Labari Daga Bauchi

Labari Daga Bauchi Media News

Ga takaitaccen bayani a taƙaice game da labarin:Gwamnatin Tinubu ta mayar da martani ga Amurka kan zargin tauye ’yancin ...
05/11/2025

Ga takaitaccen bayani a taƙaice game da labarin:

Gwamnatin Tinubu ta mayar da martani ga Amurka kan zargin tauye ’yancin addini

Gwamnatin Najeriya ta nuna rashin jin daɗi da matakin Amurka na saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargi da take ’yancin addini.
Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana hakan a Abuja, yana mai cewa matsalolin tsaro a Najeriya ba su da alaka da addini ko ƙabila, domin ta’addanci ba ya da addini.

Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai masu ƙarfi don kawo ƙarshen rashin tsaro, inda ya ce tun bayan 2023:

Sojoji sun halaka ’yan ta’adda 13,500

Sun k**a 17,000 da ake shari’a da su

Sun ceto mutane 9,800 da aka yi garkuwa da su

Ministan ya ce an samu raguwar hare-haren ta’addanci da tsattsauran ra’ayi, kuma gwamnati ta k**a shugabannin kungiyoyi da dama k**ar Mahmud Muhammad Usman, Abubakar Abba da Khalid Al-Barnawi.

Duk da matakin Amurka, Idris ya jaddada cewa Najeriya za ta ci gaba da haɗin gwiwa da Amurka da sauran ƙasashe wajen yaƙi da ta’addanci.

Ya kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa Shugaba Tinubu na jagorantar gwamnati mai nufin tsaro, ci gaba da zaman lafiya mai dorewa.

05/11/2025

KAI TSAYE: Jawabin shugaban Ƙungiyar BAUCHI STATE APC CREDIBILITY FORUM a bayan kammala zaman tattaunawa da s**a yi a yau cikin harshen turanci.

05/11/2025

KAI TSAYE: Jawabin shugaban Ƙungiyar BAUCHI STATE APC CREDIBILITY FORUM a bayan kammala zaman tattaunawa da s**a yi a yau.

05/11/2025

HIRA KAI TSAYE ..

Sheik Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi yana karin haske kan yauma Rasul

05/11/2025

BARRISTER A. I. GARBA Yayi karin haske kan kararar da s**a shigar kan filayen Spark light dake kan Titin Maiduguri jihar Bauchi.

05/11/2025

KAI TSAYE: Shugaban hukumar tsara Birane da kula da gine-gine ta jihar Bauchi a yayin fayyace zance kan abin dake faruwa a rukunin filayen Spark light dake kan Titin Maiduguri

SABUWAR KOMISHINA TA MANYAN MAKARANTU TA JIHAR BAUCHI TA SHIGA OFISHIA ranar , 04/11/2025 —Sabuwar Kwamishinan Manyan Ma...
05/11/2025

SABUWAR KOMISHINA TA MANYAN MAKARANTU TA JIHAR BAUCHI TA SHIGA OFISHI

A ranar , 04/11/2025 —
Sabuwar Kwamishinan Manyan Makarantu ta Jihar Bauchi, Hajiya Hadiza Abdulkadir Kango, ta shiga ofishinta a yau bayan karɓar mukami daga Mrs. Lydia Tsammani, wacce aka tura Ma’aikatar Harkokin Mata.

Ta yi alkawarin ci gaba da inganta harkokin ilimi a jihar.

ANKARARWAR GAGGAWA DA KIRA GA GWAMNATIN JIHAR BAUCHI Akwai wani lamari mai tayar da hankali da ke shirin jefa jama’a da ...
05/11/2025

ANKARARWAR GAGGAWA DA KIRA GA GWAMNATIN JIHAR BAUCHI

Akwai wani lamari mai tayar da hankali da ke shirin jefa jama’a da gwamnati cikin ruɗani a yankin Spark Light Layout dake da filaye sama da 500 a kan titn Maiduguri, Bauchi.

A halin yanzu, wasu mutane da ke da hannu a harkar filaye suna amfani da hanyoyin rashin gaskiya don ƙwace filayen da gwamnati ta amince da su bisa ƙa'idodinta, sannan kuma sun ɗibi jami'an tsaro da ýan Banga a jiya Talata 04 ga Nuwamba, 2025 suna rushe gine-ginen jama’a da s**a mallaki filayen su ta halas.

Wannan wurin dai asali ne na gwamnati, wanda aka tanada domin biyan waɗanda aka biya su bas**a bayan shari'o'i da s**a yi da gwamnatin jihar Bauchi a baya ta hanyar kotu, amma yanzu ana ƙoƙarin maida shi abin cin moriyar wasu ‘yan tsiraru.

