Alpu-Hausa24

Alpu-Hausa24 wannan shafin jaridar hausa24.com
(227)

Mataimakin shugaban majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Barau I. Jibrin, ya samar da cibiyoyin karatu na Jami'ar karate ...
04/06/2026

Mataimakin shugaban majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Barau I. Jibrin, ya samar da cibiyoyin karatu na Jami'ar karate daga nesa ta National Open University of Nigeria (NOUN) guda 13 a kananan hukumomin Kano Ta Arewa domin fadada damar samun ilimi ga al'ummar yankin.

An kaddamar da cibiyoyin ne a shekarar 2021, bayan Sanata Barau ya gina su tare da samar musu da muhimman kayan aiki domin tabbatar da gudanar da ayyukansu cikin inganci.

Kananan hukumomin da s**a amfana da shiri sun hada da Shanono, Rimin Gado, , Dawakin Tofa, Tofa, Gabasawa, Tsanyawa, Gwarzo, Ghari, Dambatta, Makoda, Kabo, Bichi da Bagwai.

Wannan mataki ya saukaka wa matasa da manya damar samun karatun jami'a a kusa da muhallansu, tare da rage wahalhalun tafiye-tafiye zuwa manyan birane domin neman ilimi.

Baya ga samar da gine-gine da kayan aiki, cibiyoyin sun kuma samu ma'aikata da motocin aiki domin tabbatar da gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Masu ruwa da tsaki a harkar ilimi sun bayyana wannan aiki a matsayin gagarumar gudummawa wajen bunkasa ilimi da kara yawan masu samun damar karatun digiri da sauran shirye-shiryen ilimi a Kano Ta Arewa.

Al'ummar yankin sun yabawa Sanata Barau I. Jibrin bisa wannan kokari, suna mai cewa cibiyoyin za su ci gaba da amfani ga dubban dalibai tare da taimakawa wajen habaka ilimi da ci gaban al'umma na dogon lokaci.

DSP Senator Dr. Barau I. Jibrin (Maliya) Ne Ya Samar da Cibiyoyin Karatu na National Open University of Nigeria (NOUN) a...
04/06/2026

DSP Senator Dr. Barau I. Jibrin (Maliya) Ne Ya Samar da Cibiyoyin Karatu na National Open University of Nigeria (NOUN) a Kananan Hukumomi Goma Sha Uku na Kano Ta Arewa.

Wannan gagarumin aiki na ilimi ya kawo damar samun karatun jami'a kusa da al'umma, tare da rage wahalar neman guraben karatu da tafiye-tafiye zuwa manyan birane. A shekarar 2021, an kaddamar da cibiyoyin karatun NOUN guda 13 da Sanata Barau ya gina tare da samar musu da kayan aiki a dukkan kananan hukumomin Kano Ta Arewa.

Kananan hukumomin da s**a amfana sun hada da:

Shanono

Rimin Gado

Tofa

Dawakin Tofa

Gabasawa

Tsanyawa

Gwarzo

Ghari

Dambatta

Makoda

Kabo

Bichi

Bagwai

Haka kuma, an bayyana cewa cibiyoyin sun samu ma'aikata da motocin aiki domin tabbatar da gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, lamarin da ya kara saukaka wa matasa da manya damar ci gaba da karatun digiri da sauran shirye-shiryen ilimi.

Godiya da Jinjina

Muna mika godiya ta musamman ga Mai Girma Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Jibrin, bisa wannan gagarumar gudummawa da ya bayar wajen bunkasa ilimi a Kano Ta Arewa. Hakika wannan aiki zai ci gaba da amfanar dubban dalibai na tsawon shekaru masu zuwa, tare da kara habaka ilimi da ci gaban al'umma.

GODIYA DA JINJINA GA DSP SENATOR DR. BARAU I. JIBRIN (MALIYA)Hakika babu wata kalma da za ta iya bayyana irin farin ciki...
03/06/2026

GODIYA DA JINJINA GA DSP SENATOR DR. BARAU I. JIBRIN (MALIYA)

Hakika babu wata kalma da za ta iya bayyana irin farin ciki da godiyar da ɗalibai, iyaye da al'ummar Kano Ta Arewa suke yi ga Mai Girma Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Jibrin, bisa gagarumar gudunmawar da yake bayarwa wajen bunƙasa ilimi da inganta rayuwar matasa.

