Android

Wannan kaɗan ne daga cikin irin hidimar da yayiwa Ilmin Firamare da Sakandare a faɗin Shiyyar Kano ta Arewa.

Allah ya sakawa Dsp. Dr. Barau da alheri.

Duk Wanda Ya San Sanata Barau, Ya San Ba Ya Son Rigima!Idan da gaske kana ƙaunar Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), to ka ...
25/07/2026

Duk Wanda Ya San Sanata Barau, Ya San Ba Ya Son Rigima!

Idan da gaske kana ƙaunar Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), to ka yi koyi da halayensa.

Sanata Barau ba ya gina siyasa da zagi, faɗa ko ƙiyayya. Ya fi son zaman lafiya, haɗin kai, mutunta kowa da kuma aiki domin ci gaban al'umma.

Saboda haka, kada a yi amfani da sunansa wajen tayar da husuma ko cin mutuncin wani. Gaskiyar goyon baya ita ce nuna ɗabi'a ta gari, haƙuri da natsuwa k**ar yadda jagoranka yake yi.

Mu yaɗa zaman lafiya, mu guji rigima, mu gina haɗin kai. Wannan ita ce hanyar Sanata Barau (Maliya).

Hours ago, I served as the Special Guest of Honour at the New Horizons College Speech and Prize-Giving Day for the Class...
25/07/2026

Hours ago, I served as the Special Guest of Honour at the New Horizons College Speech and Prize-Giving Day for the Class of 2026 in Minna, Niger State.

I congratulate the graduating students for completing this important phase of their academic journey, as well as other students who distinguished themselves in various examinations.

I also commend the management, teachers and parents of this great institution for their dedication and commitment to excellence.

To the graduating class, this is not the end but the beginning of a greater journey. As you proceed to higher institutions, remain focused, disciplined, and committed to both academic excellence and good character. The knowledge and values you have acquired here should guide you as you strive to become professionals and responsible citizens who will contribute meaningfully to society.

I also paid tribute to the founders of New Horizons College for leaving behind a remarkable legacy of learning and character development. Such institutions serve not just individuals, but humanity as a whole.

May Allah bless our students, grant them success in their future endeavours, and continue to strengthen this great institution.

Congratulations once again to the Class of 2026.

I also attended the Annual Speech/Prize Giving Day and Graduation Ceremony of Abu Turab Islamic School.

It was a privilege to join students, parents, teachers, and well-wishers in celebrating another important milestone in the lives of the students.

The event was not only a moment of recognition of academic excellence, but also a reminder of the enduring value of discipline, character, and sound education.

I congratulate the students and their families, and I pray for their continued success in all future endeavours.

I received members of the Kano North Vice Chairmen Forum, led by their leader, Abubakar Sule Babangida, the Vice Chairma...
24/07/2026

I received members of the Kano North Vice Chairmen Forum, led by their leader, Abubakar Sule Babangida, the Vice Chairman of Bichi Local Government, at my residence in Abuja.

During the visit, the vice chairmen, who are from the 13 Local Government Areas of my Senatorial District, commended me for the numerous developmental projects executed across the zone and the state at large.

I sincerely appreciate their visit and the kind words of encouragement they offered. I urge them to remain steadfast in promoting good governance, unity, and excellent service delivery at the grassroot for the progress and prosperity of our people.

As leaders at the grassroots, their role remains critical in deepening democratic values and ensuring that government initiatives reach the people effectively.

I assured them of my continued commitment to initiating people-oriented legislation and interventions that will directly impact the lives of our constituents.

Together, we will continue to work in the interest of our people, with dedication, sincerity, and a shared vision for sustainable development across Kano North.

Babu Wata Rashin Fahimta Tsakanin Sanata Barau I. Jibrin, PhD. Cfr. da Mawaki Dauda Kahutu Rarara Ofishin Darakta Janar ...
21/07/2026

Babu Wata Rashin Fahimta Tsakanin Sanata Barau I. Jibrin, PhD. Cfr. da Mawaki Dauda Kahutu Rarara

Ofishin Darakta Janar na Sashen Kafofin Sada Zumunta na Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Hon. Basiru Yusif Shuwaki, yana sanar da daukacin al'umma, musamman magoya bayan jam'iyyar APC, cewa babu wata rashin fahimta ko saɓani tsakanin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Barau I. Jibrin, CFR, da fitaccen mawaki, Dauda Rarara. Ya ƙara da cewar Mai girma Sanatan yafi maida hankali kan jawowa Shugaban ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da Jam'iyyar APC cigaba da Nasara musamman gabatowar zaɓen duka gari na 2027.

