Labari Daga Bauchi

Labari Daga Bauchi Media News

Kungiyar ZAMFARAWA FAMILY GROUP Ta Shirya Babban Taron Sada Zumunta a BauchiKungiyar ZAMFARAWA FAMILY GROUP Multipurpose...
31/12/2025

Kungiyar ZAMFARAWA FAMILY GROUP Ta Shirya Babban Taron Sada Zumunta a Bauchi

Kungiyar ZAMFARAWA FAMILY GROUP Multipurpose Cooperative Society Limited, ƙarƙashin jagorancin Sagir Adamu Alkali da Jumba Aliyu, ta sanar da shirya Babban Taron Sada Zumunta na Ƙarshen Shekara domin ƙarfafa haɗin kai, zumunci da fahimtar juna a tsakanin ’ya’yan dangin Zamfarawa da ke zaune a jihar Bauchi da maƙwabta.

A cewar shugabannin ƙungiyar, taron zai haɗa ilahirin al’ummar dangin Zamfarawa daga sassa daban-daban, tare da halartar manyan baki daga cikin wannan dangi mai albarka, ciki har da Alhaji Hussaini Ahmad, Imam Abdulrahman Ibrahim Idris, Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, da kuma Malam Yakubu Abubakar Gero, Babban Kwamishina na Ɗaya a Hukumar Shari’a ta Jihar Bauchi.
Shugabannin ƙungiyar sun bayyana cewa an shirya wannan taro ne domin ƙara dankon zumunci, musayar ra’ayoyi masu amfani, da kuma duba hanyoyin da za su taimaka wajen bunƙasa rayuwar ’ya’yan dangi ta fuskar zamantakewa da ci gaba mai ɗorewa.

An tsara taron zai gudana ne a ranar Alhamis, 1 ga Janairu, 2026, daga ƙarfe 9:00 na safe zuwa 3:00 na yamma, a Masallacin Fada (Central Masjid Hall), Bauchi.

A ƙarshe, shugabannin ƙungiyar sun yi kira ga dukkan ’ya’yan dangin Zamfarawa da ke jihar Bauchi da kewaye da su fito su halarta domin samun albarkar taro, tare da roƙon Allah Ya sanya a yi taro lafiya, a kammala lafiya.

ABINDA YA WAKANA YAU A OFISHIN JAM’IYYAR APC NA JIHAR BAUCHI SHIRIN KADDAMAR DA HORO GA SUPERVISORS....!!! A yau, Jam’iy...
30/12/2025

ABINDA YA WAKANA YAU A OFISHIN JAM’IYYAR APC NA JIHAR BAUCHI
SHIRIN KADDAMAR DA HORO GA SUPERVISORS....!!!

A yau, Jam’iyyar APC ta Jihar Bauchi ta kaddamar da horo ga Supervisors ta hanyar yanar gizo (online training). Wannan horon ya shafi membership registration, inda aka koya wa masu horon yadda za su gudanar da rajistar mambobi da kuma kula da tsarin gudanarwa yadda ya kamata.

Horarwar na daga cikin shirye-shiryen jam’iyyar na inganta tsare-tsaren gudanarwa a matakin jiha, tare da tabbatar da cewa duk mambobin jam’iyyar suna samun damar yin rajista cikin sauƙi da gaskiya.

Shugabannin jam’iyyar sun bayyana cewa horon zai taimaka wajen inganta aikin Supervisors, musamman wajen gudanar da rajistar mambobi da kuma tabbatar da bin ka’idoji a dukkan matakai.

Jam’iyyar ADC Ta Kira Taron Manema Labarai a Jihar BauchiJam’iyyar African Democratic Congress (ADC) reshen jihar Bauchi...
30/12/2025

Jam’iyyar ADC Ta Kira Taron Manema Labarai a Jihar Bauchi

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) reshen jihar Bauchi ta kira taron manema labarai domin bayyana matsayarta kan muhimman batutuwa da s**a shafi jam’iyyar, da kuma wasu al’amura na siyasa a halin da ake ciki.
Taron, wanda aka gudanar a jihar Bauchi, ya samu halartar shugabannin jam’iyyar a matakin jiha, tare da wakilan kafafen yaɗa labarai daban-daban.

A yayin taron, shugabannin ADC sun yi bayani kan tsarin jam’iyyar, kalubalen da take fuskanta, da tsare-tsaren ta na gaba, tare da yin kira ga mambobi da magoya baya da su ci gaba da kasancewa masu haɗin kai domin ƙarfafa jam’iyyar a jihar.
Jam’iyyar ta kuma yi amfani da damar wajen amsa tambayoyin ’yan jarida, tana mai jaddada ƙudirin ta na tafiya a kan turbar dimokiraɗiyya da bin doka da oda.

