Eagle Radio Bauchi

Eagle Radio Bauchi Eagle Radio Bauchi: Mai zagaya da ku sassan duniya.

Wannan shafin mallakin Eagle Radio Bauchi ne, gidan rediyo mai zaman kansa da ke yaɗa sahihan labarai da shirye-shirye masu gamsarwa a kan mita 96.5 zangon FM daga birnin Bauchi.

Bayan rasuwarsa ranar Juma’a, 21 ga Agusta 2026, an ga sunan Alhaji Hamza Darma cikin jerin mambobin Kwamitin Yaƙin Nema...
22/08/2026

Bayan rasuwarsa ranar Juma’a, 21 ga Agusta 2026, an ga sunan Alhaji Hamza Darma cikin jerin mambobin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na 2027 da jam’iyyar APC ta fitar.

Marigayin ya kasance ɗaya daga cikin masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa.

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce aikinsa a fafatawar siyasa a yanzu shi ne ya sanya shugabannin adawa ...
22/08/2026

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce aikinsa a fafatawar siyasa a yanzu shi ne ya sanya shugabannin adawa cikin matsin lamba tare da tabbatar da cewa ba su samu kwanciyar hankali ba.

Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake ziyarar duba wasu ayyukan samar da ababen more rayuwa da ake ci gaba da gudanarwa a Abuja.

Ya ce rikicin da ke cikin Jam’iyyar PDP ya sa ya zama da wahala a iya gano wata jam’iyyar adawa mai karfi da za ta iya zama jagora gabanin babban zaben 2027.

Ministan ya kuma ce bai damu da yadda tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suke ji game da sauye-sauyen siyasar ba.

Ya kara da cewa da ya san yadda suke ji a yanzu, zai kara jefa su cikin rikici.

Jam’iyyar NDC ta umarci ƴan takararta su fara tuntubar jama’a da masu ruwa da tsaki domin tunkarar zaɓen 2027.NDC ta kum...
22/08/2026

Jam’iyyar NDC ta umarci ƴan takararta su fara tuntubar jama’a da masu ruwa da tsaki domin tunkarar zaɓen 2027.

NDC ta kuma ce za ta kafa kwamitocin yaƙin neman zaɓe a matakai daban-daban, tare da buƙatar a guji tashin hankali da kalaman ƙiyayya.

Jam’iyyar ta ce ta sanar da INEC game da sauya tambarinta, amma har yanzu ana kammala wasu matakan gudanarwa. Don haka, ta umarci mambobinta su ci gaba da amfani da tambarin yanzu da alamar yatsu biyu har sai an kammala sauyin.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada tsohon Gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, a matsayin Darakta-Janar na kwamitin yakin nem...
22/08/2026

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada tsohon Gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, a matsayin Darakta-Janar na kwamitin yakin neman zaɓen APC na 2027.

Tinubu zai jagoranci kwamitin, yayin da Kashim Shettima da Nentawe Yilwatda za su kasance mataimakansa.

Gwamnan Imo, Hope Uzodimma, zai zama sakataren kwamitin.

Kwamitin zai kunshi manyan ƴan jam’iyyar da za su ba da shawara, ciki har da Bisi Akande, Segun Osoba, Rochas Okorocha da Abdullahi Adamu.

Bayo Onanuga ya ce Tinubu ya umurci mambobin kwamitin da su yi aiki tukuru domin ganin APC ta yi nasara a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Tinubu ya kuma ce gwamnatinsa ta cika alkawuran da ta dauka tare da sanya Najeriya kan turbar ci gaban tattalin arziki.

CIKIN HOTUNA: Kungiyar BAUCHI ORGANIZATION FOR LEADERSHIP AND DEVELOPMENT INITIATIVES ta gudanar da taron nuna goyon bay...
22/08/2026

CIKIN HOTUNA: Kungiyar BAUCHI ORGANIZATION FOR LEADERSHIP AND DEVELOPMENT INITIATIVES ta gudanar da taron nuna goyon baya da jaddada mubaya’a ga Sanata Shehu Buba Umar, ɗan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a ƙarƙashin Jam’iyyar PRP mai alamar ɗan makulli.

Taron, wanda ya samu halartar shugabannin ƙungiyoyin mata da matasa daga sassa daban-daban na Jihar Bauchi, ya kasance wata dama ta bayyana cikakken goyon baya da kuma ƙara jaddada mubaya’a ga takarar Sanata Shehu Buba Umar a zaɓen Gwamnan Jihar Bauchi.