Daraktan ya ƙara da cewae abin takaici ne yadda wasu ke amfani da kafafen sada zumunta wajen ƙirƙira da yaɗa labaran ƙarya domin haddasa ruɗani da rarrabuwar kai tsakanin magoya baya. Irin waɗannan jita-jita ba su da tushe, kuma ba sa wakiltar gaskiyar abin da ke tsakanin waɗannan manyan mutane biyu, waɗanda dangantakarsu ta ginu ne a kan mutunta juna, fahimta da kuma haɗin kai.

Ofishin Hon. Basiru Yusif Shuwaki yana kira ga dukkan magoya bayan Sanata Barau da na Mawaki Dauda Rarara da kada su bai wa masu neman tayar da fitina damar cimma manufarsu. Mafi girman martani ga irin waɗannan jita-jita shi ne ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai, haƙuri da kuma mutunta juna.

Muna kuma jan hankalin masu amfani da kafafen sada zumunta da su riƙa tantance sahihancin duk wani bayani kafin yaɗa shi. Ya k**ata a guji duk wani abu da zai iya raunana haɗin kan jam'iyyar APC ko ya jawo saɓani a tsakanin magoya baya.

Ofishin ya sake jaddada cewa babu wata matsala tsakanin Sanata Barau I. Jibrin da Dauda Rarara, kuma duk wani labari da ke cewa akasin haka ƙarya ce da aka ƙirƙira domin tayar da hankali.

Muna kira ga daukacin al'umma da su yi watsi da waɗannan jita-jita, su ci gaba da bai wa shugabanci cikakken goyon baya, tare da kare haɗin kai da martabar jam'iyyar APC.

Allah Ya ƙara haɗa kanmu, Ya ba Najeriya zaman lafiya da ɗorewar ci gaba.

An fitar da wannan sanarwa daga:

Ofishin Darakta Janar na Sashen Kafofin Sada Zumunta
Hon. Basiru Yusif Shuwaki
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya

Barau Ya Buƙaci Ƙarin Matakan Tsaro Bayan Barazanar Kachalla Maha a KanoMataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ba...
20/07/2026

Barau Ya Buƙaci Ƙarin Matakan Tsaro Bayan Barazanar Kachalla Maha a Kano

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin (Maliya), CFR, ya nuna matuƙar damuwa kan rahotannin barazanar da ake dangantawa da shugaban 'yan bindiga Kachalla Maha, inda ya buƙaci hukumomin tsaro da su ɗauki matakan gaggawa domin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Kano.

Rahotanni sun ce Sanata Barau ya isar da saƙo ga Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu, yana mai jaddada muhimmancin ƙara sa ido da ɗaukar matakan kariya domin hana duk wani abu da zai iya kawo cikas ga zaman lafiyar al'umma.

Wannan mataki na Sanata Barau ya samu yabon al'umma da dama, inda s**a bayyana cewa ya sake nuna kishinsa ga rayuka da dukiyoyin jama'a. A cewarsu, tun daga lokacin da ya zama wakilin Kano ta Arewa, ya kasance yana amfani da matsayinsa wajen tallafawa hukumomin tsaro da kuma neman hanyoyin da za su tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Masu lura da al'amuran siyasa sun bayyana cewa irin wannan ƙoƙari na nuna shugabanci nagari da jajircewa wajen kare muradun al'umma. Sun yi kira ga hukumomin tsaro da su ci gaba da aiki tare domin tabbatar da cewa Kano da sauran sassan ƙasar nan sun kasance cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Sanata Barau Ya Ƙarfafa Ayyukan Addinin Musulunci a Jihar KanoSanata Dakta Barau I. Jibrin, PhD, CFR (Mujaddadul Islam),...
19/07/2026

Sanata Barau Ya Ƙarfafa Ayyukan Addinin Musulunci a Jihar Kano

Sanata Dakta Barau I. Jibrin, PhD, CFR (Mujaddadul Islam), ya ci gaba da nuna jajircewarsa wajen tallafawa harkokin addinin Musulunci da malamai a Jihar Kano.

A cikin ayyukan da ya aiwatar, ya bai wa Limaman Jumu'a na hedkwatar ƙananan hukumomi 13 da ke Kano ta Arewa motocin Sharon, sannan ya raba babura ga Limaman Jumu'a na Kano ta Arewa gaba ɗaya domin sauƙaƙa musu gudanar da ayyukan wa'azi.

Haka kuma, Sanatan ya tallafa wa manyan ƙungiyoyin addinin Musulunci a faɗin Jihar Kano da sabbin motocin Hummer, ciki har da Tijjaniyya, Qadiriyya, JIBWIS, JIBWIS Jos, da kuma Ofishin Babban Limamin Jihar Kano.

Wannan na daga cikin ayyukan da ke nuna irin gudunmawar Sanata Barau wajen ƙarfafa addinin Musulunci da tallafa wa malamai da cibiyoyin addini a Jihar Kano.

Address

Bauchi
740213

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alpu-Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Alpu-Hausa24:

Shortcuts

Share