Abin da ke faruwa a yanzu ba wai kawai barazana ce ga rayuwar jama’a ba, har ma yana iya ɓata sunan gwamnati da kawo sabuwar fitina.

Muna kira ga Gwamnatin Jihar Bauchi da ta gaggauta tsoma baki cikin a wannan lamari, ta binciki abin da ke faruwa, ta kuma tabbatar da cewa duk wanda yake amfani da doka don cutar da jama’a ya fuskanci hukunci.

Adalci shi ne ginshikin zaman lafiya. Gwamnati da ta tsaya kan gaskiya tana kare kanta da mutuncin jama’arta.

Daga ƙarshe masu wannan hakkin sun roƙi jama'a saboda Allah, da su taya su yaɗa wannan saƙon har Gwamna ya gani.

Saƙon musamman daga gamayyar masu filaye da Gidaje a wajen da abin ya shafa.

MUSLIM NA FARKO YA ZAMA MAGAJIN BIRNIN NEW YORK NA AMURKA BAYAN LASHE ZABE ZOHRAN MANDAMI_____Zohran Mamdani, ɗan jam’iy...
05/11/2025

MUSLIM NA FARKO YA ZAMA MAGAJIN BIRNIN NEW YORK NA AMURKA BAYAN LASHE ZABE ZOHRAN MANDAMI
_____

Zohran Mamdani, ɗan jam’iyyar Democrat, ya zama Musulmi na farko da ya lashe zaɓen Magajin Birnin New York a Amurka.

Duk da adawar da ya fuskanta daga manyan attajirai da kuma tsohon Shugaba Donald Trump, Mamdani mai shekaru 34 ya samu nasara kan tsohon Magajin birnin, Andrew Cuomo, wanda ya tsaya takara a ƙarƙashin jam’iyyar Indipenda.

An haifi Mamdani a Uganda, iyayensa kuma ‘yan Indiya ne, sai dai s**a koma New York da zama tun yana ɗan shekara bakwai.

Me zaku ce kan hakan...?

DA DUMI-DUMI: JIHAR GOMBE SUNA CIKIN ALHERI DUMU DUMU Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna halacc...
04/11/2025

DA DUMI-DUMI: JIHAR GOMBE SUNA CIKIN ALHERI DUMU DUMU
Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna halacci da kulawa ga tsofaffin ma’aikatan jiha da na kananan hukumomi, inda ya amince da biyan Naira biliyan 8.2 a matsayin giratuti da hakkokin ritaya.

Wannan mataki na daga cikin kokarin gwamnatin sa na tabbatar da adalci da jin kai ga waɗanda s**a ba da gudunmawa wajen gina jihar Gombe.

04/11/2025

SABUWAR KOMISHINA TA MANYAN MAKARANTU TA JIHAR BAUCHI TA SHIGA OFISHI

Bauchi, 04/11/2025 —
Sabuwar Kwamishinan Manyan Makarantu ta Jihar Bauchi, Hajiya Hadiza Abdulkadir Kango, ta shiga ofishinta a yau bayan karɓar mukami daga Mrs. Lydia Tsammani, wacce aka tura Ma’aikatar Harkokin Mata.

Ta yi alkawarin ci gaba da inganta harkokin ilimi a jihar.

04/11/2025

KOMISHINAN MANYAN MAKARANTU TA JIHAR BAUCHI, MRS. LYDIA TSAMMANI, TA YI BAN KWANA DA OFISHINTA, TA KOMAWA SABON MUKAMI NA KOMISHINAN MATA

4/11/2025 —
Kakakin Ma’aikatar Manyan Makarantu ta Jihar Bauchi, Mrs. Lydia Tsammani, ta yi ban kwana da ofishinta domin komawa sabon mukamin da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Muhammad (Kauran Bauchi), ya ba ta a matsayin Komishinan Mata.

A wajen taron ban kwana, ta gode wa Gwamnan Jihar bisa sake ba ta dama da kuma ma’aikatan ma’aikatar bisa haɗin kai da goyon baya da s**a nuna a lokacin aikinta.

Ta ce za ta ci gaba da aiki da jajircewa a sabon mukamin domin ci gaban mata da jihar Bauchi baki ɗaya.

Address

DADA Plaza, OPPOSITE FARIYA FOUNDATION
Bauchi
ABUBAKARUMARSTATESECRETARIAT740261

Telephone

08063773778

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labari Daga Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labari Daga Bauchi:

Share