Labari Daga Bauchi

  • Home
  • Labari Daga Bauchi

Labari Daga Bauchi Media News

20/07/2025
20/07/2025

KAITSAYE

Kungiyar Wunti Community for Women Development tare da haɗin gwiwar wasu kungiyoyin mata na cikin garin Bauchi, tana gabatar da babban taron kiran goyon bayan Dr. Bala Maijama’a Wunti, domin karɓar ƙiran al’umma na fitowa takarar Gwamnan Jihar Bauchi a shekara ta 2027 (Daga Bala Sai Bala).

Taron na gudanane a gaban makarantar Dr. Ibrahim Tahir Comprehensive Secondary School, Bauchi.

GAGARUMIN TARON JAM’IYYAR MATASA NAJERIYA, RESHEN JIHAR BAUCHIAn gudanar da gagarumin taron kafa Jam’iyyar Matasa ta Naj...
20/07/2025

GAGARUMIN TARON JAM’IYYAR MATASA NAJERIYA, RESHEN JIHAR BAUCHI

An gudanar da gagarumin taron kafa Jam’iyyar Matasa ta Najeriya, reshen Jihar Bauchi cikin natsuwa da armashi da cikakken tsari. Wannan taron yana daga cikin matakan da ake dauka domin karfafa matasa wajen samun dama a fagen siyasa da kuma ciyar da kasa gaba.

A farkon taron, Usman Mijin Yawa a matsayinsa na Mai Gabatar da Shirin (MC) ya jagoranci shirin, inda ya gabatar da wadanda za su yi jawabi, tare da tabbatar da cewa dukkan lamurra sun tafiya yadda ya kamata bisa tsari da jadawalin da aka tsara.

Jawaban da aka gabatar a wajen taron:

1. Jawabin Budewa:
Shugaban Jam’iyyar Matasa, Nuruddeen H. Danrimi, ya gabatar da jawabinsa na budewa inda ya bayyana burin kafa wannan jam’iyya da kuma muhimmancin matasa wajen ciyar da kasa gaba ta hanyar shiga harkokin siyasa.

2. Bayani kan Makasudin Taro:
An gabatar da takaitaccen tarihin Jam’iyyar Matasa daga Comr. Jabir A. Kofa (Sakataren Jam’iyyar Matasa) inda ya bayyana dalilin kafa wannan jam’iyya a Najeriya, tare da irin kokarin da aka dade ana yi domin cika wannan buri.

3. Jawabi na Musamman:
Shugaban Jam’iyyar Matasa na Karamar Hukumar Tafawa Balewa ya gabatar da muhimmiyar magana mai taken: "Bukatar Hadin Kan Matasa" inda ya jaddada cewa babu wata nasara da matasa za su samu a siyasance sai sun hada kai.

4. Maraba da Baki:
Comr. Salmanu Dass (Daraktan Yada Sako) ya yi maraba da baki tare da bayyana muhimmancin wannan taro ga matasan Bauchi da Najeriya baki daya.

5. Babban Jawabin Taro:
Babban bako kuma jigo na musamman a taron, Col. Adamu Bauchi (Rtd.), ya gabatar da cikakken jawabi kan taken taron:
"Fito da Dama ga Matasa ta Hanyar Shiga Cikin Harkokin Siyasa: Rawar da Jam’iyyar Matasa ke Takawa wajen Samar da Sauyin Mulki Cikin Sauki."
A cikin jawabinsa ya jaddada yadda matasa za su iya amfani da damar da ke gabansu ta hanyar shiga siyasa domin sauya tafarkin shugabanci a Najeriya.

6. Kalaman Karfafa Gwiwa:
Comr. Aliyu Abdullahi ya gabatar da karin jawabi inda ya karfafa gwiwar matasa da su tsaya tsayin daka wajen ci gaba da neman damar shugabanci.