Sanata Barau ya sake nuna cewa shi jagora ne mai hangen nesa da kishin talakawa ta hanyar ɗaukar nauyin ɗalibai zuwa Federal University Dutsin-Ma, inda yake biyan musu kuɗaɗen makaranta tare da tallafa musu da alawus na Naira Dubu Hamsin (₦50,000) a kowane wata domin rage musu wahalhalun rayuwa da mayar da hankalinsu gaba ɗaya kan karatu.

Wannan abin alheri ba kawai tallafin karatu ba ne, wata babbar gudunmawa ce wajen gina makomar matasa, rage zaman banza, yaƙi da talauci da kuma samar da ƙwararrun matasa waɗanda za su zama ginshiƙan ci gaban al'umma a nan gaba. Duk iyayen da ke ganin 'ya'yansu suna karatu cikin kwanciyar hankali saboda wannan tallafi suna ci gaba da yi wa Sanata Barau addu'a dare da rana.

A yau, dubban matasa suna samun damar cimma burikansu na ilimi ne saboda irin wannan kyakkyawan tsari da Sanata Barau ya samar. Wannan ya tabbatar da cewa jagora nagari shi ne wanda yake amfani da damar da Allah Ya ba shi wajen taimakon jama'a da inganta rayuwarsu.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya saka wa DSP Senator Dr. Barau I. Jibrin (Maliya) da mafificin alheri, Ya ƙara masa lafiya, hikima, ɗaukaka da nasara a dukkan al'amuransa. Allah Ya sanya wannan alheri da yake yi ya zamo silar samun rahama da albarka a gare shi da iyalansa.

Barau Maliya, jagoran matasa, ginshiƙin ilimi, abin alfaharin Kano Ta Arewa, kuma gwarzon ci gaban al'umma. Allah Ya ƙara ɗaukaka. Ameen.

SANATA BARAU YA DAWO DA ƊAN MAJALISAR JIHAR MAKODA CIKIN APCMataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Ji...
02/06/2026

SANATA BARAU YA DAWO DA ƊAN MAJALISAR JIHAR MAKODA CIKIN APC

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Jibrin, ya sake ƙara wa jam'iyyar APC ƙarfi a Kano bayan ya karɓi ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar Mazabar Makoda, Muhammad Ahmad Tomas, wanda ya dawo jam'iyyar APC daga NDC. Rahotanni sun nuna cewa Tomas ya sanar da komawarsa APC ne bayan ganawa da Sanata Barau a Abuja.

Wannan ci gaba na zuwa ne bayan ɗan majalisar ya bar APC a baya, inda aka karɓe shi a sabuwar jam'iyyarsa tare da jagoran siyasa a Kano, Rabiu Musa Kwankwaso. Komawarsa APC cikin kankanin lokaci na nuna yadda tasirin siyasar Sanata Barau ke ci gaba da ƙarfafa jam'iyyar APC a Kano ta Arewa.

Allah Ya ci gaba da ba APC nasara tare da haɗin kan al'umma domin cigaban Jihar Kano da Najeriya baki ɗaya.

  Barau Yana AikiWannan rufin langa-langar da ake gani, shi ne matsugunnin ɗaliban Takuya Primary School a baya kafin zu...
30/05/2026


Barau Yana Aiki

Wannan rufin langa-langar da ake gani, shi ne matsugunnin ɗaliban Takuya Primary School a baya kafin zuwan sauyi.

A yau kuwa, cikin jajircew na Mai Girma Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Dr. Barau I. Jibrin, CFR, FCNA, makarantar ta samu sabbin ajujuwa na zamani tare da ingantaccen muhalli domin koyarwa da koyo.

Wannan wani babban ci gaba ne da ke nuna irin ƙoƙarin da Sanata Barau ke yi wajen bunƙasa ilimi da kyautata rayuwar al’umma a Kano ta Arewa baki ɗaya.

Allah Ya ƙara masa lafiya, hikima da ikon ci gaba da yi wa al’umma hidima.

GUDUNMUWAR BARKA DA SALLAH: ƘUNGIYOYIN SOCIAL MEDIA NA KANO TA AREWA DA JIHA SUN YABAWA SANATA BARAU I. JIBRINƘungiyoyin...
27/05/2026

GUDUNMUWAR BARKA DA SALLAH:

ƘUNGIYOYIN SOCIAL MEDIA NA KANO TA AREWA DA JIHA SUN YABAWA SANATA BARAU I. JIBRIN

Ƙungiyoyin Social Media na Kano ta Arewa da Jihar Kano baki ɗaya sun miƙa saƙon godiya da jinjina ga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ta Ƙasa, Sanata Barau I. Jibrin, bisa irin kulawa, goyon baya da gudunmawar alheri da yake ci gaba da bai wa matasa da ƙungiyoyin sadarwa na zamani a faɗin jihar.

