Bichi News

Bichi News Kafa mai kawo muku labarai, ayyuka, al’adu da ci gaban Ƙaramar Hukumar Bichi dake Jihar Kano a kowane lokaci. Ba wariya, ba bangaranci, ba banbanci.

Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya yafe mana kurakuranmu, Ya biya mana dukkan buƙatunmu na alheri, Ya tsare mu daga dukkan shar...
21/08/2026

Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya yafe mana kurakuranmu, Ya biya mana dukkan buƙatunmu na alheri, Ya tsare mu daga dukkan sharri, Ya ba mu lafiya da zaman lafiya.

Barkanmu da Juma’a!

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!Allah Ya yi wa Alhaji Ahmad Gadanya (Wamban Gadanya) rasuwa a yau Alhamis, 20 ga Agu...
20/08/2026

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un!

Allah Ya yi wa Alhaji Ahmad Gadanya (Wamban Gadanya) rasuwa a yau Alhamis, 20 ga Agusta, 2026, a ƙasar Masar (Egypt), bayan fama da rashin lafiya.

Marigayin ya kasance mahaifin Malam Bello Ahmad Gadanya, Comrade Jazuli Ahmad Gadanya, da sauran ’yan uwa da iyalansa.

Za a sanar da lokaci da wurin da za a gudanar da jana’izarsa nan gaba, da zarar mun samu cikakken bayani.

Muna miƙa saƙon ta’aziyya ga Malam Bello Ahmad Gadanya, Comrade Jazuli Ahmad Gadanya, ’yan uwa da abokan arziki bisa wannan babban rashi.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa, Ya kuma ba iyalansa da daukacin al’ummar Musulmi haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!Al’ummar Bichi sun girgiza da rasuwar matashi Sani Mansur (Alhaji), wanda Allah Ya yi...
20/08/2026

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!

Al’ummar Bichi sun girgiza da rasuwar matashi Sani Mansur (Alhaji), wanda Allah Ya yi wa rasuwa a yammacin yau Alhamis, 20 ga Agusta, 2026.

Tuni aka gudanar da jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, inda aka binne shi a Makarantar Bayan Tsohon Asibiti.

Marigayin ya kasance mutum ne mai kyakkyawar mu’amala, haƙuri, sauƙin kai da kyakkyawar zamantakewa da kowa. Ya kasance mutum mai mutunci da son zaman lafiya, wanda rasuwarsa ta girgiza al’ummar Bichi.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kurakuransa, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya bai wa iyalansa, ’yan uwansa, abokansa da daukacin al’ummar Bichi haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

Kwamitin Lafiya na Mai Girma Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bichi, ƙarƙashin jagorancin Dr. Yusuf Mohammed Sabo, tar...
20/08/2026

Kwamitin Lafiya na Mai Girma Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bichi, ƙarƙashin jagorancin Dr. Yusuf Mohammed Sabo, tare da Hukumar Asibitin Bichi da Daraktan Shiyya na Bichi, sun cimma matsaya kan sake buɗe ƙofar baya ta Babban Asibitin Bichi.

Bichi News ta rawaito cewa an cimma matsayar ne a yau, Alhamis 20 ga Agusta, 2026, bayan wani zama na musamman da ɓangarorin s**a gudanar domin tattauna batun rufe ƙofar bayan asibitin.

Hakan ya biyo bayan sanarwar da Hukumar Asibitin Bichi ta bayar a jiya, Laraba, inda ta ba da umarnin rufe ƙofar bayan asibitin har abada, lamarin da ya jefa wasu daga cikin al’ummar yankin cikin damuwa da rudani.

A yayin zaman, an cimma matsayar cewa za a sake buɗe ƙofar bayan asibitin nan take, sai dai bisa yarjejeniyar cewa za ta kasance a buɗe ne daga ƙarfe 8:00 na safe zuwa ƙarfe 8:00 na dare.

Haka kuma, an yi kira ga al’umma da su sanya ido tare da bayar da gudunmawa wajen tabbatar da cewa ba a ci gaba da aikata laifuka ko wasu munanan abubuwa ta wannan ƙofa ba.