Mahalarta taron sun bayyana aniyarsu ta yin aiki tare domin ganin an samu nasarar takarar Sanata Shehu Buba Umar a ƙarƙashin Jam’iyyar PRP.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya mayar wa Shugaba Bola Tinubu martani, bayan da shugaban ya soki shir...
22/08/2026

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya mayar wa Shugaba Bola Tinubu martani, bayan da shugaban ya soki shirin Atiku na dawo da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Tinubu ya ce alkawarin dawo da tallafin man fetur da Atiku ya yi wata alama ce ta rashin fahimta sosai game da shugabanci da tattalin arziki.

A martaninsa, Atiku ya zargi Tinubu da aiwatar da manufofin tattalin arziki da s**a jefa ƴan Najeriya cikin wahala.

Ya ce cire tallafin man fetur ba tare da ingantaccen shirin sauyi da kariya daga hauhawar farashi ba ya haifar da tashin farashin man fetur, sufuri da kayan abinci, tare da rage karfin sayen jama’a.

Atiku ya bayyana cewa shirin da yake gabatarwa ba wai dawo da tsohon tsarin tallafin man fetur ba ne, illa wani tsari ne mai iyaka, kasafin kuɗi, wa’adi da kuma sa ido mai zaman kansa.

Ya kuma yi tambaya kan abin da gwamnatin Tinubu ta cire, yana mai cewa rahotannin asusun NNPC sun nuna akwai kuɗaɗen da ake dangantawa da tsaron mak**ashi da kuma gibin farashin man fetur.

Atiku ya ce bai k**ata a gina tsarin tarayya ta hanyar talauta ƴan ƙasa domin ƙara yawan kuɗin da ake turawa Gwamnatocin jihohi ba.

22/08/2026
CIKIN HOTUNA: Yadda Hon. Aliyu Aminu Garu, ɗan takarar Majalisar Wakilai mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Bauchi a ƙarƙashin...
21/08/2026

CIKIN HOTUNA: Yadda Hon. Aliyu Aminu Garu, ɗan takarar Majalisar Wakilai mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Bauchi a ƙarƙashin jam’iyyar APM, ya kai ziyara gidan Alhaji Muntaka Musa Duguri domin neman goyon baya da addu’o’i, tare da fatan samun nasarar jam’iyyar a gabanin zaben shekarar 2027.

Rundunar Ƴan Sandan Jihar Bauchi ta fara bincike kan mutuwar Abdulrazak Ibrahim, mai shekaru 39, a ofishin ƴan vigilante...
21/08/2026

Rundunar Ƴan Sandan Jihar Bauchi ta fara bincike kan mutuwar Abdulrazak Ibrahim, mai shekaru 39, a ofishin ƴan vigilante da ke Bakin Kura, ƙaramar hukumar Bauchi.

An kai rahoton lamarin ga ƴan sanda ne a ranar 20 ga Agusta, 2026, da misalin ƙarfe 6:39 na yamma.

An gayyaci Abdulrazak ofishin ƴan bangan ne domin bincike kan zargin sata da mahaifiyarsa, Hauwa Ibrahim, ta shigar.

Sai dai ya rasu ne yayin da yake hannun ƴan bangan.

Ƴan sanda sun tura jami’an bincike zuwa wurin, inda aka k**a ƴan banga uku da suke bakin aiki a lokacin. A yanzu haka suna tsare domin bincike.

An kai gawar Abdulrazak Asibitin Koyarwa na ATBU da ke Bauchi, inda aka ajiye ta a ɗakin adana gawarwaki.

Ƴan sanda sun ce babu wata alamar tashin hankali ko muzgunawa da aka gani a jikin gawar, amma za a gudanar da binciken gawa domin gano ainihin abin da ya haddasa mutuwarsa.

21/08/2026

KAI TSAYE: Jawabin Jigon Jam’iyyar APM, Alhaji Muntaka Musa Duguri, yayin da yake jawabin maraba na zinariyar Hon. Aliyu Aminu Garu, ɗan takarar Majalisar Wakilai mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Bauchi, a gidansa da ke nan Bauchi.

Address

No. 22 Buba Yero Street Behind Matrix Filling Station Along Yelwa Road Bauchi
Bauchi
740102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Eagle Radio Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category