05/11/2025
Ga takaitaccen bayani a taƙaice game da labarin:
Gwamnatin Tinubu ta mayar da martani ga Amurka kan zargin tauye ’yancin addini
Gwamnatin Najeriya ta nuna rashin jin daɗi da matakin Amurka na saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargi da take ’yancin addini.
Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana hakan a Abuja, yana mai cewa matsalolin tsaro a Najeriya ba su da alaka da addini ko ƙabila, domin ta’addanci ba ya da addini.
Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai masu ƙarfi don kawo ƙarshen rashin tsaro, inda ya ce tun bayan 2023:
Sojoji sun halaka ’yan ta’adda 13,500
Sun k**a 17,000 da ake shari’a da su
Sun ceto mutane 9,800 da aka yi garkuwa da su
Ministan ya ce an samu raguwar hare-haren ta’addanci da tsattsauran ra’ayi, kuma gwamnati ta k**a shugabannin kungiyoyi da dama k**ar Mahmud Muhammad Usman, Abubakar Abba da Khalid Al-Barnawi.
Duk da matakin Amurka, Idris ya jaddada cewa Najeriya za ta ci gaba da haɗin gwiwa da Amurka da sauran ƙasashe wajen yaƙi da ta’addanci.
Ya kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa Shugaba Tinubu na jagorantar gwamnati mai nufin tsaro, ci gaba da zaman lafiya mai dorewa.