Daraktan Shiyya na Bichi ya yabawa Kwamitin Lafiya bisa shiga tsakani da ƙoƙarin da ya yi wajen ganin an warware matsalar, tare da addu’ar Allah Ya ƙara haɗa kan dukkan waɗanda abin ya shafa.

Rahoto:
Kamalu Ibrahim Namowa
Abdullahi Sada Abdullahi

Ya kai matashi, kada ka bari dogon buri, ganin ka yi karatu mai zurfi, kunyar mutane, ganin kanka kamar wani, ko kuma so...
20/08/2026

Ya kai matashi, kada ka bari dogon buri, ganin ka yi karatu mai zurfi, kunyar mutane, ganin kanka kamar wani, ko kuma son yin budurwa, su hana ka gina rayuwarka.

Idan Allah Ya ba ka jari ko wata dama, ka yi amfani da ita wajen gina makomarka.

Ka sani, ba kunya ba ce ka fara da ƙaramar sana’a. Babbar kunya ita ce mutum ya zauna yana roƙon mutane su taimake shi, alhali yana da damar yin sana’ar da zai dogara da ita.

Ka riƙa tuna cewa Allah Ya umurci mutum da neman abin da zai dogara da shi. Duk abin da ka samu ta hanyar halal yana da albarka.

Ka yi aiki tukuru, ka dogara ga Allah, ka yi addu’a neman sa’a, sannan ka ɗauki matakin farawa. Ka yi haƙuri, kada ka bari sha’anin budurwa ya shagaltar da kai, ka guji almubazzaranci. In Sha Allah, za ka ga abin da za ka zama a nan gaba.

Ga wasu ƙananan sana’o’i 30 da matashi zai iya farawa da su:

1. Wankin mota
2. Gyaran waya
3. POS
4. Sayar da turare
5. Sayar da gwanjo
6. Sayar da takalma
7. Sayar da kayan miya
8. Sayar da man gyada ko man ja
9. Sayar da gurasa
10. Sayar da katin waya da data
11. Gyaran takalma
12. Sana’ar faci
13. Gyaran keke da babur
14. Kiwon zomaye
15. Kiwon kaji
16. Sayar da kifi
17. Sana’ar akomanci
18. Gasa ko dafaffen masara
19. Sayar da kayan lambu
20. Sayar da ƙwan kaji ko na zabi
21. Sayar da nama (Suya Meat)
22. Jogon kaji
23. Sayar da dafaffen abinci
24. Sayar da man fetur (bunburutu)
25. Sayar da ƙanƙara
26. Sayar da burodi
27. Sayar da kayan ƙamshi
28. Sayar da dabino
29. Sayar da dankalin Hausa ko na Turawa
30. Sayar da alawowi na yara

Ka tuna:

Sana’a ba ta da girma ko ƙanƙanta. Abin da ya fi muhimmanci shi ne ta kasance halal, ta ciyar da kai, kuma ta taimaka maka wajen gina makomarka.

Kada ka jira sai ka samu babban jari. Ka fara da abin da kake da shi. Ƙaramin farawa na iya zama babban nasara gobe.

Allah Ya azurta duk wani matashi da sana’ar halal, Ya sanya albarka a cikin abin da yake samu. Amin.

Malam Ibrahim.

Da'iratu Riyadur Rijalu Fi Madahin Nabiyi S.A.W na farin cikin gayyatar 'yan uwa da masoya ANNABI MUHAMMADU S.A.W zuwa b...
20/08/2026

Da'iratu Riyadur Rijalu Fi Madahin Nabiyi S.A.W na farin cikin gayyatar 'yan uwa da masoya ANNABI MUHAMMADU S.A.W zuwa babban Taron Ƙara wa Juna Sani (Seminar Karo na 4), wanda suke gabatarwa duk shekara.

RANA: Asabar, 9 Rabi'ul Auwal = 22/08/2026
LOKACI: 10:00 na safe
WURI: Twins Theatre, FCE Bichi

Sanarwa daga:
Chairman Riyadur Rijalu, Khalifa Abdulmajid Bichi

Domin ƙarin bayani:
📞 08162648995
📞 08030772040

Allah Ya ba da ikon halarta, Ya sa taron ya kasance mai albarka. Ameen.

