TNU Hausa

TNU Hausa Domin samun labarai na gaskiya akan lokaci, ta hanyar zurfin bincike, Shirin salon rayuwa, dajin ra’ayoyin masu bibiyar mu. Whatsapp: 09060992687

Sanarwa, zaburarwa, tare da tattaunawa daku a kowace rana. General merchandise, online marketing and advertising, ICT services, SIM and NIN/BVN support, content creation and branding.

Sufeto-Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, ya ba da labarin wani lamari mai ban mamaki da ya faru a lokacin da ya...
22/08/2026

Sufeto-Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, ya ba da labarin wani lamari mai ban mamaki da ya faru a lokacin da yake matsayin DPO a Ago Iwoye, Jihar Ogun.

Disu ya ce wani tsohon soja ya taɓa zuwa ofishin ’yan sanda yana matsa musu lamba da su kashe ɗansa, wanda ɗalibin jami’a ne, bayan an k**a shi bisa zargin kasancewa cikin ƙungiyar asiri.

A cewarsa, mahaifin ya shafe kusan yini yana roƙon jami’an su kashe ɗan nasa, yana mai cewa ba ya son ya koma gida saboda abin da ya aikata.

Sai dai abin mamaki shi ne, washegari mahaifin ya sake komawa ofishin ’yan sandan, amma wannan karon ya zo ɗauke da abinci domin ya kai wa ɗansa da ake tsare da shi.

IGP Disu ya ce lamarin ya nuna irin yanayin da wasu iyaye kan tsinci kansu a ciki, inda fushi da takaici kan haɗu da ƙauna da kulawar da suke yi wa ’ya’yansu.

Ya bayyana wannan labari ne a Abuja yayin wani taron matasa mai taken National Youth Leadership and Security Dialogue, wanda Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta shirya.

Taron ya mayar da hankali ne kan rawar da matasa za su taka wajen shugabanci, inganta tsaro da kuma hana tashin hankali da daba.

Disu ya ƙara da cewa duk da matsalar da matashin ya fuskanta a lokacin, daga bisani ya kammala karatunsa, ya yi aure, sannan ya zama uba.

Ya ce labarin ya kasance darasi mai nuna cewa kuskuren da mutum ya aikata a wani lokaci bai k**ata ya zama ƙarshen rayuwarsa ba, musamman idan aka samu damar gyara da komawa kan turba.

Tsohon Gwamnan Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Rabiu Musa Kwankwaso, ya mi...
22/08/2026

Tsohon Gwamnan Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Rabiu Musa Kwankwaso, ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mutanen da s**a rasa rayukansu a wani hatsarin kwale-kwale a Gorau, ƙaramar hukumar Goronyo ta Jihar Sokoto.

Kwankwaso ya bayyana hatsarin a matsayin babban abin takaici, yana mai kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike domin gano ainihin abin da ya haddasa kifewar kwale-kwalen.

A cewar rundunar ’yan sandan Jihar Sokoto, mutane 77 ne ke cikin kwale-kwalen a lokacin da hatsarin ya faru. An ce fasinjojin sun haɗa da manoma da sauran mutanen da ke tafiya zuwa gonakinsu.

Rahotanni sun ce ya zuwa yanzu an gano gawarwaki 46, yayin da aka samu nasarar ceto mutane 15 da ransu. Haka kuma, ana ci gaba da aikin neman wasu 16 da har yanzu ba a san inda suke ba.

Kwankwaso ya yaba wa jami’an tsaro da masu aikin ceto, da kuma masu ruwa na yankin, bisa ƙoƙarin da suke yi wajen ceto waɗanda s**a tsira da kuma gano mutanen da s**a ɓace.

Ya kuma yi kira ga hukumomin gwamnati da su ɗauki ƙarin matakan kariya a hanyoyin ruwa, musamman wajen tabbatar da tsaron fasinjoji, domin kauce wa sake faruwar irin wannan mummunan lamari a nan gaba.

