ASU Media TV

ASU Media TV ASU Media TV Online. 09037484655
(2)

ASU MEDIA Gidan Jaridace ta Mai Zamanka wacce aka Samar da ita Dan isar da sakonni tareda fitar da sahihan labarai, Da kuma tallace-tallace wa kamfanoni da sauransu.

Siyasar Najeriya cike take da mayaudara da masu cin Amana — JonathanTsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bayyana ...
05/09/2025

Siyasar Najeriya cike take da mayaudara da masu cin Amana — Jonathan

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bayyana siyasar Najeriya a matsayin mai cike da masu cin amana da kuma masu yaudara.

“A Najeriya da wuya ka ga mutum ɗaya ya faɗi abu ɗaya da safe ya kuma tsaya a kai da yamma,” in ji shi a jiya.

Jonathan ya yi wannan jawabi ne a wurin bikin cika shekara 70 na tsohon Shugaban Ma’aikatansa, Cif Mike Ogiadomhe, a Benin, babban birnin Jihar Edo.

Ya bambanta Ogiadomhe, wanda ya taɓa zama mataimakin gwamnan Jihar Edo, a matsayin mutum mai dogaro da sahihancin magana, inda ya ce: “Na sha ganin masu cin amana, musamman a zaɓen 2015 (inda na sha kaye hannun marigayi Shugaba Muhammadu Buhari), amma Mike mutum ne da zai iya tsayawa ko da za a yi masa duka saboda ni.

“Maganarsa maganar gaskiya ce da za ka iya kaiwa banki. Amma yawancin ’yan siyasa ba haka suke ba. Za su gaya maka abu ɗaya yanzu, cikin awa guda ka ga sun sauya magana.”

A ’yan kwanakin nan, shugabannin PDP da dama sun rika kira ga tsohon shugaban ƙasar da ya tsaya takara a 2027.

Cikin waɗanda ke kiran Jonathan ya tsaya takarar neman tikitin PDP akwai tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, tsohon Ministan Yaɗa Labarai, Farfesa Jerry Gana, da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed.

Sai dai Jonathan bai ce komai kan kiran ba, duk da cewa a watan Mayu uwargidansa, Patience Jonathan, ta bayyana cewa mijinta zai goyi bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ta ce ya taimaka wa Jonathan wajen samun nasara a zaɓen 2011.

RARARA ZAI AURAR DA YARANSA 10Wannan sune jerin angwaye da Amare wayanda Mawaki Dauda Kahutu Rarara zai ɗaurawa aure ran...
05/09/2025

RARARA ZAI AURAR DA YARANSA 10

Wannan sune jerin angwaye da Amare wayanda Mawaki Dauda Kahutu Rarara zai ɗaurawa aure ranar 26/09/25

Nan da kwana 21 insha Allahu za'ayi wannan kataparen biki a jahar kano.

Rarara shine wanda ya ɗauki nauyin duk wani abu da ya shafi wannan biki, tun daga ɓangaren angwaye harda amaren su.

A yau 04-09-2025 Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Muhammad Abdullahi Abubakar SAN ya halarci Taron Muslim Lawyers Association...
04/09/2025

A yau 04-09-2025 Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Muhammad Abdullahi Abubakar SAN ya halarci Taron Muslim Lawyers Association Of Nigeria (MULAN) wanda suke gudanar wa a duk wata a Babban birinin tarayya Abuja .

HOTUNA: Gwamnan jihar Katsina, Umar Dikko Radda, ya jagoranci tawogar manyan jihar zuwa wajen shugaban ƙasa don kai koke...
03/09/2025

HOTUNA: Gwamnan jihar Katsina, Umar Dikko Radda, ya jagoranci tawogar manyan jihar zuwa wajen shugaban ƙasa don kai koke kan rashin tsaro da ya addabi jihar.

03/09/2025

Tareda Sadiq Abdullahi kobi Benzima daya daga cikin matasa yan Gwagwarmayan siyasa a Jihar Bauchi.
Acikin Shirinmu na FAGEN SIYASA.

Duk irin tallan Gwamnan Yobe da Malam Nata'ala yayi da ƙyar ya tura masa miliyan 2, mutumin da rubutu ya kamata yayi kaw...
03/09/2025

Duk irin tallan Gwamnan Yobe da Malam Nata'ala yayi da ƙyar ya tura masa miliyan 2, mutumin da rubutu ya kamata yayi kawai don daukar nauyin rashin lafiyar sa saboda irin tallan da yayi masa amma ya gaza.

