
15/08/2025
Muna Zargin Gwamnatin Kano Ta Jifge Ƴãɲ-Dãba A Garuruwan Da Za A Yi Zaɓe Muna Kira Ga Jami'an Tsarø Su Ɗauki Matakin Gagggawa, Cewar Shuwaki
Ɗan siyasa a Jihar Kano, Hon. Basiru Yusuf Shuwaki ya zãrgi Gwamnatin Jihar Kano a ƙarƙashin jagorancin, Injiniya Abba Kabir Yusuf da nemaɲ haddasa fitiɲã da tashin haɲkali a zaɓen cike gurbi da za a gudanar gobe a Jihar.
Shuwaki wanda ya bayyana haka ta cikin tattaunawarsa da Dokin Ƙarfe TV, ya fara ne da cewa, "Muna kira ga jami'aɲ tsarø su ɗauki matakin gaggawa kan zaɓen da za a yi a ƙaramar hukumar Ƙunchi, Garo, Shanono da Ɓagwai, saboda gwamnan Kano ya shiga garuruwan Ƙunchi da Shanono muna zargģin ɲsun jifge ƴãɲ dãba a garuruwan suna yawo da makamai domin su ƙwace zaɓe". Inji shi.
Ya kuma ƙara da cewa, "Muna zargiɲ mutanen da ke tare hanyoyi irin na Birnin Gwari su yi fãśhi, su aka ɗebo aka kawo mana. A jiya sun shiga ƙaramar hukumar Shanono sun sassãri mutãɲe, muna da hujjoji na hotuna da bidiyo, dan haka muke kira ga jami'an tsaro da su ɗauki mataki, duk wanda ba ɗan gari ba ne a kore shi ya tafi garinsu a ƙyale mutane su zaɓi abin da suke so". In ji Hon.Basiru Yusuf Shuwaki.