Ya ce ya k**ata a dauki darasi daga hatsarin tare da inganta matakan tsaro a harkokin sufuri ta ruwa.

Al’ummar wasu yankunan Karamar Hukumar Kebbe a Jihar Sakkwato sun koka matuƙa kan yadda hare-haren ’yan bindiga ke ƙara ...
22/08/2026

Al’ummar wasu yankunan Karamar Hukumar Kebbe a Jihar Sakkwato sun koka matuƙa kan yadda hare-haren ’yan bindiga ke ƙara tsananta, lamarin da ya tilasta dubban mutane barin gidajensu domin neman mafaka.

Mazauna yankin sun ce hare-haren da aka kai musu a baya-bayan nan sun yi sanadin mutuwar mutane da dama, tare da lalata gidaje da shaguna da kuma sace dabbobi masu yawa.

Wani mazaunin Kebbe, Ashiru Muhammad Sani Kebbe, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wasu mutane da s**a fita gonaki s**a dawo da gudu, suna gargadin cewa ’yan bindiga na kan hanyar shiga garin.

Ya ce maharan sun zo ne da dimbin babura, inda kowanne babur ke ɗauke da mutum uku.

A cewarsa, jami’an tsaro sun yi ƙoƙarin dakile harin, amma ’yan bindigar sun zagaye su, lamarin da ya yi sanadin mutuwar sojoji huɗu kafin sauran jami’an su ja da baya.

Ya ce bayan haka ’yan bindigar sun shiga wasu kauyuka, inda s**a kashe mutane, s**a sace dabbobi, tare da kwashe kayayyaki daga shaguna.

Ashiru ya ce yankunan Kaya, Barga, Unbutu, Aungushi da wasu kauyuka sun fuskanci mummunan hari, inda aka kashe mutane da dama a wasu wuraren, musamman Aungushi.

Ya ƙara da cewa hare-haren sun tilasta mazauna wasu kauyuka barin gidajensu, yayin da wasu gidaje da motoci da shaguna s**a kone.

A halin yanzu, wasu daga cikin waɗanda s**a tsere daga gidajensu na samun mafaka a garin Kebbe, yayin da wasu kuma s**a nufi Jihar Kebbi domin neman tsira.

Alhaji Sa’idu Atta Ungushi, tsohon kansilan mazabar Ungushi, ya ce wasu daga cikin mutanen garin sun koma Karamar Hukumar Jega ta Jihar Kebbi saboda kusancinta da yankinsu.

Ya bayyana takaicinsa kan abin da ya kira gazawar hukumomi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

“Me muka yi wa gwamnati har za ta kyale ana kashe mu? Muna neman gwamnati ta taimaka mana, ta samar mana da wurin zama da kuma abubuwan da za mu dogara da su,” in ji shi.

Tsohon kansilan ya ce hare-haren sun yi matuƙar illa ga rayuwar al’ummar yankin, inda aka kashe mutane, aka lalata gidaje da shaguna, sannan aka rasa dabbobi da sauran dukiyoyi.

Ya kuma ce mutane sama da 5,000 daga kauyuka daban-daban ne s**a tsere zuwa wuraren da suke ganin za su samu mafaka, ciki har da mutanen Ungushi, Mai Guda, Agwada, Birnin Malam, Nasara da Tingarge.

Mazauna yankin sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Sakkwato da su ƙara kaimi wajen kare al’umma tare da gaggauta tallafa wa waɗanda hare-haren s**a raba da gidajensu.

Sun ce matsalar rashin tsaro ta jefa su cikin mawuyacin hali, musamman ganin yadda s**a rasa gidaje da dukiyoyi, tare da kasa komawa gonakinsu domin gudanar da noma.

Premier League 2026/27Masoya kwallon kafa a duniya na shirin sake shiga cikin yanayin gasar Premier League ta Ingila, ya...
21/08/2026

Premier League 2026/27

Masoya kwallon kafa a duniya na shirin sake shiga cikin yanayin gasar Premier League ta Ingila, yayin da kakar 2026/2027 za ta fara a yau, Juma’a 21 ga Agusta 2026.

