ASU Media TV

ASU Media TV ASU Media TV Online. 09037484655
(1)

ASU MEDIA Gidan Jaridace ta Mai Zamanka wacce aka Samar da ita Dan isar da sakonni tareda fitar da sahihan labarai, Da kuma tallace-tallace wa kamfanoni da sauransu.

CBN zata fitar da sabbin takardun kuɗi na N10,000 da N20,000‎
30/10/2025

CBN zata fitar da sabbin takardun kuɗi na N10,000 da N20,000

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da sabon haraji na kashi 15% ga ƴan kasuwa masu shigo da man fetur da dizal zuwa...
30/10/2025

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da sabon haraji na kashi 15% ga ƴan kasuwa masu shigo da man fetur da dizal zuwa Nijeriya

Tambaya Shin dame - dame ya kamata Mai mota ya tabbatar ya tanada Dan gujewa kamu da hukunci daga Hukumar BAROTA ?Haka m...
30/10/2025

Tambaya

Shin dame - dame ya kamata Mai mota ya tabbatar ya tanada Dan gujewa kamu da hukunci daga Hukumar BAROTA ?

Haka ma me mashin na ACHABA?

Da Me mashin na hawa dun zurga zurgan biyan bukatu na yau da kullum.

Shine masu Keke ma suna ciki ne ko a'a ?

Ina wannan tambayar ne dan watakila bazan rasa abota da wani Jami'in Barota ba, ko Kuma Wanda yake da masaniya ko ilimi akan dokokin Hukumar BAROTAN.

Sannan tayiwu akwai mutane makamanta na masu bukatar Karin sani Gameda Dokokin Hukumar BAROTA .

Daga:- Moh'd Alkasim

Alhaji Saleh Danburam Misau Yayi Murabus Daga Kujeranshi Na Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Bauchi.
28/10/2025

Alhaji Saleh Danburam Misau Yayi Murabus Daga Kujeranshi Na Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Bauchi.

Shugaba Tinubu ya bukaci Majalisar Dattawa da ta tabbatar da sabbin shugabannin rundunonin tsaro daya nada
28/10/2025

Shugaba Tinubu ya bukaci Majalisar Dattawa da ta tabbatar da sabbin shugabannin rundunonin tsaro daya nada

     Yana da kyau masu fada aji da Kuma ita Karan kanta Gwamnati .Ta Mika hankalinta Ga Hukumar BAROTA duba da abinda ya...
28/10/2025


Yana da kyau masu fada aji da Kuma ita Karan kanta Gwamnati .
Ta Mika hankalinta Ga Hukumar BAROTA duba da abinda ya faru a titin kofar Ran dake cikin Jihar Bauchi.

Banida cikakken masaniya Gameda abinda ya faru amman naji cewa Sun take wani ko Sun kade shine Oho....
Sannan ance wai Wanda s**a Kaden yadebo yarane daga makaranta sai s**ayi kokarin tsare shi sakanakon rashin PLATE NUMBER na abin hawan .

Yanada kyau a Kara wa Yan BAROTA haro Dan su San Aikin da kyau , Sannan su San yanda zasu dinga tunkarar masu laifi .

Na fahimci cewa BAROTA sunyi Kaurin suna awajen Al'umma Sannan sunyi bakin jini duba da yanda nake Jin korafe korafe daga wajen Al'umma. Duk da cewa dama aiki irin nasu dole sai an fiskanci kyara da kushe da Kuma nuna gazawa , tsangwada da Sauran su.
Amman yanada kyau ita HUKUMAR BAROTA na Jihar Bauchi, su dinga sassautawa, ba komai ne za'a dinga nuna karfi da Girman Iko irin na Gwamnati ba, Musamman in akayi la'akari da cewa Al'umma kusan a fusace suke Kuma komai na Iya faruwa idan aka matsa lamba.
Dan haka yanada kyau Hukumar BAROTA Susan yanda zasu dinga tunkarar mutane idan s**a fita bakin Aiki.

