31/07/2026
Matashi Daga Bauchi Ya Nemi Goyon Bayan Manyan Jihar Domin Cika Burinsa Na Zama Ɗan Sanda
Wani matashi ɗan asalin Jihar Bauchi mai suna Muhammad Haruna ya yi kira ga manyan shugabanni da masu ruwa da tsaki a jihar da su tallafa masa wajen cika burinsa na zama jami'in rundunar 'yan sandan Najeriya.
Muhammad Haruna ya bayyana cewa ya sha ƙoƙarin neman aikin 'yan sanda sau da dama, amma har yanzu bai samu nasarar shiga aikin ba. Ya ce hakan ne ya sa ya yanke shawarar neman taimako da goyon bayan shugabannin jihar, yana mai fatan za su taimaka masa ta kowace hanya da ta dace.
Daga cikin waɗanda ya yi kira gare su akwai Mai Girma Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Bauchi), Mai Martaba Sarkin Bauchi Alhaji Dr. Rilwanu Suleimanu Adamu, Sanata Shehu Buba Umar, Barrister Mohammed Abdullahi Abubakar (Makama Babba), Dr. Bala Wunti, Dr. Yakubu Adamu, PhD, Ministan Lafiya na Tarayyar Najeriya Dr. Muhammad Ali Pate, Sanata Halliru Dauda Jika, Dokajin Bauchi, da kuma Alhaji Mahidu Mu'azu Abubakar (Sarkin Doka).
Ya ce burinsa shi ne ya samu damar yi wa ƙasa hidima a matsayin jami'in 'yan sanda, tare da bayar da gudummawarsa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron al'umma.
A ƙarshe, Muhammad Haruna ya yi addu'ar Allah Ya saka wa duk wanda ya taimaka masa da alheri, yana mai fatan shugabannin da ya yi kira gare su za su dubi buƙatarsa cikin tausayi da kulawa.