Wasan farko na kakar zai hada Arsenal da Coventry City a filin Emirates. Arsenal za ta fara kare kambunta na Premier League, yayin da Coventry City ta dawo gasar Premier League bayan shafe shekaru 25 ba tare da taka leda a matakin farko na Ingila ba.

Wannan kakar na zuwa ne da manyan sauye-sauye a kungiyoyi da dama. Manchester City za ta fara sabon zamani bayan tafiyar Pep Guardiola, yayin da Manchester United za ta kasance karkashin Michael Carrick. Liverpool kuma za ta fara sabon babi ba tare da Mohamed Salah ba, yayin da Chelsea ke karkashin sabon koci Xabi Alonso.

A wasan farko, Arsenal na neman fara kakar da nasara domin kare kambinta, amma za ta iya fuskantar kalubale saboda wasu manyan ‘yan wasanta suna da matsalar dacewa da wasa. Sabon dan wasanta Bruno Guimarães ma yana cikin wadanda ake tantama ko zai buga wasan saboda rauni.

Bayan wasan Arsenal da Coventry, sauran wasannin karshen makon farko za su hada da Hull City da Manchester United, Newcastle United da Liverpool, Brentford da Tottenham, da Bournemouth da Manchester City. Chelsea kuma za ta fara kakar ne a waje da Fulham ranar Litinin.

Sabuwar kakar Premier League na dauke da tambayoyi masu yawa: Shin Arsenal za ta iya kare kambinta? Shin Manchester City za ta iya samun nasara a sabon zamani? Shin Manchester United za ta ci gaba da farfadowa? Kuma Liverpool za ta iya yin takara ba tare da Salah ba?

A takaice, komai ya shirya domin wata sabuwar kakar Premier League mai cike da tarihi, gasa da kuma abubuwan mamaki.

Shin wa kuke ganin zai lashe gasar bana?

Allah Ya yi wa ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC a Jihar Kano, Alhaji Hamza Usman Darma, rasuwa.Wani ɗan gidan ma...
21/08/2026

Allah Ya yi wa ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC a Jihar Kano, Alhaji Hamza Usman Darma, rasuwa.

Wani ɗan gidan marigayin ne ya tabbatar da rasuwar tasa ga DAILY NIGERIAN HAUSA.

Rahotanni sun ce marigayin ya kasance ɗaya daga cikin fitattun masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar jam’iyyar APC a Kano.

Za a sanar da ƙarin bayani kan dalilin rasuwar da kuma lokacin da za a gudanar da jana’izarsa.

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ziyarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda ya gab...
21/08/2026

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ziyarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda ya gabatar masa da takardar shaidar nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar.

Adeleke ya isa fadar shugaban ƙasar da misalin ƙarfe 5:20 na yamma, inda ya zarce kai tsaye zuwa ofishin Shugaba Tinubu domin ganawar sirri.

Ziyarar ta zo ne kwanaki kaɗan bayan Adeleke ya sake lashe zaɓen gwamnan Osun da aka gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026, inda ya samu kuri’u 511,067, ya doke ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu kuri’u 444,815.

Bayan ganawar, Adeleke ya bayyana cewa ya je fadar shugaban ƙasar ne domin nuna godiyarsa ga Tinubu, musamman kan abin da ya bayyana a matsayin rawar da shugaban ya taka wajen tabbatar da gudanar da zaɓen cikin ’yanci da adalci.

Ya ce nasarar da ya samu ta nuna cewa idan aka bai wa jama’a damar bayyana ra’ayinsu cikin ’yanci, zaɓin al’umma zai iya yin tasiri.

Shugaba Tinubu ya taya Adeleke murnar nasarar tasa tun bayan bayyana sak**akon zaɓen, inda ya buƙace shi da ya haɗa kan al’ummar Osun tare da mayar da hankali wajen ci gaban jihar a wa’adin mulkinsa na gaba.

