Bauchi Daily Post

  • Home
  • Bauchi Daily Post

Bauchi Daily Post Jarida ce da za ta riƙa kawo muku labaran jihar Bauchi da kewaye daga 5STARS MEDIA PRODUCTION.
(1)

YANZU-YANZU: Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Iran ya sanar da cewa martanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan hare-haren ...
27/11/2024

YANZU-YANZU: Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Iran ya sanar da cewa martanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan hare-haren baya-bayan nan na Isra'ila zai wuce tunanin gwamnatin Isra'il@.

Iran ba za ta taba lamuntar keta huruminta ba, in ji Manjo Janar Mohammad Baqeri yayin wani taro da manyan kwamandojin sojoji da ya gudana a birnin Tehran a ranar Talata.

A cikin jawaban nasa, Janar Baqeri ya bayyana cewa gwamnatin Isra'il@ tana cikin matukar rudani a wannan lokaci a Gaza da kudancin Lebanon.

Jaridar Arewa

DA ƊUMI-ƊUMI: “Addini na ya hana hakan” Khadijah taƙi amincewa da musafaha da shugaban bankin UBASunanta Khadijah Abdulh...
24/11/2024

DA ƊUMI-ƊUMI: “Addini na ya hana hakan” Khadijah taƙi amincewa da musafaha da shugaban bankin UBA

Sunanta Khadijah Abdulhamid, Husna daga makarantar Sakandaren Sweet Haven ta Jihar Kano, ta ki amincewa da musafaha da Oliver Alawuba, Shugaban Kamfanin UBA, a wajen gabatar da lambar yabo ta UBA Foundation Nigeria, inda ta ce Addininta ya hana hakan.

Daga Usman Umar Katsina

Gwamnan jihar Jigawa ya jagoranci jana'izar mutane sama da 100 da s**a kone sanadiyar tankan Fetur jiya da dare a garin ...
16/10/2024

Gwamnan jihar Jigawa ya jagoranci jana'izar mutane sama da 100 da s**a kone sanadiyar tankan Fetur jiya da dare a garin Majia jihar Jigawa.

Inda aka tona babban kabari aka saka duka gawarwacin ciki. Muna Addu'ar Allah ya jikansu ya yafe musu kura kuransu, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani.

KAJI RABO: An Naɗa Umar Bush Sarautar "Lakakan Zazzau"Wane fata zaku yi masa?
04/10/2024

KAJI RABO: An Naɗa Umar Bush Sarautar "Lakakan Zazzau"

Wane fata zaku yi masa?

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Sanata Buba ya caccaki Gwamnan Bauchi Bala Mohammed kan zargin fashi da makamiSanata Buba ya caccaki Gw...
04/10/2024

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Sanata Buba ya caccaki Gwamnan Bauchi Bala Mohammed kan zargin fashi da makami

Sanata Buba ya caccaki Gwamnan Bauchi Bala Mohammed kan zargin fashi da makami Yana cewa Zargi maras tushe, mara tushe, kage

Sanata mai wakiltan Bauchi ta Kudu Sanata Shehu Umar Buba, ya bayyana a matsayin mara tushe, kage da kuma zage-zage, zargin da Gwamnan Jihar Bauchi Sen Bala Mohammed Abdulkadir ya yi na cewa yana goyon baya da daukar nauyin ayyukan ‘yan fashi.

Ku tuna cewa Gwamnan ya a wata wasika da ya aike wa Shugaban kasa, Sen Bola Ahmed Tinubu mai kwanan wata 19 ga Satumba, 2024, ya yi zargin cewa Sanatan na daya daga cikin masu goyon bayan ‘yan fashi da makami a kasar nan, inda ya bukaci a k**a shi, a gudanar da bincike tare da gurfanar da shi a gaban kuliya.

Sanatan wanda shi ne Shugaban Kwamitin Tsaro da Leken Asiri na Majalisar Dattawa ya tabbatar da cewa ba zai ji tsoro da irin wadannan ikirari da ba su da tushe b***e mak**a.

A wata sanarwa da mai taimaka masa na majalisar, Hassan Gajin Duguri ya fitar a ranar Alhamis, Sanata Shehu Buba ya bayyana koke-koken da Gwamnan ya kai wa Shugaba Tinubu a matsayin abin dariya ne kuma abin takaici ne.

Sanatan ya bayyana cewa da ba zai mayar da martani ga wannan zargi maras tushe ba amma ya ga ya zama dole a daidaita batun domin a karyata labarin.