Kammalawa:

A karshe, an jaddada babban makasudin wannan taro cewa yana da nufin fito da dama ga matasa domin su shiga harkokin siyasa cikin natsuwa da tsari tare da taka rawar gani wajen samar da shugabanci nagari a Najeriya.

SANARWA GA JAMA’ANA BAI WA SANATA SHEHU BUBA UMAR WA’ADIN WATA GUDA YA FITO YA BAYYANA NIYYARSA TA TAKARAR GWAMNAN JIHAR...
20/07/2025

SANARWA GA JAMA’A

NA BAI WA SANATA SHEHU BUBA UMAR WA’ADIN WATA GUDA YA FITO YA BAYYANA NIYYARSA TA TAKARAR GWAMNAN JIHAR BAUCHI A 2027, KO IN KAISHI KOTU!

Ni, Safiyanu Manaja Gumau, a matsayina na cikakken masoyin Sanata Shehu Buba Umar, ina sanar da daukacin jama’ar jihar Bauchi da ma dukkan ‘yan Najeriya cewa na bai wa Sanatan wa’adin wata guda (30 kwanaki) ya fito ya bayyana wa jama’a a fili cewa zai tsaya takarar kujerar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2027.

Wannan kira da wannan wa’adi da na yi masa ba komai ba ne illa domin muna da tabbacin cewa jihar Bauchi tana bukatar shugaba nagari irin Sanata Shehu Buba Umar wanda zai kawo wa jihar ci gaba, zaman lafiya da adalci ga kowa da kowa.

Idan har cikin wannan wa’adin na wata guda bai fito ba ya bayyana wannan kuduri nasa a bayyane, to zan dauki matakin shari’a, in kai shi gaban kotu domin bani da wata mafita face hukuma ta saurare ni a matsayin wanda ke da muradin jin dadin jihar sa. A matsayina na masoyinsa tun tuni, ina ganin shi ne mutum daya tilo da zai iya ceto jihar Bauchi daga halin da take ciki yanzu.

Wallahi na gaji da jira.

Ina rokon Allah ya tabbatar mana da wannan buri na mu, domin Shehu Buba Umar ne fatan mu kuma burin mu a matsayin Gwamnan Jihar Bauchi, 2027 in sha Allah.

20/7/2025
---

Wanda ya fitar da wannan sanarwa:

Safiyanu Manaja Gumau
+234 813 255 7142

Sakon GayyataA madadin Kungiyar Wunti Community for Women Development tare da haɗin gwiwar wasu kungiyoyin mata na cikin...
19/07/2025

Sakon Gayyata

A madadin Kungiyar Wunti Community for Women Development tare da haɗin gwiwar wasu kungiyoyin mata na cikin garin Bauchi, muna farin cikin gayyatar ka zuwa babban taron kiran goyon bayan Dr. Bala Maijama’a Wunti, domin karɓar ƙiran al’umma na fitowa takarar Gwamnan Jihar Bauchi a shekara ta 2027 (Daga Bala Sai Bala).

Taron zai gudana ne...

Rana: Lahadi, 20 ga Yuli, 2025
Lokaci: 10:00 na safe
Wuri: A gaban makarantar Dr. Ibrahim Tahir Comprehensive Secondary School, Bauchi.

Zuwan ka zai kasance babban girmamawa a gare mu, kuma ƙarfafawa ne ga muradunmu na cigaban Jihar Bauchi.

Mun gode.

19/07/2025

GAMAYYAR KUNGIYOYIN SHIYYAR BAUCHI TA KUDU NA JAM’IYYAR PDP SUN NEMI FARUQ MUSTAPHA YA FITO TAKARAR GWAMNAN JIHAR BAUCHI 2027

2027 KIRA ZUWA GA FAROUQ MUSTAPHA (Coalition | Bauchi South | PDP | 2027

Gamayyar kungiyoyin magoya bayan jam’iyyar PDP na shiyyar Bauchi ta Kudu sun gudanar da taro na musamman domin bayyana goyon bayansu ga Rt. Hon. Faruq Mustapha (Jigon Katagum), kwamishinan raya karkara da ci gaban birane na jihar Bauchi, akan ya tsaya takarar kujerar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben shekarar 2027.

