22/08/2026
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya mayar wa Shugaba Bola Tinubu martani, bayan da shugaban ya soki shirin Atiku na dawo da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Tinubu ya ce alkawarin dawo da tallafin man fetur da Atiku ya yi wata alama ce ta rashin fahimta sosai game da shugabanci da tattalin arziki.
A martaninsa, Atiku ya zargi Tinubu da aiwatar da manufofin tattalin arziki da s**a jefa ƴan Najeriya cikin wahala.
Ya ce cire tallafin man fetur ba tare da ingantaccen shirin sauyi da kariya daga hauhawar farashi ba ya haifar da tashin farashin man fetur, sufuri da kayan abinci, tare da rage karfin sayen jama’a.
Atiku ya bayyana cewa shirin da yake gabatarwa ba wai dawo da tsohon tsarin tallafin man fetur ba ne, illa wani tsari ne mai iyaka, kasafin kuɗi, wa’adi da kuma sa ido mai zaman kansa.
Ya kuma yi tambaya kan abin da gwamnatin Tinubu ta cire, yana mai cewa rahotannin asusun NNPC sun nuna akwai kuɗaɗen da ake dangantawa da tsaron mak**ashi da kuma gibin farashin man fetur.
Atiku ya ce bai k**ata a gina tsarin tarayya ta hanyar talauta ƴan ƙasa domin ƙara yawan kuɗin da ake turawa Gwamnatocin jihohi ba.