Ƙungiyoyin sun bayyana cewa Sanata Barau jagora ne mai hangen nesa, wanda ya fahimci muhimmancin kafafen sada zumunta wajen wayar da kan al’umma, yaɗa ayyukan alheri da bunƙasa cigaban dimokuraɗiyya da zaman lafiya.

A cikin sanarwar da aka fitar ta hannun shugabannin ƙungiyoyin, ƙarƙashin jagorancin DG Social Media na gidan Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Hon. Basiru Yusuf Shuwaki (SLA), sun yaba da irin yadda Sanatan ke ƙarfafa matasa tare da ba su damar taka rawar gani wajen tallata ayyukan cigaba da manufofin gwamnati.

Ƙungiyoyin sun kuma tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da haskaka nasarori da ayyukan alherin da Sanata Barau I. Jibrin ke gudanarwa a Kano ta Arewa da Jihar Kano baki ɗaya, musamman waɗanda s**a shafi cigaban matasa, ilimi, zaman lafiya da bunƙasa tattalin arziki.

Haka zalika, sun yi amfani da wannan dama wajen taya ɗaukacin al’ummar Musulmi murnar Babbar Sallah, tare da addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya maimaita mana wannan lokaci cikin ƙoshin lafiya, zaman lafiya da yalwar arziki.

A ƙarshe, ƙungiyoyin sun roƙi Allah Ya ƙara wa Sanata Barau I. Jibrin lafiya, hikima da ɗaukaka, Ya kuma ci gaba da ba shi ikon yi wa al’umma hidima cikin gaskiya da riƙon amana.

DG Social Media Hon. Basiru Yusuf Shuwaki

— Sanarwa Daga:
Auwal Wadata Sansan
Shugaban Ƙungiyar Kapmen Yankin Kano ta Arewa

A jiya Litinin 25/05/2026; aka gudanar da taron manema labarai kan yadda rabon Takin Zamani na noma zai kasance, wanda m...
26/05/2026

A jiya Litinin 25/05/2026; aka gudanar da taron manema labarai kan yadda rabon Takin Zamani na noma zai kasance, wanda mai girma mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya zaɓaɓɓen Sanatan Kano ta Arewa, kuma Ɗantakarar Sanata karo na huɗu a kakar zaɓe me zauwa ta 2027, Sanata Dakta Barau I. Jibrin PhD. Cfr. Zai rabawa Manoman yankin sa da yake wakilta na Kano ta Arewa kamar yadda ya saba a duk shekara. A wannan karon Mai girma Sanatan zai raba Tirela 88 ga Al'ummar yankin nasa wanda Mutane 53,040 zasu amfana da wannan Takin a faɗin ƙananan hukumomin Kano ta Arewa 13.

Hon. Prof. Muhammad Ibn Abdallah Shugaban ma'aikatan Ofishin Mai girma mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya tare da Hon. Sh*tu Madawaki Ghari Mai magana da yawun Sanatan sune s**a jagoranci zaman.

Taron yasamu halattar manya manyan jagorori daga dukkanin ɓangarorin Kano ta Arewa tare da ƴan jaridu da ƴan Social Media.

Basiru Yusuf Shuwaki
D.G Social Media na Dsp. Dr. Barau PhD.
26/05/2026

SANATA BARAU I JIBRIN MALIYA ZAI RABAWA  AL’UMMAR KANO TA AREWA NAIRA MILIYAN DARI DA TALATIN DA HUDU DA DUBU DARI TARA ...
25/05/2026

SANATA BARAU I JIBRIN MALIYA ZAI RABAWA AL’UMMAR KANO TA AREWA NAIRA MILIYAN DARI DA TALATIN DA HUDU DA DUBU DARI TARA (1,34,90000) BARKA DA SALLAH

Al’umma maza da mata na yankin Kano Ta Arewa suna ci gaba da bayyana farin ciki da jin dadinsu bisa irin kulawa, tausayi da kuma jajircewar da Mai Girma Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Barau I. Jibrin ke nunawa al’ummar da yake wakilta.

