Bakandamiya News

Bakandamiya News Bakandamiya News
Stay with us to get latest news and updatas.
(1)

Sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Abia yace zai sanya jihar ta zama wuri mara daɗi ga masu aikata laifuka.Sabon Kwamis...
11/08/2026

Sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Abia yace zai sanya jihar ta zama wuri mara daɗi ga masu aikata laifuka.

Sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Abia, CP Wilfred Afolabi, ya bayyana cewa jihar ba za ta zama mafakar masu aikata laifuka ba.

Ya kuma yi alƙawarin gudanar da rundunar ’yan sanda mai gaskiya, ƙwarewa da kuma amfani da bayanan sirri wajen yanke shawara, tare da mayar da hankali kan kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Afolabi ya bayyana hakan ne a ranar Talata, a lokacin taronsa na farko da manyan jami’an rundunar ’yan sandan jihar.




Ya gargadi jami’an kan karɓar kuɗaɗen na goro daga mutane, tare da yin alƙawarin cewa zai sanya jihar Abia ta zama wuri mara daɗi ga masu aikata laifuka.

Da yake jawabi ga jami’an, Kwamishinan ’Yan Sandan ya ce ya zo Abia ne da manufa guda ɗaya, yin hidima cikin gaskiya da riƙon amana, aiwatar da doka ba tare da tsoro ko nuna wariya ba, da kuma kare rayuka da dukiyoyin kowane mazaunin jihar.

11/08/2026

Labaran Dare 11 ga watan Augusta, 2026

Mai Karantawa Halima Dahiru

Olusegun Obasanjo, ya soki tsarin dimokuraɗiyyar da ake amfani da shi a yawancin ƙasashen Afirka.Tsohon Shugaban Ƙasa, O...
11/08/2026

Olusegun Obasanjo, ya soki tsarin dimokuraɗiyyar da ake amfani da shi a yawancin ƙasashen Afirka.

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya soki tsarin dimokuraɗiyyar da ake amfani da shi a yawancin ƙasashen Afirka, yana mai cewa an aro tsarin ne daga ƙasashen Yamma, kuma hakan ya haifar da al’adar siyasar “wanda ya ci ya kwashe komai”.

Obasanjo ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin taron tattaunawa kan dimokuraɗiyya na gidauniyar Goodluck Jonathan ta shekarar 2026, wanda aka gudanar babban birnin Jihar Bauchi.

Ya ce dimokuraɗiyyar sassaucin ra’ayi ta Yamma da ƙasashen Afirka da dama s**a gada, ba a tsara ta ne bisa la’akari da yanayin da Afirka take ciki ba.

Ya kwatanta yadda aka rungumi wannan tsarin da mutum ya sanya rigar da ba a ɗinka ta daidai gwargwadon jikinsa ba.

11/08/2026

Shirin Ya Mace

Tareda Ikilima Abubakar

Ɗan majalisar dokokin Jihar Kano mai wakiltar ƙaramar hukumar Tudun Wada, ya fice daga APC zuwa PDP.Kakakin majalisar do...
11/08/2026

Ɗan majalisar dokokin Jihar Kano mai wakiltar ƙaramar hukumar Tudun Wada, ya fice daga APC zuwa PDP.

Kakakin majalisar dokokin Kano, Ismail Falgore, ne ya karanta wasiƙar murabus ɗin Shuwaki a zaman majalisar na ranar Litinin.
A cikin wasiƙar, Shuwaki ya ce ya yanke shawarar barin APC ne bayan “nazari mai zurfi da shawarwari” da ya gudanar da abokan siyasarsa, magoya bayansa da iyalansa.

Ya kuma gode wa shugabannin APC daga matakin mazaba zuwa na ƙasa kan damar da s**a ba shi da goyon bayan da ya samu a lokacin da yake cikin jam’iyyar.

Sai dai ya ce ya zaɓi wata sabuwar hanyar siyasa da ta dace da ƙa’idoji da ra’ayinsa.

Bayan karanta wasiƙar, Kakakin majalisar ya tambayi Shuwaki ko shi da kansa ne ya gabatar da wasiƙar, inda ɗan majalisar ya tabbatar da hakan tare da bayyana cewa ya koma PDP tun watanni da s**a gabata, sai dai shawarwari na siyasa s**a jinkirta sanar da hakan a hukumance.

NURPC ta gargaɗi masu neman aiki da su Guji shiga hannun 'yan damfara.Hukumar kula da harkokin man fetur na sama, NUPRC,...
11/08/2026

NURPC ta gargaɗi masu neman aiki da su Guji shiga hannun 'yan damfara.

Hukumar kula da harkokin man fetur na sama, NUPRC, ta gargadi masu neman aiki da sauran jama’a kan wasu ‘yan damfara da ke yawo da takardun daukar aiki na bogi, tare da karbar kudi da sunan samun aiki a hukumar.

Hukumar ta ce a halin yanzu ba ta gudanar da wani shirin daukar ma’aikata.

Hukumar ta ce wasu masu damfara na yawo da takardun daukar aiki na bogi a kafafen sada zumunta, inda suke neman kudi daga masu neman aiki da sunan za su taimaka musu wajen samun gurbin aiki a hukumar.

NUPRC ta bayyana cewa wasu daga cikin takardun daukar aikin da ake yadawa a kafafen sada zumunta na bogi ne, yayin da wasu kuma aka samar da su ta hanyar fasahar Artificial Intelligence, AI.

Hukumar ta bukaci jama’a da su yi taka-tsantsan, kada su biya wani kudi ko ba da bayanan sirri ga mutanen da ke ikirarin cewa za su samar musu da aiki a NUPRC.

