ASU Media TV

ASU Media TV ASU Media TV Online. 09037484655

ASU MEDIA Gidan Jaridace ta Mai Zamanka wacce aka Samar da ita Dan isar da sakonni tareda fitar da sahihan labarai, Da kuma tallace-tallace wa kamfanoni da sauransu.

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya ƙaddamar da aikin gina wuraren shaƙatawa da gwamnatin Bauchi zata yi kan n...
10/08/2026

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya ƙaddamar da aikin gina wuraren shaƙatawa da gwamnatin Bauchi zata yi kan naira biliyan 4.68.

DA DUMI-DUMI: Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya ayyana Musulma Hon. Zainab Abubakar Ibrahim a matsayin wadda za ta ma...
07/08/2026

DA DUMI-DUMI: Gwamna Agbu Kefas na jihar Taraba ya ayyana Musulma Hon. Zainab Abubakar Ibrahim a matsayin wadda za ta mara masa baya a matsayin mataimakiyar gwamna a zaben 2027.

Me zaku ce?

Sponsored:-OFFICIAL CONGRATULATORY MESSAGE: APPOINTMENT AS CEO, WORLD ENERGY COUNCIL NIGERIAIt is with immense pride and...
07/08/2026

Sponsored:-

OFFICIAL CONGRATULATORY MESSAGE: APPOINTMENT AS CEO, WORLD ENERGY COUNCIL NIGERIA

It is with immense pride and personal satisfaction that I extend my warmest congratulations to you, Dr. Bala Wunti, on your appointment as the Chief Executive Officer of the World Energy Council, Nigeria.
Your elevation to this prestigious global position is a testament to your decades of dedicated service, profound technical expertise, and unwavering commitment to the advancement of the Nigerian energy sector. Having followed your distinguished career, I have observed firsthand your capacity for visionary leadership and your ability to navigate complex challenges with intellectual rigor and integrity.

The World Energy Council plays a pivotal role in shaping the global energy transition, and having a son of Bauchi State at the helm of its Nigerian operations brings great honor to our state and nation. I am confident that under your stewardship, the Council will achieve significant milestones in fostering energy security, promoting sustainable practices, and driving innovative policy solutions that align with Nigeria's developmental aspirations.

As you embark on this critical assignment, I pray that the Almighty grants you the wisdom, strength, and health to lead with distinction. Your success is a beacon of hope and inspiration for the younger generation of professionals across our great country.
Please accept the assurances of my highest regards and best wishes as you continue to serve our nation on this global stage.
Sincerely,

(Signed)
H.E. Barr. M.A. Abubakar, SAN
Former Governor of Bauchi State &
APC Gubernatorial Candidate, 2027

Through:
Moh’d Alkasim
New Media Aide to H.E. M.A. Abubakar, SAN

Yanzu haka cikin daren nan gidan man AY Shafa dake bayan Rita Lori Hotel a Garki, Area 8 Abuja ya k**a da wuta.
06/08/2026

Yanzu haka cikin daren nan gidan man AY Shafa dake bayan Rita Lori Hotel a Garki, Area 8 Abuja ya k**a da wuta.

Isma"il Alhassan Musa YA bayyana ficewarsar daga Jam'iyyar ADC mai alamar musabaha.
06/08/2026

Isma"il Alhassan Musa YA bayyana ficewarsar daga Jam'iyyar ADC mai alamar musabaha.

04/08/2026

TIRKASHI: Nuhu Dan Hausa ya yi wa Rarara wankin babban bargo akan wakar s**ar Isah Ali Pantami!

Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da sakin kuɗi Naira miliyan 618,312,000 domin biyan tallafin karatu ga ɗaliban jihar 15...
04/08/2026

Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da sakin kuɗi Naira miliyan 618,312,000 domin biyan tallafin karatu ga ɗaliban jihar 15,000 da aka zaɓa a ƙarƙashin Shirin Tallafin Karatu na Cikin Gida na shekarar 2026.

Ana sa ran fara biyan kuɗaɗen ne da kaso na farko, wanda zai shafi ɗalibai daga cibiyoyin ilimi 14 da ke cikin jerin farko na shirin.

Cibiyoyin sun haɗa da Jami'ar Sa'adu Zungur (SAZU), Jami'ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU), Kwalejin Ilimi ta Azare, Abubakar Tatari Ali Polytechnic, Federal Polytechnic Bauchi, Adamu Tafawa Balewa College of Education Kangere, College of Agriculture Bauchi, Aliko Dangote College of Nursing Sciences Bauchi, Bill and Melinda Gates College of Health Sciences and Technology da ke Ningi, A.D. Rufai College of Legal and Islamic Studies da ke Misau, School of Nursing ta Asibitin Koyarwa na ATBU, Al-Muhibbah Open University, Bauchi Oil and Gas Academy da ke Alkaleri, da kuma Federal College of Education Jama'are.

Shirin tallafin karatun na cikin gida na gwamnatin jihar na da manufar tallafa wa ɗaliban Bauchi da ke karatu a manyan makarantun gaba da sakandare, domin rage musu nauyin kuɗaɗen karatu da kuma ƙarfafa su wajen ci gaba da neman ilimi.

Ana sa ran waɗanda aka zaɓa za su fara karɓar kuɗaɗen tallafin bisa tsarin da Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Bauchi ta tanada.