A wani babban mataki na kara kusantar al’umma da tallafawa rayuwarsu musamman a wannan lokaci na shagulgulan babbar Sallah, Mai Girma Sanata DSP BARAU I JIBRIN MALIYA zai gudanar da rabon sakon barka da sallah na kimanin Naira miliyan Dari da talatin da hudu da dubu dari tara ( #134,900,000) domin faranta ran al’ummar Kano Ta Arewa baki daya.

Wannan karamci da tallafi ya zo ne a daidai lokacin da al’ummar musulmi ke shirye-shiryen gudanar da bukukuwan Sallah, lokaci wanda iyalai da dama ke bukatar taimako da kulawa domin gudanar da rayuwa cikin walwala da farin ciki.

Rabon tallafin zai hada da shugabannin jam’iyyar All Progressives Congress na Kano Ta Arewa, shugabannin EXCO, wakilan mazabu guda 141, matasa maza da mata, kungiyoyin CRC LAFIYA JARI, kungiyar YAN TAURI, da kuma kungiyar Abba Gida Gida Organization tare da sauran al’umma masu bukata.

Hakika, wannan aiki babban shaida ne dake nuna cewa Sanata BARAU I JIBRIN ba kawai jagora bane, har ila yau uba ne mai tausayin talakawansa, wanda kullum burinsa shine ganin rayuwar al’umma ta inganta. A duk lokacin da bukatar jama’a ta taso, yana kasancewa a gaba wajen tallafawa da samar da mafita.

Ba a dade ba ma, cikin satin daya gabata, Mai Girma Sanatan ya kaddamar da rabon taki ga manoman Kano Ta Arewa, inda aka raba sama da buhunan taki dubu hamsin da uku domin bunkasa noma da karfafa tattalin arzikin manoma.

Wannan ya kara tabbatar da cewa jagorancinsa ya ta’allaka ne akan aiki tukuru, tausayi da cigaban al’umma.

A yau al’ummar Kano Ta Arewa na iya cewa cikin alfahari cewa sun samu shugaba mai hangen nesa, shugaba mai tausayi, kuma jagora wanda yake fifita bukatun jama’a fiye da komai.

Muna kara godewa Allah Madaukakin Sarki daya azurta mu da shugaba irin DSP BARAU I JIBRIN MALIYA. Muna rokon Allah Ubangiji Ya kara masa lafiya, hikima, daukaka da karin nasara a dukkan al’amuransa, Ya kuma ci gaba da amfani da shi wajen kawo ci gaba da walwalar al’umma.

Allah Ya kara daukaka Mai Girma Sanata DSP BARAU I JIBRIN MALIYA.
Allah Ya albarkaci Kano Ta Arewa.
Allah Ya sanya alheri cikin wannan Sallah.
Amin summa Amin.

DSP. Dr. Barau I. Jibrin PhD. Cfr. Ne GATAN ILMI kuma GARKUWAN ILMI a duk faɗin Arewacin Najeriya.1. Ya Kawo Federal Pol...
25/05/2026

DSP. Dr. Barau I. Jibrin PhD. Cfr. Ne GATAN ILMI kuma GARKUWAN ILMI a duk faɗin Arewacin Najeriya.

1. Ya Kawo Federal Polytechnic Kabo
2. Ya Kawo Open University 13 L.G
3. Ya kawo Study Centres reshen FUDMA
4. Ya kawo Resunan FCET Bichi a L.G 5
5. Ya biya Scholarship ga Ɗaliban gaba da sakandire na Kano ta arewa
6. Ya rabawa Ƙungiyar Dalibai na manyan Makarantu Motoci
7. Ya Dalibai na gaba da Sakandire Mashina
8. Ya Rabawa Daliban gaba da sakandire Kekuna
9. Ya rabawa Daliban gaba da sakandire Kwamfutoci
10. Ya Rabawa Daliban gaba da sakandire Wayoyi
11. Ya kawo Police College
13. Ya gina Blocks masu yawa a makarantun Kano ta arewa
14. Ya raba kujeru a dukkanin makarantun kano ta arewa
15. Yana biyawa Daliban Sakandire Ƙuɗin Jarabawar NECO ga waɗanda s**a faɗi Jarabawar Qualifying duk shekara.
16. Tura Ɗalibai Ƙasashen Waje Domin Yin Degree na II

Basiru Yusuf Shuwaki DG media

Address

Bauchi
740213

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alpu-Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Alpu-Hausa24:

Share