Kungiyoyin sun bayyana cewa suna da yakinin cewa Faruq Mustapha zai iya jagorantar jihar Bauchi cikin gaskiya, adalci da nagartaccen shugabanci.

GAMAYYAR KUNGIYOYIN SHIYYAR BAUCHI TA KUDU NA JAM’IYYAR PDP SUN NEMI FARUQ MUSTAPHA YA FITO TAKARAR GWAMNAN JIHAR BAUCHI...
19/07/2025

GAMAYYAR KUNGIYOYIN SHIYYAR BAUCHI TA KUDU NA JAM’IYYAR PDP SUN NEMI FARUQ MUSTAPHA YA FITO TAKARAR GWAMNAN JIHAR BAUCHI 2027

2027 KIRA ZUWA GA FAROUQ MUSTAPHA (Coalition | Bauchi South | PDP | 2027

Gamayyar kungiyoyin magoya bayan jam’iyyar PDP na shiyyar Bauchi ta Kudu sun gudanar da taro na musamman domin bayyana goyon bayansu ga Rt. Hon. Faruq Mustapha (Jigon Katagum), kwamishinan raya karkara da ci gaban birane na jihar Bauchi, akan ya tsaya takarar kujerar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben shekarar 2027.

Kungiyoyin sun bayyana cewa suna da yakinin cewa Faruq Mustapha zai iya jagorantar jihar Bauchi cikin gaskiya, adalci da nagartaccen shugabanci.

KUNGIYAR ABG BOYS TA KARAMAR HUKUMAR DARAZO TA NEMI DR. ADAMU BABAYO GABARIN YA FITO TAKARAR KUJERAR GWAMNAN JIHAR BAUCH...
19/07/2025

KUNGIYAR ABG BOYS TA KARAMAR HUKUMAR DARAZO TA NEMI DR. ADAMU BABAYO GABARIN YA FITO TAKARAR KUJERAR GWAMNAN JIHAR BAUCHI A SHEKARAR 2027

Kungiyar ABG Boys da ke karamar hukumar Darazo, Jihar Bauchi ta bayyana bukatar ta ga Dr. Adamu Babayo Gabarin, kwamishinan matasa da wasanni na jihar, da ya tsaya takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2027, bisa la’akari da irin ayyukan alheri da ya riga ya shimfida a fadin jihar Bauchi tun daga lokacin da yake rike da mukamai daban-daban a gwamnatin jihar.

Shugaban kungiyar ya bayyana hakan ne ga manema labarai, inda ya ce sun yanke wannan shawara ne bayan sun yi nazari kan tarihin ayyukan Dr. Babayo Gabarin tun daga lokacin da yake matsayin Kwamishinan Gidaje da Tsare-tsaren Kasa (Lands and Survey), S.A bangaren lafiya, kakakin jam’iyyar PDP har zuwa matsayin kwamishinan matasa da wasanni.

Abubuwan da s**a ja hankalin kungiyar ABG Boys sun hada da:

Nadin Mukamai (Appointment):
Kungiyar ta bayyana cewa ABG ya baiwa matasa sama da mutum 20 mukamai a lokacin da yake kwamishina, wanda hakan ya basu dama su taimaki kansu da wasu a cikin al’umma.

Shirye-shirye (Programs):
Ya samar da dama ga matasa maza da mata ta hanyoyi daban-daban kamar SMC, New Incentive da sauran shirye-shirye, inda kowane wata suke amfana da akalla Naira 40,000, wasu har suna biya wa iyayensu da ‘yan uwansu bukatu daga wannan dama.