Ya caccaki Gwamna Mohammed kan yadda yake ci gaba da zagi da cin mutuncin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a yayin da yake tunzura ‘yan kasa kan gwamnatin tarayya, yana mai tambayar ta yaya zai kuskura ya mika koke ga dan majalisar da ke mayar da martani ga hargitsin da ya yi maras tushe.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, A matsayinsa na Sanata mai wakiltan Bauchi ta Kudu a Majalisar Dokoki ta kasa, Sanata Buba ya jure wa Gwamna Bala Mohammed girman kai, wuce gona da iri, da dabi’un da ba su dace ba, wadanda s**a hada da kage-kage marasa tushe da s**a samo asali daga yadda Sanatan ke kare Shugaban kasa kan wasu kalamai na batanci.

Jagoran Addinin Musulunci a Iran Ayatollah Ali Khamenei zai jagoranci sallar Juma'a a masallacin Imam khomeini dake birn...
04/10/2024

Jagoran Addinin Musulunci a Iran Ayatollah Ali Khamenei zai jagoranci sallar Juma'a a masallacin Imam khomeini dake birnin Tehran.

Ayatollah Khamenei ya shafe shekaru huɗu bai jagoranci sallar Juma'a ba tun shekarar 2020, bayan martanin Iran kan Isra'ila bisa kisan babban jami'in juyin juya halin Iran Qasem Soleimani.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran ta daura damarar yaki da Isra'ila, da kuma kare kanta daga hare-haren ramuwar gayya da Isr̃à'ilàr ta ce za ta kai a lokacin da ya dace.

01/10/2024
YANZU-YANZU: Hukumar Sojin ruwa ta Najeriya ta sanar da korar Abbas daga aiki a hukumance.
27/09/2024

YANZU-YANZU: Hukumar Sojin ruwa ta Najeriya ta sanar da korar Abbas daga aiki a hukumance.

DA DUMI-DUMI: Abdul Samad Rabi’u Ya bada Naira Biliyan 1 Da  ayan abinci na kimanin Biliyan 1 Ga wadanda ambaliyar ruwa ...
24/09/2024

DA DUMI-DUMI: Abdul Samad Rabi’u Ya bada Naira Biliyan 1 Da ayan abinci na kimanin Biliyan 1 Ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri.

Babban Daraktan Kamfanin na BUA Abdul Samad Rabi’u wanda Babban Daraktan Kungiyar Alhaji Kabir Rabiu ya wakilta ya kai ziyarar jajantawa tare da bayar da tallafin Naira Biliyan 1 da kuma Kayan Abinci na Naira Biliyan 1 ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar.

ABUN A YABA: Yadda dakarun jami'an tsaron Najeriya ke bawa manoma kariya suna kwashe amfanin gona a wasu sassan jihar Ka...
24/09/2024

ABUN A YABA: Yadda dakarun jami'an tsaron Najeriya ke bawa manoma kariya suna kwashe amfanin gona a wasu sassan jihar Katsina, sak**akon hare-haren ƴan bindiga.

Gwamnan Borno Babagana Zulum ya naɗa kwamitin mutum 35 domin fara raba tallafi ga wanda Ambaliyar Ruwa yayiwa ɓarna a ji...
23/09/2024

Gwamnan Borno Babagana Zulum ya naɗa kwamitin mutum 35 domin fara raba tallafi ga wanda Ambaliyar Ruwa yayiwa ɓarna a jihar.

Zulum ya bayyana cewar yanzu haka a kwai Naira Biliyan 4 da Miliyan 400 a cikin Asusun gwamnatin wanda jama'a s**a bayar da tallafi.

Gwamna ya ce gwamnatinsa zata maida hakan kan gyaran gine-gine da s**a rushe tare da gyara Asibitoci, Makarantu da hanyoyin da s**a lalace a Ambaliyar.

Hukumar Ƴan Sanda Ta Jihar Bauchi Tayi Nasarar Cafke Matashi Dauda Sa'idu Bisa Lalata Kabarin Mabiya Addinin Kirista Tar...
23/09/2024

Hukumar Ƴan Sanda Ta Jihar Bauchi Tayi Nasarar Cafke Matashi Dauda Sa'idu Bisa Lalata Kabarin Mabiya Addinin Kirista Tare Da Ɗebe Rodina A Cikin Garin Bauchi.

Matashin Ya Amsa Laifinsa Inda Yace Ya Saida Rodin Kan Kuɗi N12,000, Yayin Da Ya Yi Amfani Da Kuɗin Wajen Siyan Tabar Wiwi, Abinci Da Sauran su.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bauchi Daily Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bauchi Daily Post:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share