19/07/2025
KUNGIYAR ABG BOYS TA KARAMAR HUKUMAR DARAZO TA NEMI DR. ADAMU BABAYO GABARIN YA FITO TAKARAR KUJERAR GWAMNAN JIHAR BAUCHI A SHEKARAR 2027
Kungiyar ABG Boys da ke karamar hukumar Darazo, Jihar Bauchi ta bayyana bukatar ta ga Dr. Adamu Babayo Gabarin, kwamishinan matasa da wasanni na jihar, da ya tsaya takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2027, bisa la’akari da irin ayyukan alheri da ya riga ya shimfida a fadin jihar Bauchi tun daga lokacin da yake rike da mukamai daban-daban a gwamnatin jihar.
Shugaban kungiyar ya bayyana hakan ne ga manema labarai, inda ya ce sun yanke wannan shawara ne bayan sun yi nazari kan tarihin ayyukan Dr. Babayo Gabarin tun daga lokacin da yake matsayin Kwamishinan Gidaje da Tsare-tsaren Kasa (Lands and Survey), S.A bangaren lafiya, kakakin jam’iyyar PDP har zuwa matsayin kwamishinan matasa da wasanni.
Abubuwan da s**a ja hankalin kungiyar ABG Boys sun hada da:
Nadin Mukamai (Appointment):
Kungiyar ta bayyana cewa ABG ya baiwa matasa sama da mutum 20 mukamai a lokacin da yake kwamishina, wanda hakan ya basu dama su taimaki kansu da wasu a cikin al’umma.
Shirye-shirye (Programs):
Ya samar da dama ga matasa maza da mata ta hanyoyi daban-daban kamar SMC, New Incentive da sauran shirye-shirye, inda kowane wata suke amfana da akalla Naira 40,000, wasu har suna biya wa iyayensu da ‘yan uwansu bukatu daga wannan dama.
Rabon Hectar (Gona):
ABG ya bai wa matasa fiye da hektoci 300 na filayen noma, inda kowanne ke da darajar sama da Naira 300,000 a yau. Wasu sun noma don iyalansu, wasu kuma sun taimaki gidajensu.
Biyan Kudaden Karatu (School Fees):
Ya dauki nauyin yara da dama wajen biyan kudin NECO/JAMB da kula da lafiyarsu daga farko har zuwa kammala karatu. Har yanzu yana ci gaba da biya su sama da Naira 1.8m a kowacce shekara.
Jarin Kasuwanci (Empowerment):
ABG ya tallafa wa matasa da mata da jarin kasuwanci, inda wasu s**a karbi Naira 50,000, 100,000 har ma da 300,000 domin su fara sana’o’insu.
Jawabin Shugaban Kungiyar ABG Boys:
“Idan za mu cire adawar siyasa, Dr. Adamu Babayo Gabarin tamkar abin koyi ne ga sauran ‘yan siyasar Bauchi. Wannan ne irin aikin da muke so. Wanda ke ba da dama, taimako da tallafi. Mu dubi gaskiya, duk wanda zai yi mana irin wannan hidima a siyasance, masoyi ne.”
Kungiyar ta kuma ce siyasa ba karya ba ce, kuma lokaci yayi da za a cire adawar siyasa a tallafa masa domin ci gaba da amfanar da al’umma gaba daya.
A KARSHE KUNGIYAR TA CE:
“ABG For Governor 2027.”
Allah ya saka da gidan Aljanna wa iyayen ka.”
Wannan sanarwa ce daga: Mai magana da yawun ABG Boys, Nura Adamu Beti (Comr. D. Beti) Mataimakin Kwamishina, Bangaren Sadarwa. Ranar 07/2025.