Rabon Hectar (Gona):
ABG ya bai wa matasa fiye da hektoci 300 na filayen noma, inda kowanne ke da darajar sama da Naira 300,000 a yau. Wasu sun noma don iyalansu, wasu kuma sun taimaki gidajensu.

Biyan Kudaden Karatu (School Fees):
Ya dauki nauyin yara da dama wajen biyan kudin NECO/JAMB da kula da lafiyarsu daga farko har zuwa kammala karatu. Har yanzu yana ci gaba da biya su sama da Naira 1.8m a kowacce shekara.

Jarin Kasuwanci (Empowerment):
ABG ya tallafa wa matasa da mata da jarin kasuwanci, inda wasu s**a karbi Naira 50,000, 100,000 har ma da 300,000 domin su fara sana’o’insu.

Jawabin Shugaban Kungiyar ABG Boys:

“Idan za mu cire adawar siyasa, Dr. Adamu Babayo Gabarin tamkar abin koyi ne ga sauran ‘yan siyasar Bauchi. Wannan ne irin aikin da muke so. Wanda ke ba da dama, taimako da tallafi. Mu dubi gaskiya, duk wanda zai yi mana irin wannan hidima a siyasance, masoyi ne.”

Kungiyar ta kuma ce siyasa ba karya ba ce, kuma lokaci yayi da za a cire adawar siyasa a tallafa masa domin ci gaba da amfanar da al’umma gaba daya.

A KARSHE KUNGIYAR TA CE:

“ABG For Governor 2027.”

Allah ya saka da gidan Aljanna wa iyayen ka.”

Wannan sanarwa ce daga: Mai magana da yawun ABG Boys, Nura Adamu Beti (Comr. D. Beti) Mataimakin Kwamishina, Bangaren Sadarwa. Ranar 07/2025.

AIKIN ALHERI SAI ƊAN ARZIKI - AKY MAKAMA YA KADDAMAR DA SHIRIN LAFIYA. Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Alkale...
19/07/2025

AIKIN ALHERI SAI ƊAN ARZIKI - AKY MAKAMA YA KADDAMAR DA SHIRIN LAFIYA.

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Alkaleri da Kirfi a majalisar tarayya, Hon. AKY, ya ɗauki nauyin kula da lafiyar ido kyauta ga jama’ar mazabarsa. Wannan shirin lafiya zai gudana ne tare da haɗin gwiwar kwararrun likitocin ido daga Asibitin Makkah Special Eye Hospital Bauchi, wadanda za su halarci wuraren da aka tanada domin duba lafiyar jama’a.

Abubuwan da shirin zai ƙunsa:

Masu buƙatar magungunan ido za a basu kyauta.

Masu buƙatar glass (madubi) na ido za a samar musu.

Masu buƙatar aikin ido (surgery) za a yi musu kyauta.

Wannan aiki yana da nufin saukaka wa mutane masu fama da cututtukan ido a yankin Alkaleri da Kirfi, musamman ma wadanda basu da halin zuwa manyan asibitoci ko biyan kuɗin magani mai tsada.

Hon. AKY yana daga cikin wakilan da s**a dade suna jajircewa wajen tallafa wa jama’arsu ta fannin lafiya, ilimi, da sauran cigaba. Wannan aiki na jinƙai yana daga cikin ayyukan lada da zai ci gaba da yi domin samun alkhairi a rayuwa da mulki.

Muna roƙon Allah ya ƙara masa ikon ci gaba da gudanar da irin waɗannan ayyuka masu amfani, har zuwa lokacin da Allah zai bashi nasara ya gaji ko ya fi haka, In Sha Allah.

AKY MAKAMA MEDIA
19/07 /2025

19/07/2025

AN KADDAMAR DA SHIRIN KOYAR DA MATA SANA'AR KIWON KIFI A BAUCHI

An kaddamar da sabon shirin koyar da mata sana’ar kiwon kifi kyauta karkashin Dan Galadima Aquaculture Development Program (DGADP) a yau Asabar, 19/07/2025 a Kobi, Bauchi. Wannan shirin na hadin gwiwa ne da Zidsal City Fish Farm karkashin jagorancin Alh. Yazid Tahir Naira.