Ba ina nufin Karsu cigaba da Aikin su bane sai dai Ina nusar dasu cewa su Kara horar da ma'aikatansu ta Inda zasu kirkiro sabon salon da zasu kyautata alakarsu da Al'umma Kuma su cigaba da aikinsu cikin sauki da lumana batare da fuskantar tsana ko tsangwama da kiyayya daga wajen Al'umma ba.

Naku:- Moh'd Alkasim

28/10/2025

Shin me ke faruwa ne tsakanin Hukumar BAROTA da Al'umma kofar Ran dake Jihar Bauchi.

27/10/2025

Rikicin Kadija Mai Nunfashi da Kabiru Legas

Ana matsa min lamba na shiga APC - Gwamnan Plateau, MutfwangGwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa yana s...
27/10/2025

Ana matsa min lamba na shiga APC - Gwamnan Plateau, Mutfwang

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa yana shan matsin lamba daga wasu jiga-jigan siyasa don ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC.

Ya bayyana hakan ne a wani taron da aka gudanar a gidan gwamnati, Jos, inda ya ce Allah da jama’ar da s**a zaɓe shi ne kaɗai za su iya yanke masa hukuncin sauya jam’iyya.

“Sun matsa min lamba, amma na gaya musu cewa sai Allah da ku jama’a ne za su bani izini,” in ji shi.

Ya tambayi jama’a ko sun umarce shi da sauya jam’iyya, inda s**a amsa da ƙarfi da cewa “A’a.”

Wannan furuci na Mutfwang ya biyo bayan rahotannin da s**a ce APC a Filato na ƙoƙarin jawo shi zuwa jam’iyyarsu, lamarin da jiga-jigan APC s**a yi watsi da shi.

Gwamnan ya ce waɗanda ke adawa da jita-jitar sauya shekar tasa suna yin hakan ne saboda tsoro, yana mai cewa da yawancin ‘yan APC a Filato za su yi farin cikin ganin ya shiga jam’iyyarsu.

Tun bayan zaɓen 2023, PDP ta rasa gwamnoni uku zuwa APC, yayin da wasu gwamnoni a Taraba, Zamfara da Osun ke zargin suna shirin komawa jam’iyyar mai mulki.

Da dumi'dumi: Tsohon Ministan Ayyuka na Musamman, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya mika fom ɗinsa na neman zama Shugaban j...
27/10/2025

Da dumi'dumi: Tsohon Ministan Ayyuka na Musamman, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya mika fom ɗinsa na neman zama Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa a hedkwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Amma kuma tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, bai samu damar sayen fom ɗinsa ba bayan ya ce babu jami’an da ke sayar da fom din a ofishin jam’iyyar.

Lamido ya yi barazanar kai ƙarar kotu idan har aka hana shi shiga takara.

DA DUMI-DUMI:Sule Lamido Zai Maka Jam’iyyar PDP a KotuTsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa z...
27/10/2025

DA DUMI-DUMI:Sule Lamido Zai Maka Jam’iyyar PDP a Kotu

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa zai kai jam’iyyar PDP kotu bayan an ƙi sayar masa da fom ɗin takarar shugabancin jam’iyyar. Lamido, wanda ya isa hedikwatar PDP da ke Abuja a safiyar Litinin don karɓar fom ɗin takara, ya ce an hana shi ba tare da wani dalili mai tushe ba.

Ya bayyana wannan mataki a matsayin rashin adalci da tauye hakkinsa a cikin jam’iyyar, yana mai cewa zai bi ta kotu don neman adalci da tabbatar da gudanar da zaben shugabanni cikin gaskiya da tsari.

Lamido ya jaddada cewa yana nan daram a PDP, tare da fatan ganin jam’iyyar ta farfaɗo da ƙarfinta kafin babban zaben 2027.

An nada Birgediya Janar Marcus Kokko mai ritaya a matsayin Basaraken kabilar Sayawa.
27/10/2025

An nada Birgediya Janar Marcus Kokko mai ritaya a matsayin Basaraken kabilar Sayawa.

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ASU Media TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ASU Media TV:

Share