ME ZAKU CE KAN HAKAN....?

“Ba Mu da Wata Boyayyar Manufa Kan ’Yan Adawa” — Gwamnatin TarayyaGwamnatin Tarayya ta Nijeriya ta sake jaddada ƙudirin ...
30/12/2025

“Ba Mu da Wata Boyayyar Manufa Kan ’Yan Adawa” — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta Nijeriya ta sake jaddada ƙudirin ta na bin doka da oda, tare da yin watsi da zarge-zargen da ke ikirarin cewa tana shirin kai hari ko tsangwama ga ’yan adawa a ƙasar nan.
Gwamnatin ta bayyana cewa ba ta da wani shiri na kamawa, tsarewa ko gurfanar da ’yan adawa ba bisa ƙa’ida ba, tana mai cewa duk wani zargi a wannan fanni ƙarya ne tsagwaronta.

Wannan bayani ya fito ne daga Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, biyo bayan ɓullar wata takardar bogi da ke yawo a kafafen sadarwa, wadda ta yi ikirarin cewa an kafa wata rundunar haɗin gwiwa mai suna “ADP4VIP” (Arrest, Detain, Prosecute for Very Important Persons).
Ministan ya ce takardar ta yi ƙaryar cewa wai rundunar ta haɗa da EFCC, ICPC, NFIU tare da jagorancin Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaron Ƙasa, domin kai farmaki ga fitattun ’yan adawa ba tare da bin doka ba.

Ya ce masu yaɗa wannan ƙarya sun fake da abin da s**a kira “majiyoyi masu tushe” ne kawai domin raunana harkokin siyasar ’yan adawa, musamman ’yan jam’iyyar African Democratic Congress (ADC)

Alhaji Mohammed Idris ya jaddada cewa:
“Babu wani shiri mai suna ADP4VIP. Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu tana mai da hankali ne kan aiwatar da muhimman manufofinta, ciki har da sauye-sauyen tattalin arziki, yaƙi da matsalar tsaro, faɗaɗa damar kasuwanci da dawo da amincewar masu zuba jari.”
Ya ƙara da cewa, ƙoƙarin da wasu ’yan adawa ke yi na fassara bin doka a matsayin tsangwama, wata dabara ce da ake amfani da ita domin kare wasu manyan mutane daga fuskantar hukuncin doka da ayyukan hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa.

Ministan ya kuma yi nuni da Sashe na 40 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 (da aka yi wa gyara), wanda ya bai wa ’yan ƙasa ’yancin haɗuwa da taruwa ba tare da tsangwama ba, yana mai cewa Shugaba Tinubu ya rantse wajen kare kundin tsarin mulki da dukkan tanade-tanadensa.
“Shugaba Tinubu cikakken mai bin tafarkin dimokiraɗiyya ne, kuma a ƙarƙashin jagorancinsa, Gwamnatin Tarayya tana girmama doka, bin ƙa’ida da ’yancin aiki na hukumomi ba tare da tsoma baki ba.”

Ministan ya yi kira ga ’yan siyasa da al’umma gaba ɗaya da su guji yaɗa labaran ƙarya da ruɗani, musamman yayin da ake tunkarar manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2027.

Ya ce ’yan Nijeriya su kasance masu lura da labaran da suke karantawa da yadawa, tare da ƙin amincewa da siyasar rarrabuwar kai da karkatar da gaskiya.
A ƙarshe, Ministan ya tabbatar da cewa yayin da ake rufe shafin shekarar 2025 ana shiga sabuwar shekara, Gwamnatin Tinubu ba za ta bari siyasar banza ta ɗauke mata hankali ba, domin ’yan Nijeriya sun cancanci cigaba mai ɗorewa da sakamako a fili.

ME ZAKU CE KAN HAKAN....?

Musulunci Ya Samu Karuwa: Mutane 1,758 Sun Karɓi Addinin Musulunci a Jihar Bauchi.Addinin Musulunci ya samu gagarumar ka...
30/12/2025

Musulunci Ya Samu Karuwa: Mutane 1,758 Sun Karɓi Addinin Musulunci a Jihar Bauchi.

Addinin Musulunci ya samu gagarumar karuwa yayin da mutane dubu ɗaya da dari bakwai da hamsin da takwas (1,758) s**a karɓi Musulunci a ƙarƙashin ƙungiyar Muslim Professionals in Da’awah (MPD) ta ƙasa da reshen jihar Bauchi.

