Eagle Radio Bauchi

Eagle Radio Bauchi Flying You Around The World
(1)

An bayyana nasaran da Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya samu ne yayin wani taron manema labarai da shugaban ...
20/05/2026

An bayyana nasaran da Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya samu ne yayin wani taron manema labarai da shugaban kwamitin zaben fidda gwani na jam'iyyar APC a Jihar Gombe, Malam Labiru Musa Kafur, ya gudanar

Malam Labiru Musa ya sanar da cewa Gwamna Inuwa Yahaya ya samu jimillar kuri’u 131,009, hakan yasa ya zama wanda ya samu tikitin tsayawa takarar babban zabe a karkashin jam'iyyar.

Haj. Zainab Baban-Takko, wadda take neman takarar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi a mazabar Bauchi ta Tsakiya ƙarƙashin J...
20/05/2026

Haj. Zainab Baban-Takko, wadda take neman takarar Majalisar Dokokin Jihar Bauchi a mazabar Bauchi ta Tsakiya ƙarƙashin Jam'iyyar APC, ta sanar da janyewa daga zaben fidda gwani. Ta ce ta ɗauki matakin ne bayan nazari da lura da yadda tsarin yake gudana, inda ta bayyana rashin gamsuwa da bin ƙa’idojin dimokuraɗiyya.

Ta ƙara da cewa janyewarta ba fushi ba ne ko rashin nasara, illa dai mataki ne na ƙa’ida da ta ɗauka cikin nutsuwa da imani da gaskiya.

Ta gode wa magoya bayanta da s**a mara mata baya, tare da kira gare su da su ci gaba da zaman lafiya da mutunta juna.

A ƙarshe, ta jaddada cewa za ta ci gaba da hidimtawa al’umma tare da addu’ar Allah Ya tabbatar da adalci da ingantaccen tsarin dimokuraɗiyya.

Sanata Shehu Buba Umar mai wakiltar Bauchi ta Kudu ya janye daga takarar gwamnan Bauchi a jam’iyyar APC kafin zaɓen fidd...
20/05/2026

Sanata Shehu Buba Umar mai wakiltar Bauchi ta Kudu ya janye daga takarar gwamnan Bauchi a jam’iyyar APC kafin zaɓen fidda gwani na ranar 21 ga Mayu, 2026.

Ya ce ya ɗauki matakin ne saboda rashin gamsuwa da yadda ake gudanar da harkokin jam’iyyar a jihar, yana zargin karya kundin tsarin mulki, dokar zaɓe da ƙa’idojin APC.

Sanatan ya kuma bayyana cewa rikicin shugabanci da ke cikin APC a Bauchi, musamman kan wasu muƙaman kwamitin gudanarwa, na barazana ga haɗin kan jam’iyyar a jihar.

Daga karshe dai Arsenal ta lashe gasar Premier ta kasar Birtaniya bayan shekaru 22
19/05/2026

Daga karshe dai Arsenal ta lashe gasar Premier ta kasar Birtaniya bayan shekaru 22

HOTUNA:Hukumar EFCC ta k**a tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, da misalin ƙarfe 3:30 na asubahin yau.Shugaban...
19/05/2026

HOTUNA:

Hukumar EFCC ta k**a tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, da misalin ƙarfe 3:30 na asubahin yau.

Shugaban EFCC, Ola Olukoyede ya tabbatar da kamen Saleh Mamman, wanda aka samu da laifin almundahanar kuɗaɗen gwamnati har Naira biliyan 33.8.

Farfesan ya janye ne bisa zargin shirya kwarfe shi a karo na biyu!
19/05/2026

Farfesan ya janye ne bisa zargin shirya kwarfe shi a karo na biyu!

Jami’an Hisbah a jihar Kebbi sun k**a mutumin a gidan matar auren da ke yankin Badariya a Birnin Kebbi.Darakta mai kula ...
19/05/2026

Jami’an Hisbah a jihar Kebbi sun k**a mutumin a gidan matar auren da ke yankin Badariya a Birnin Kebbi.

Darakta mai kula da harkokin Shari’a na hukumar, Sirajo Kamba, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa mazauna yankin ne s**a sanar da Hisbah bayan sun ga mutumin ya shiga gidan matar da tsakar dare.

A cewarsa, lokacin da jami’an Hisbah s**a isa gidan, matar ta fara musanta cewa babu kowa a ciki, amma daga bisani ta amince a bincika gidan inda aka gano mutumin a boye cikin jaka.

Ya ce bincike ya nuna akwai alaka ta soyayya tsakanin mutumin da matar auren, kuma dukkansu sun amsa zargin yayin tambayoyi.

NAN

Sanatocin jihar Borno uku masu ci a yanzu; Ali Ndume na Borno ta Kudu, Mohammed Monguno na Borno ta Arewa da Kaka Shehu ...
19/05/2026

Sanatocin jihar Borno uku masu ci a yanzu; Ali Ndume na Borno ta Kudu, Mohammed Monguno na Borno ta Arewa da Kaka Shehu Lawan na Borno ta Tsakiya, sun samu tikitin jam’iyyar APC ba tare da hamayya ba a zaben fidda gwani da aka gudanar a jihar.

An tabbatar da Ali Ndume a matsayin dan takarar jam’iyyar ne bayan babban abokin hamayyarsa, Abdullahi Askira, ya janye daga takarar bayan tuntuba da shugabannin jam’iyyar.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi wannan jawabi ne a Rano yayin taron tabbatar da Sulaiman Kawu Sumaila a matsa...
19/05/2026

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi wannan jawabi ne a Rano yayin taron tabbatar da Sulaiman Kawu Sumaila a matsayin ɗan takarar Sanatan Kano ta Kudu, inda ya ce shirunsa ba tsoro ba ne, sai dai ladabi da kiyaye zaman lafiya.

Ya kuma yi ishara da batun bambancin shekaru dake tsakaninsa da tsohon Ubangidansa, Rabiu Musa Kwankwaso, yana mai cewa ana girmama manya, amma hakan ba yana nufin za a yi shiru idan aka ci gaba da tsokano mutum bane.

Ya ce idan aka ci gaba da tursasa shi, zai iya bankado abubuwa da dama da ba a sani ba a siyasar jihar Kano.

19/05/2026

BAUCHI A SAFIYAR YAU, TALATA.

19/05/2026

SPONSORED:

Sakon Usman Abdullahi Koli, dangane da zaben fidda gwani na kujerar gwamna a karkashin jam'iyyar APC da ake shirin gudanarwa.

Address

No. 22 Buba Yero Street Behind Matrix Filling Station Along Yelwa Road Bauchi
Bauchi
740102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Eagle Radio Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category