Dan haka Abinda Tciani ya yiwa Malam Nata'ala ba zamu taba mantawa ba Allah ya saka masa da alkairi.

A yayin da wadanda Malam Nata'ala ya tallata a harkar siyasa s**a watsar dashi sai wani daga waje ne zai tsallako ya taimake mu.

~ Cewar Umar Baana

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Juma'a 5 Ga Watan Satumba A Matsayin Ranar Hutu, Domin Bikin Maulidi Na Tunawa Da Haihuwar A...
03/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Juma'a 5 Ga Watan Satumba A Matsayin Ranar Hutu, Domin Bikin Maulidi Na Tunawa Da Haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W)

Yadda Jama'ar Gari Suke Rububiñ Yin Hotuna Da Tubabbùñ 'Ý@ñ B1nd1g@, Bayan An Yi Sulhu Da Su A Yankin Kankara Dake Katsi...
02/09/2025

Yadda Jama'ar Gari Suke Rububiñ Yin Hotuna Da Tubabbùñ 'Ý@ñ B1nd1g@, Bayan An Yi Sulhu Da Su A Yankin Kankara Dake Katsina

Me za ku ce?

Zargin 'Anti Party' a cikin jam'iyya bai zamo dalilin da za a hukunta Wike ba in ji PDPJam’iyyar PDP mai adawa a Nijeriy...
02/09/2025

Zargin 'Anti Party' a cikin jam'iyya bai zamo dalilin da za a hukunta Wike ba in ji PDP

Jam’iyyar PDP mai adawa a Nijeriya ta bayyana cewa, ba za a iya daukar matakin ladabtarwa a kan tsohon Gwamnan Jihar Rivers kuma Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, bisa zargin yin aikin cin amanar jam’iyya ba sai an gabatar da ƙorafi a hukumance tare da shaidu masu tabbatar da hakan.

DA ƊUMI-ƊUMI: Tsohon Ministan Shari'a  Abubakar Malami ya tsallakē rijiyã da bayaTsohon Ministan Shari'a, kuma jagoran J...
01/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Tsohon Ministan Shari'a Abubakar Malami ya tsallakē rijiyã da baya

Tsohon Ministan Shari'a, kuma jagoran Jam'iyyar haɗaka ta ADC da tawagarsa sun tsallake rijiya da baya, bayan wasu ɓata gari sun farmake su da duwatsu, ya yin dawowa daga Ta'aziyya a cikin birnin Kebbi.

Lamarin ya faru a yau Litinin, ya yin da shi da tawagarsa suke kan hanyar dawowa daga Ta'aziyya a cikin birnin Kebbi.

Kotu a Finland ta yanke wa jagoran Biafara Simon Ekpa hukuncin shekara 6 a gidan yari Kotu ta Päijät-Häme da ke Finland ...
01/09/2025

Kotu a Finland ta yanke wa jagoran Biafara Simon Ekpa hukuncin shekara 6 a gidan yari

Kotu ta Päijät-Häme da ke Finland ta yanke wa Simon Ekpa, mai rajin kafa ƙasar Biyafara, hukuncin shekara shida a gidan yari kan laifukan ta’addanci.

Kotun ta same shi da laifin tayar da zaune-tsaye da kuma shiga cikin ayyukan ƙungiyar ta’addanci.

A cewar jaridar YLE ta Finland, kotun ta bayyana cewa Ekpa ya yi amfani da “yawan mabiyan da yake da su a kafafen sada zumunta” wajen hura tarzoma a yankin kudu maso gabashin Najeriya tsakanin watan Agustan 2021 da Nuwamban 2024.

Kotun ta kuma gano cewa Ekpa babban jigo ne a wata ƙungiyar ‘yan a ware masu ɗaukar makami, wadda burinta shi ne raba Najeriya don kafa ƙasar Biyafara.

Haka kuma kotun ta tabbatar da cewa Ekpa ya samar wa wasu ƙungiyoyi makamai, bama-bamai da harsasai “ta hanyar sadarwa da yake da ita a yankin”, sannan an kuma same shi da laifin ƙarfafa mabiyansa a dandalin sada zumunta na X da su aikata laifuka a Najeriya.

Duk Dàn Arewa Mai Hàñķali Ba Zai Zabì Tinùbù Ba A Zaben 2027, Cewar Sule Lamido.
01/09/2025

Duk Dàn Arewa Mai Hàñķali Ba Zai Zabì Tinùbù Ba A Zaben 2027, Cewar Sule Lamido.

Address

Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ASU Media TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ASU Media TV:

Share