Wannan ya faru ne a yayin gagarumin gangamin ayyukan Da’awah na shekara-shekara da ƙungiyar MPD ta saba gudanarwa, wanda a wannan karo aka shirya kuma aka aiwatar da shi a ƙananan hukumomin Ganjuwa da Toro na jihar Bauchi.

Taron ya samu halartar mambobin ƙungiyar daga sassa daban-daban na ƙasar nan, inda kowa ya bada tasa gudunmawa domin ganin ayyukan sun gudana cikin nasara.

A yayin gudanar da wannan gangami, an aiwatar da aikin jinya kyauta ga al’umma, ba tare da la’akari da addini ko bambancin ra’ayi ba, domin Musulmi da waɗanda ba Musulmi ba sun amfana da wannan hidima ta jinƙai.

A ƙarshen taron, ƙungiyar MPD ta buƙaci goyon baya da tallafi a fannoni daban-daban da s**a haɗa da:

Daukar nauyin Hafizai da Malaman Da’awah,

Kayan sawa (tufafi) ga sababbin Musulmi,

Gina rijiya ko burtsatse (borehole),
Da kuma gina masallatai a yankunan da ake bukata.

Masu neman ƙarin bayani za su iya tuntuba ta lambobin waya kamar haka:
📞 08038879139
📞 08029811055
📞 08036385797

An gudanar da wannan gagarumin taro ne daga ranar 25 zuwa 28 ga watan Disamba, 2025

Rahoto:
Mubarak Abubakar Bauchi
Admin Secretary, MPD Bauchi

GAYYATA! GAYYATA!! GAYYATA!!!MADARASSATUL MU’AZU BIN JABAL AL-LITHIFIZUL QUR’ANI ISLAMIYA(Malam Sarki Giade)A madadin Sh...
30/12/2025

GAYYATA! GAYYATA!! GAYYATA!!!
MADARASSATUL MU’AZU BIN JABAL AL-LITHIFIZUL QUR’ANI ISLAMIYA
(Malam Sarki Giade)

A madadin Shugaban makarantar, muna farin cikin gayyatar ‘yan uwa, abokan arziki da daukacin al’umma zuwa taron yaye daliban karatun Al-Qur’ani mai girma karo na bakwai (07).

A wannan yaye-yaye, makarantar za ta yaye dalibai maza da mata guda sittin da takwas (68), ciki har da masu karatun Tarteel da Warsh, Alhamdulillah.
MANYAN BAKI NA MUSAMMAN
Taron zai samu halartar manyan baki masu daraja, daga cikinsu akwai:
HRH Alh. Sabo Abdulkadir Mohammed, Maimartaba Sarkin Giade
Alh. Abubakar Sadiq, Wazirin Giade
Hon. Usman Muhammad Saleh, Shugaban Karamar Hukumar Giade (Sa’in Giade) Hon. Yakubu Adamu, PhD, Kwamishinan Kuɗi Hon. Mohammed Ali Pate, Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a Sen. Shehu Buba Umar
’Yan Majalisu, Kwamishinoni, Sarakuna, Manyan Malamai, Jami’an Tsaro da sauran manyan baki masu daraja.

MANYAN MALAMAI MASU WA’AZI
Sheikh Ja’afar Muhammad Rabi’u Gulbum
Sheikh Malam Alhaji Tata Azare

TARON ZAI GUDANA - :

Rana: Alhamis, 01/01/2026
Lokaci: Karfe 4:00 na yamma
Wuri: Harabar makarantar Madarassatul Mu’azu Bin Jabal, kusa da Gidan Ruwan Walima, Giade

Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya ba mu ikon halarta, Ya kuma sanya taron ya kasance mai albarka.

Allahumma Ameen.

NAJERIYA TA KAMMALA WASANNIN RUKUNI CIKIN ƊAUKAKA — NASARA TA UKU A JERE A AFCON 2025NIGERIA 🇳🇬 3 UGANDA 🇺🇬 1Ƙungiyar ƙw...
30/12/2025

NAJERIYA TA KAMMALA WASANNIN RUKUNI CIKIN ƊAUKAKA — NASARA TA UKU A JERE A AFCON 2025

NIGERIA 🇳🇬 3 UGANDA 🇺🇬 1
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya (Super Eagles) ta nuna cikakken ƙwazo da ƙarfi a gasar AFCON 2025, bayan da ta doke Uganda da ci 3–1, inda ta kammala dukkan wasannin rukuni ba tare da rashin nasara ba.