GAIYYATAR ’YAN UWA ZUWA TARON MAULUDIN ANNABI S.A.WDA’IRATU YUNUSIYYA IBRAHIMIYYA ATTIJJANIYYATI – SABON GARI, BICHIA ma...
20/08/2026

GAIYYATAR ’YAN UWA ZUWA TARON MAULUDIN ANNABI S.A.W

DA’IRATU YUNUSIYYA IBRAHIMIYYA ATTIJJANIYYATI – SABON GARI, BICHI

A madadin shugabannin wannan Da’ira Mai Albarka, muna gayyatar ’yan uwa Musulmai, masoya Annabi Muhammad (S.A.W), zuwa wajen taron Mauludin Annabi (S.A.W) da wannan Da’ira ta saba gabatarwa duk shekara, wanda a wannan shekara zai kasance karo na 15.

Insha Allah, taron zai kasance kamar haka:

📅 Rana: Alhamis, 7/3/1448, 20/08/2026
⏰ Lokaci: 9:00 na dare zuwa wayewar gari
📍 Wuri: Kofar Gidan Marigayi Alh. Haruna (Gurgu), kusa da Mai Semon Vita Islamiyya, Sabon Gari, Bichi.

Allah Ya ba da ikon halarta. Amin.

Ƴar Najeriya, Maryam Ibrahim Dan Azumi, ta yi na ɗaya a gasar musabaƙar Alƙur’ani mai girma ta Hizb 60 tare da Tafsiri, ...
19/08/2026

Ƴar Najeriya, Maryam Ibrahim Dan Azumi, ta yi na ɗaya a gasar musabaƙar Alƙur’ani mai girma ta Hizb 60 tare da Tafsiri, inda ta yi fice wajen karatun Alƙur’ani da fahimtar ma’anoni da tafsirinsa.

A ban garan maza kuma Muhammad Abdullahi Marafa, ɗan Jihar Zamfara, ya samu matsayi na biyar.

Wannan gagarumar nasara ta ƙara ɗaukaka sunan Najeriya a fagen gasar Alƙur’ani, tare da nuna irin ƙoƙari da hazakar matasan ƙasar wajen haddace Littafin Allah da fahimtar saƙonsa.

Gasar ta bana ta samu halartar masu fafatawa daga ƙasashe 133 na duniya, yayi da Najeriya ta samu daraja a idon duniya.

Kungiyar Kwankwasiyya Bichi Kowa Namu ta Ƙaramar Hukumar Bichi ta gudanar da wani taro na musamman, inda ta sanar da sau...
19/08/2026

Kungiyar Kwankwasiyya Bichi Kowa Namu ta Ƙaramar Hukumar Bichi ta gudanar da wani taro na musamman, inda ta sanar da sauya sunan kungiyar zuwa APC Bichi Kowa Namu.

Taron ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Alhaji Habibu Idris Gwamnati, inda mambobin kungiyar s**a bayyana aniyarsu ta ci gaba da aiki tare da jam’iyyar APC tare da ba da gudunmawa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar a zaɓuka masu zuwa.

Kungiyar ta kuma jaddada ƙudurinta na haɗa kan mambobinta da ƙara ƙarfafa ayyukan jam’iyyar a Bichi.

Murnar Ranar Hoto ta DuniyaA yayin bikin Ranar Hoto ta Duniya, muna gabatar muku da wasu daga cikin hotunan da aka ɗauka...
19/08/2026

Murnar Ranar Hoto ta Duniya

A yayin bikin Ranar Hoto ta Duniya, muna gabatar muku da wasu daga cikin hotunan da aka ɗauka a Ƙaramar Hukumar Bichi.

Wane hoto ne ya fi birge ku a cikin waɗannan hotunan?

Masu ɗaukar hotunan: Ibrahim Kabir Abubakar, Ahmad Mario, VIP Photography, Daddy Photography.

Address

Bichi Local Government
Bichi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bichi News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bichi News:

Shortcuts

Share