ASU MEDIA TV

-Zamani TV

Mun Samu damar kai ziyara na musamman wa Shugaban rundunar Yansandan Jihar Bauchi CP ........ a Ofishinsa dake Police He...
04/08/2026

Mun Samu damar kai ziyara na musamman wa Shugaban rundunar Yansandan Jihar Bauchi CP ........ a Ofishinsa dake Police Headquarters anan cikin garin Bauchi.

Tawagar namu ta kai wannan Ziyarar ne don sada zumunci tareda Jinjinanwa Shugaban Yansanda bisa irin kokarinsa na inganta Tsaro a Jihar Bauchi Tareda tabbatuwar zaman lafiya musamman wajen kyautata alaka tsakanin Jimi'an tsaro da Al'ummar jihar Bauchi.

Sannan Hon Umar Ibrahim Sade wanda yake jagorantar tawagar ya bayyanawa Shugaban Yansandan cewa wannnan tawagar ta kawo masa wannan ziyarar ne dan kara karfafa alaka tsakanin Tawagar Jagororin yada labarai na gidan M A da rundunar Yansandan .

A yayin da Shugaban Yansandan yake nasa jawabin ya bayyana jin dadin sa, da wannan ziyarar da muka kai mishi.
Daga karshe ya mana fatan Alkhairi akan abinda muka agaba da kuma Allah ya maida mungida lafiya.

Acikin tawagar namu akwai Tsohon Kwamishinan Yada labarai na Jihar Bauchi Umar Ibrahim Sade wanda shine ya jagorancemu, sannan akwai Shamsuddeen Lukman Abubakar Mataimaki na Musamman ga M.A Abubakar SAN a fannin Sadarwa, akwai ni Moh'd Alkasim Mataimaki na musamman a fannin Sadarwa na zamani wa tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Mohammed Abdullahi Abubakar, sai tsohon Shugaban Gidan TV na BATV Comr Ningi da kuma Hajiya Hansa'u Ibrahim .

Moh'd Alkasim II Mataimaki na Musamman a fannin Sadarwa na zamani wa M.A Abubakar SAN Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi

Masu skills irin na Professor Isa Ali Pantami a kamfanin Google, Microsoft, Amazon da Binance tamu ta crypto duk shekara...
02/08/2026

Masu skills irin na Professor Isa Ali Pantami a kamfanin Google, Microsoft, Amazon da Binance tamu ta crypto duk shekara ana biyansu daga $300,00 zuwa $450,000, Wato daga Naira Million 411, Zuwa Million 616.

Wannan salary kenan banda stock bonus na kamfani. Ana kiran skill din Chief Information Security Officer, Wato shugaban dake kula da bangaren Cybersecurity, Irin wannan aikin Malam ya yiwa Nigeria a 2023.

Sannan Irinsu malam dai sune AI Research Scientist, Wadanda duk shekara suna samun salary a shekara daga $250k zuwa $650k Wato daga 342 Million zuwa 930 Million Naira, Haka ake biyan wadanda suke aiki a AI Mind, Microsoft d.s.s.

A bangaren consultantation da malam babban kamfani ne dashi a Abuja a wannan bangaren, bincike ya tabbatar da Cybersecurity consultants suna iya samun abinda bai gaza $300k ba a shekara, Wato dama 400 Million Naira. Banda sauran ayyukan da suke yiwa Gwamnati kamfanoni a kasashen Duniya da suna iya samun biliyoyin kudade a shekara.

Skill irin na Cybersecurity, AI Research da Technology Consulting suna daga cikin ayyukan da ake biya mafi tsada a duniya saboda suna da matukar muhimmanci ga tsaron bayanai da cigaban fasaha.

Idan mutum ya kai matakin da kamfanonin duniya k**ar Google, Microsoft, Amazon ko Binance suke nema, samun manyan kudade ba abin mamaki bane.

A maimakon mutane su rika mamakin arzikin masu ilmi, ya k**ata mu fara girmama knowledge economy da value na expertise. A wannan zamanin, ilmi da skill sun fi yawancin albarkatu daraja.

Irin wadannan mutanen kake tambaya ina s**a samu kudaden siyan gidaje a Abuja? 🤣🤣🤣 Dan Allah kai mai tambaya bakaji kunya ba? 🤔

Wannan fa kadan ne daga cikin skills biyu kacal na lissafo wanda malam yake dasu wanda ga abinda masu su suke samu a duniya. Banda sauran harkokin manyan business dinshi da yake gudanarwa.

Daga Abba Sani Pantami

SHEHU BUBA UMAR DA MANSUR MANU SORO BABU SUNANSU A TAKARDA DA INEC TAFIYAR YAU .Yan takaran da sunayensu yayi batan dabo...
02/08/2026

SHEHU BUBA UMAR DA MANSUR MANU SORO BABU SUNANSU A TAKARDA DA INEC TAFIYAR YAU .

Yan takaran da sunayensu yayi batan dabo cikin jadawalin sunayen yan takaran da Hukumar Zabe mai zaman kanta na INEC ta fitar.

Duk da cewa lamarin ya shafi yan takarkari da dama daga jihohin kasar nan , a Jihar Bauchi Sanata Shehu Buba ya Sanata Mai ci ayanzu haka , sanan kuma dan takaran Gwamnan Jihar Bauchi a Jam'iyyar PRP da Hon Mansur Manu Soro dan Majalisan tarayya mai wakiltan Ganjuwa darazo sune sunayensu bai bayyana ba a cikin takardan da Hukumar Zabe Mai Zaman kanta INEC ta fitar a yau .

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ASU Media TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ASU Media TV:

Share