Wannan sakamako ya zama nasara ta uku a jere, abin da ke nuna shiri, haɗin kai da burin lashe kofin da ‘yan wasan Najeriya ke da shi. Masoya ƙwallon ƙafa a fadin ƙasar sun cika da murna da alfahari, suna ganin wannan a matsayin alamar alheri kafin shiga matakan ƙarshe na gasar.

Yanzu idanu sun koma kan wasannin gaba, yayin da ake sa ran Super Eagles za su ci gaba da ɗaga tutar Najeriya a nahiyar Afirka.

30/12/2025

Kungiyar Bauchi Development Forum ƙarƙashin jagorancin Banu Yakubun Bauchi ta kai ziyarar taya murna ga sabon Shugaban TUC na Jihar Bauchi, Alhaji Umar Tafida. Sun nuna farin ciki da goyon baya gare shi, tare da jaddada kwarin gwiwa cewa zai yi shugabanci nagari wajen kare haƙƙin ma’aikata. A nasa jawabin, Alhaji Umar Tafida ya gode musu, yana mai tabbatar da aniyarsa ta tafiyar da TUC bisa gaskiya, haɗin kai da riƙon amana domin ci gaban ma’aikata da jihar Bauchi

30/12/2025

KAI TSAYE....

Taron Manema Labarai na Jam'iyar ADC a jihar Bauchi

SABON SHUGABAN TUC NA JIHAR BAUCHI YA KARƁI ZIYARAR TAYA MURNA DAGA ’YAN UWA ZURIYAR BANI YAKUBUKungiyar Bauchi Developm...
30/12/2025

SABON SHUGABAN TUC NA JIHAR BAUCHI YA KARƁI ZIYARAR TAYA MURNA DAGA ’YAN UWA ZURIYAR BANI YAKUBU

Kungiyar Bauchi Development Forum, ƙarƙashin jagorancin Banu Yakubun Bauchi, ta kai ziyarar taya murna ga sabon Shugaban Ƙungiyar Ma’aikata ta Ƙasa (TUC) na Jihar Bauchi, Alhaji Umar Tafida.

Shugabannin da s**a halarci ziyarar sun haɗa da:Chairman: Barr. Muktar Othman Esq., tsohon Attorney General
Vice Chairman: Alhaji Yusuf Marafa
Secretary General: Alhaji Mahmood Aminu Adamu Junba.

A yayin ziyarar, ƙungiyar ta kuma yi amfani da damar wajen nuna godiya bisa naɗin mutane biyu da aka ba su guraben ayyuka a muhimman wurare, lamarin da s**a bayyana a matsayin abin alfahari ga al’umma

Ziyarar ta gudana ne domin nuna farin ciki, alfahari da cikakken goyon baya ga sabon shugaban TUC, bisa amana da aka ɗora masa. ’Yan uwa zuriyar Bani Yakubu sun bayyana cikakkiyar kwarin gwiwarsu cewa Alhaji Umar Tafida zai yi shugabanci nagari, tare da jajircewa wajen kare muradun ma’aikata da inganta walwalarsu a faɗin Jihar Bauchi.
Haka kuma, sun jaddada cewa Bauchi Development Forum na da aniyar ci gaba da ba da haɗin kai da shawarwari masu amfani domin ƙarfafa zaman lafiya, adalci da bunƙasar harkokin ma’aikata a jihar.

A nasa jawabin, Alhaji Umar Tafida ya nuna matuƙar godiya ga Bauchi Development Forum da ’yan uwa zuriyar Bani Yakubu bisa wannan ziyara da goyon bayan da s**a nuna masa. Ya tabbatar da aniyarsa ta tafiyar da harkokin TUC bisa gaskiya, riƙon amana da haɗin kai, tare da fifita kare haƙƙin ma’aikata a kowane lokaci.

Ziyarar taya murnar ta kasance wata muhimmiyar alama ta ƙarfafa zumunci, haɗin kai da kyakkyawar dangantaka tsakanin ƙungiyoyin ci gaban al’umma da ƙungiyar ma’aikata, domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Bauchi.

30/12/2025

HIRA KAI TSAYE...

Makoman yan Nigeria in Tunubu ya dawo karo na biyu..

Daga Alh Abdulhamid Dankyarko

Address

DADA Plaza, OPPOSITE FARIYA FOUNDATION
Bauchi
ABUBAKARUMARSTATESECRETARIAT740261

Telephone

08063773778

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labari Daga Bauchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Labari Daga Bauchi:

Share