Labari Daga Bauchi

Labari Daga Bauchi Media News

14/04/2026

KAI TSAYE DAGA GARIN MAGAMA A KARAMAR HUKUMAR TORO...

Yanzu haka mutanen garin Magama a karamar hukumar Toro sun zabi Barr Usaini Umar Majikiran Bauchi a matsayin Dan takaran kujeran Dan majalisar tarayya Mai wakiltar karamar hukumar Toro a zaben 2027

KOTU TA BAI WA TSOHON GWAMNAN KADUNA, NASIR EL-RUFAI BELI KAN NAIRA MILIYAN 200Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kadu...
14/04/2026

KOTU TA BAI WA TSOHON GWAMNAN KADUNA, NASIR EL-RUFAI BELI KAN NAIRA MILIYAN 200

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna State, ya samu beli daga Kotun Tarayya bayan sauraron bukatar da lauyoyinsa s**a gabatar.

A hukuncin da kotun ta yanke, an amince da bayar da belin ne kan kudi Naira miliyan 200, bayan la’akari da hujjojin da bangaren kare ya gabatar, inda kotun ta bayyana cewa ya dace a ba shi damar fita bisa wasu sharudda.

Rahotanni sun nuna cewa an bayar da belin ne a shari’ar zargin almundahana da ake yi masa, wacce ke gaban kotun. Sai dai har yanzu ba a fitar da cikakken bayani kan dukkan sharuɗɗan belin ba a hukumance.

A cewar rahoton jaridar Punch Newspaper, duk da amincewa da belin, za a ci gaba da tsare El-Rufai a hannun Independent Corrupt Practices Commission (ICPC) har sai ya cika sharuddan da kotu ta gindaya.
Ana sa ran zai ci gaba da fuskantar shari’ar da ake yi a kansa har zuwa kammalawa, yayin da lamarin ke ci gaba da jan hankalin al’umma da masu bibiyar harkokin siyasa a fadin kasar nan.

JADDADA GOYON BAYA NA MUSAMMAN GA MALAM USMAN ADAMU AHMED SUPHI (2027)Dr. Anas Giade ya sake jaddada cikakken goyon baya...
14/04/2026

JADDADA GOYON BAYA NA MUSAMMAN GA MALAM USMAN ADAMU AHMED SUPHI (2027)

Dr. Anas Giade ya sake jaddada cikakken goyon bayansa ga Malam Usman Adamu Ahmed Suphi domin tsayawa takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaɓen shekarar 2027. Wannan matsayi nasa ya zo ne bisa la’akari da nagartar halayya, kwarewa, da kuma hangen nesa na Malam Usman Suphi wajen jagorantar al’umma zuwa turbar cigaba mai dorewa.

A cewarsa, lokaci ya yi da al’ummar Jihar Bauchi za su samu shugaba nagari, mai tsoron Allah, mai gaskiya da rikon amana, wanda zai yi aiki tukuru ba tare da son zuciya ba domin inganta rayuwar jama’a. Ya bayyana Malam Usman Suphi a matsayin mutum mai zurfin ilimi, gogewa a harkokin shugabanci, da kuma kwarewa wajen tafiyar da al’amuran jama’a cikin adalci da hikima.

Dr. Anas Giade ya kara da cewa, Malam Usman Suphi mutum ne mai kishin talakawa, mai sauraron koke-koken jama’a, wanda yake da cikakken shiri na bunkasa tattalin arzikin jihar ta hanyar samar da ayyukan yi ga matasa, karfafa harkokin noma da kasuwanci, da kuma jawo hankalin masu zuba jari domin habaka cigaban masana’antu.

Haka kuma, ya bayyana cewa Malam Usman Suphi na da kudurin inganta bangaren ilimi ta hanyar samar da ingantattun makarantu, tallafa wa malamai, da kuma samar da tsare-tsare da za su bai wa matasa damar samun ilimi mai amfani da zai basu damar cin gashin kansu. A bangaren lafiya kuwa, ya yi alkawarin inganta cibiyoyin kiwon lafiya tare da tabbatar da samun kulawa mai inganci ga kowa da kowa.

Bugu da kari, Malam Usman Suphi na da nagartar dabi’u irin su gaskiya, jajircewa, tawali’u, hakuri, da kuma jajircewa wajen cika alkawura. Shi shugaba ne mai hangen nesa, wanda ke da burin ganin Jihar Bauchi ta zama abar koyi a fannin tsaro, walwala da ci gaban al’umma baki daya.

A karshe, Dr. Anas Giade ya yi kira ga daukacin al’ummar Jihar Bauchi—matasa, mata, dattawa, da duk masu ruwa da tsaki—da su hada kai su mara wa wannan kuduri baya, domin tabbatar da samun shugabanci nagari wanda zai kawo sauyi na gaskiya da cigaba mai anfani ga kowa da kowa.

Allah Ya taimaka, Ya kuma tabbatar da Malam Usman Adamu Ahmed SUPHI a matsayin Jagoran Jihar Bauchi a zabe mai zuwa ameen.

14/04/2026

KAI TSAYE DAGA GARIN MAGAMA A KARAMAR HUKUMAR TORO...

Yanzu haka Barr Usaini Umar Ya samu kyakyawar tarba agun mutanen Magama

MATASHI DAN SIYASA YA BAYYANA GOYON BAYANSA GA GWAMNAN BAUCHI, YA SOKI MASU ADAWA  DA SHIGARSA APCWani matashi dan siyas...
14/04/2026

MATASHI DAN SIYASA YA BAYYANA GOYON BAYANSA GA GWAMNAN BAUCHI, YA SOKI MASU ADAWA DA SHIGARSA APC

Wani matashi dan siyasa, Alhaji Ibrahim A.I.G, ya yi kakkausar s**a ga wasu da ya kira “makiyan ci gaban jihar Bauchi” bisa adavarsu da shigar Mai Girma Gwamna cikin jam’iyyar APC.

Matashin ya bayyana cewa irin ayyukan alheri da cigaba da Gwamnan Bauchi ya gudanar a fadin jihar, idan aka rasa irin sa, hakan babbar asara ce ga al’ummar Bauchi baki daya.

Ya kara da cewa su a matsayinsu na masu kishin jihar Bauchi, suna goyon bayan duk wani mataki da zai kawo cigaba, inda ya jaddada cewa idan Gwamnan ya yanke shawarar shiga jam’iyyar APC, za su mara masa baya dari bisa dari.
Alhaji Ibrahim A.I.G ya kuma tuna irin gudunmawar da ya bayar a zaben 2023, inda ya yi aiki tukuru tare da Hon. Aliyu Aminu Garu wajen ganin an samu nasara.

Ya yi alkawarin cewa a wannan karon ma, zai kara zage damtse wajen tabbatar da samun kuri’u masu yawa daga al’ummar Nassarawa.

A cewarsa, zai ci gaba da wayar da kan matasa da mata tare da jawo goyon baya a duk inda Gwamnan ya je, sakamakon kyakkyawar alaka da fahimtar juna da ke tsakaninsu da al’ummar yankin.

Ya kammala da cewa, suna da yakinin cewa wannan hadin kai zai kawo karin cigaba da dorewar zaman lafiya a jihar Bauchi.

Address

DADA Plaza, OPPOSITE FARIYA FOUNDATION
Bauchi
ABUBAKARUMARSTATESECRETARIAT740261

Telephone

08063773778

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labari Daga Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labari Daga Bauchi:

Share