Ta kuma shawarci masu neman aiki da su dogara da sahihan kafafen hukumar domin samun bayanan da s**a shafi daukar ma’aikata, tare da yin watsi da duk wata takardar aiki da ba ta da ingantacciyar shaida.


BAI KAMATA RIKICIN TURAI YA SHAFI FARASHIN MAN FETUR A AFIRKA BA.Gwamnatin Tarayya ta ce rikice-rikicen da ke faruwa a T...
11/08/2026

BAI KAMATA RIKICIN TURAI YA SHAFI FARASHIN MAN FETUR A AFIRKA BA.

Gwamnatin Tarayya ta ce rikice-rikicen da ke faruwa a Turai da yankin Bahar Rum bai k**ata su zama abin da ke kayyade farashin man fetur a nahiyar Afirka ba.

Gwamnatin ta ce ya k**ata kasashen yammacin Afirka su samar da wani tsarin farashi na bai ɗaya da zai fi dacewa da yanayin kasuwarsu.

Gwamnatin Tarayya ta Najeriya ta bayyana cewa rikice-rikicen siyasa da tsaro da ke faruwa a Turai da yankin Bahar Rum bai k**ata su rika yin tasiri kai tsaye wajen kayyade farashin man fetur a nahiyar Afirka ba.

Gwamnatin ta ce dogaro da farashin da ake amfani da shi a wasu kasuwannin duniya na iya jefa kasashen Afirka cikin matsalar farashin mak**ashi da ba ya la’akari da yanayin kasuwarsu.

Saboda haka, Najeriya na kokarin ganin an samar da wani benchmark na farashin man fetur na yankin Yammacin Afirka, wanda zai yi la’akari da bukatun kasashe da kuma yanayin kasuwar yankin.

Gwamnatin ta yi nuni da cewa samar da irin wannan tsarin zai taimaka wajen tabbatar da ingantaccen farashi da rage tasirin rikice-rikicen da ke faruwa a wasu sassan duniya kan kasuwar man fetur ta Afirka.

Bakandamiya News

DSS Ta Amince Da Kuskuren K**a Mustapha Marwa, Ta Ba Shi Haƙuri.Hukumar ta ce bincikenta ya tabbatar da cewa matashin ba...
11/08/2026

DSS Ta Amince Da Kuskuren K**a Mustapha Marwa, Ta Ba Shi Haƙuri.

Hukumar ta ce bincikenta ya tabbatar da cewa matashin ba shi da hannu a ayyukan da ake zarginsa da su.

Hukumar Tsaro ta Fararen Kaya ta Najeriya, DSS, ta amince da cewa an yi kuskure wajen k**a da tsare Mustapha Marwa bisa zargin kasancewa cikin wata ƙungiyar da ke da alaƙa da ayyukan ta’addanci.

A cewar hukumar, cikakken bincike da ta gudanar ya tabbatar da cewa Mustapha Marwa ba shi da wata alaƙa da ƙungiyar Ansaru da ake zargi da hannu wajen sace ɗalibai 46 a wani hari da ya faru a baya.

DSS ta bayyana cewa bayan gano kuskuren, ta nemi afuwar Mustapha Marwa tare da ɗaukar matakan gyara domin kauce wa irin wannan kuskure a nan gaba.

Hukumar ta kuma ce kuɗin da aka ba shi ba diyya ba ne ta fuskar shari’a, sai dai wani tallafi ne da aka bayar domin taimaka masa wajen sake daidaita rayuwarsa bayan lokacin da ya shafe a tsare.

DSS ta jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta cikin kwarewa da bin doka, tare da tabbatar da kare haƙƙin jama’a yayin yaƙi da ta’addanci da sauran barazanar tsaro a ƙasar.

Bakandamiya News

Tsohon Gwamnan Adamawa Bindow Ya Gana Da Tinubu Bayan Ficewarsa Daga ADC.Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa, Umar Jibrilla Bin...
11/08/2026

Tsohon Gwamnan Adamawa Bindow Ya Gana Da Tinubu Bayan Ficewarsa Daga ADC.

Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa, Umar Jibrilla Bindow, ya gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, bayan ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar African ADC.

Majiyoyi sun bayyana cewa ganawar ta gudana ne a daren ranar Litinin a Presidential Villa da ke Abuja.

Sai dai har yanzu ba a bayyana cikakken abin da aka tattauna a yayin ganawar ba.

Ganawar ta zo ne jim kaɗan bayan Bindow ya fice daga jam’iyyar ADC, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce kan matakin siyasar da tsohon gwamnan zai ɗauka a gaba.

Bindow ya kasance gwamnan Adamawa daga shekarar 2015 zuwa 2019, kuma ya sake shiga harkokin siyasa a wani lokaci da jam’iyyu ke ƙara shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen 2027.

Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa a hukumance daga fadar shugaban ƙasa ko daga bangaren Bindow da ta bayyana dalilin ganawar ko abin da aka cimma a yayin tattaunawar.

Bakandamiya News

11/08/2026

LIVE NOW:

SIR AHMADU BELLO INTERNATIONAL CONFERENCE CENTER, BAUCHI

VOTE OF THANKS / CLOSING REMARKS BY H.E. DR. GOODLUCK EBELE JONATHAN, GCFR, GCON
Chairman/Founder, Goodluck Jonathan Foundation

Gov. Sen. Senator Bala Abdulkadir Mohammed (KAURAN BAUCHI) hosted the 2026 GJF DEMOCRACY DIALOGUE.

Theme:"BEYOND ELECTIONS: CAN POLITICAL PARTIES AND THE JUDICIARY SAVE AFRICAN DEMOCRACY"

Join the conversation live on Bakandamiya News | Kauran Bauchi Media TV

Address

Bauchi
740271

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bakandamiya News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share