An shirya shirin ne domin ba wa mata horo da tallafi don su iya dogaro da kansu ta hanyar kiwon kifi a cikin gidajensu. Mahalarta sun bayyana farin cikinsu da wannan dama da za ta taimaka musu wajen samun hanyoyin kasuwanci da habaka rayuwarsu.

Lambar Tuntuɓa:
📞 09035680626,
07069957007

19/07/2025

AN KADDAMAR DA SHIRIN KOYAR DA MATA SANA'AR KIWON KIFI A BAUCHI

An kaddamar da sabon shirin koyar da mata sana’ar kiwon kifi kyauta karkashin Dan Galadima Aquaculture Development Program (DGADP) a yau Asabar, 19/07/2025 a Kobi, Bauchi. Wannan shirin na hadin gwiwa ne da Zidsal City Fish Farm karkashin jagorancin Alh. Yazid Tahir Naira.

An shirya shirin ne domin ba wa mata horo da tallafi don su iya dogaro da kansu ta hanyar kiwon kifi a cikin gidajensu. Mahalarta sun bayyana farin cikinsu da wannan dama da za ta taimaka musu wajen samun hanyoyin kasuwanci da habaka rayuwarsu.

Lambar Tuntuɓa:
📞 09035680626,
07069957007

AN KADDAMAR DA SHIRIN KOYAR DA MATA SANA'AR KIWON KIFI KYAUTA KARKASHIN (DAN GALADIMA AQUACULTURE DEVELOPMENT PROGRAM - ...
19/07/2025

AN KADDAMAR DA SHIRIN KOYAR DA MATA SANA'AR KIWON KIFI KYAUTA KARKASHIN (DAN GALADIMA AQUACULTURE DEVELOPMENT PROGRAM - DGADP)

Yau Asabar, 19/07/2025 ne kungiyar magoya bayan Shamsudeen Bala Mohammed (Dan Galadiman Duguri) s**a kaddamar da sabon shirin koyar da mata sana’ar kiwon kifi kyauta, domin karfafa gwiwar mata wajen dogaro da kansu ta hanyar harkar kiwon kifi a cikin gidajensu.

Wannan shiri na musamman wanda aka sanya wa suna Dan Galadima Aquaculture Development Program (DGADP), an shirya shi ne tare da hadin gwiwar Kamfanin Sarrafa Kifi na Zidsal City Fish Farm, Miri Jos Road, Bauchi a karkashin jagorancin Alh. Yazid Taheer Naira .

An gudanar da kaddamarwar ne a makarantar firamare ta Kobi, Bauchi, inda mata da dama s**a samu halarta, bayan sun kammala cikewa da mika fom din shiga shirin. Mahalarta sun nuna farin cikinsu da wannan dama da aka ba su domin koyon sana’ar da za ta iya kawo sauyi a rayuwarsu da na iyalansu.

Jagoran shirin, Alh. Yazid Tahir Naira, ya bayyana cewa za a ci gaba da gudanar da horon har zuwa lokacin da mahalarta za su iya fara harkar kiwon kifi cikin sauki a gidajensu. Ya ce shirin zai ba matan dama wajen samun horo na zamani, tallafi da hanyoyin kasuwanci don tabbatar da dorewar sana'ar.

Kwamitin tsare-tsaren shirin ya hada da kwararru daga Zidsal City Fish Farm dake Bauchi, wadanda za su jagoranci koyarwar daga mataki na farko har zuwa kammala.

---

Lambar Tuntuɓa
📞 09035680626,
07069957007

Address


Telephone

08063773778

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labari Daga Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labari Daga Bauchi:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share