Fitaccen mai wallafa abubuwan yawon buɗe ido a kafafen sada zumunta, Traveltomtom, ya bayyana takaicinsa kan yadda aka h...
21/08/2026

Fitaccen mai wallafa abubuwan yawon buɗe ido a kafafen sada zumunta, Traveltomtom, ya bayyana takaicinsa kan yadda aka hana shi shiga Babban Cocin Ƙasa da ke Abuja, yayin da ya ce a Babban Masallacin Abuja an tarbe shi cikin fara’a duk da cewa shi Kirista ne.

Traveltomtom, wanda ya shahara wajen ziyartar ƙasashe daban-daban da kuma yada abubuwan da ya gani a kafafen sada zumunta, ya ce abin da ya faru a Abuja ya ba shi mamaki matuƙa.

Ya bayyana cewa lokacin da ya je Babban Cocin Ƙasa, ya samu matsala wajen shiga, inda jami’an tsaro s**a hana shi wucewa tare da umartar sa da ya tuntubi manajan cocin kafin a ba shi izinin shiga.

A cewarsa, ya ziyarci cocin ne k**ar yadda ya saba yi a sauran ƙasashen da ya kai ziyara, kuma bai ɗauki wata kyamara a hannunsa ba. Ya ce wayarsa ma tana cikin aljihunsa.

Traveltomtom ya ce jami’an sun bayyana masa cewa matakan tsaron da ake bi a cocin na da alaƙa da yanayin tsaro a Najeriya, musamman wajen tantance baƙi kafin su shiga.

Ya ce ya kuma bayyana musu cewa shi Kirista ne kuma ɗan darikar Katolika, amma duk da haka ba a ba shi damar shiga ba sai ya bi wasu ƙa’idoji.

Sai dai abin da ya fi ba shi mamaki, a cewarsa, shi ne yadda aka tarbe shi a Babban Masallacin Abuja.

Ya ce duk da kasancewarsa Kirista ba Musulmi ba, mutanen da s**a tarbe shi a masallacin sun nuna masa karamci tare da ba shi damar ɗaukar hotuna da bidiyo yadda ya ga dama.

Traveltomtom ya bayyana cewa bambancin tarbar da ya samu a wuraren biyu ya sa ya yi mamakin yadda lamarin ya kasance.

Ya ce abin da ya faru ya sa ya yi tunani sosai, musamman ganin cewa a wurin ibadar Musulmi an tarbe shi cikin fara’a, yayin da a cocin da ya je domin ziyara aka sanya masa wasu ƙa’idoji kafin ya samu damar shiga.

21/08/2026

Sakon Hukumar Hisba ta Jihar Kano Game da Taron Mauludi a Fadin Jihar Kano.

Akalla mutane 14,000 ne s**a mutu a Jamus sak**akon tsananin zafin rana a cikin watanni biyar na farkon shekarar 2026, a...
20/08/2026

Akalla mutane 14,000 ne s**a mutu a Jamus sak**akon tsananin zafin rana a cikin watanni biyar na farkon shekarar 2026, adadin da ya zarce wanda aka taba samu a shekarun baya.

Cibiyar Robert Koch (RKI) ta Jamus ce ta bayyana hakan a wani rahoto da ta fitar, inda ta ce mutuwar da ake alakantawa da tsananin zafi ta kai kimanin mutum 17 cikin 100,000 a tsakanin ranar 6 ga watan Afrilu zuwa 9 ga watan Agusta na shekarar 2026.

Rahoton ya nuna cewa adadin mutanen da zafi ya kashe a wannan shekara ya riga ya zarce na wasu shekarun baya. A cikin shekaru goma da s**a gabata, shekarar 2018 ce ta kasance cikin shekarun da aka fi samun mace-macen da s**a shafi zafi, inda aka kiyasta mutuwar mutane 9,400. A shekarar 2019 kuma, an samu kusan mutuwar mutane 7,600.

RKI ta ce yawan mace-macen da ake alakantawa da tsananin zafi na ƙaruwa cikin sauri, musamman idan aka yi la’akari da cewa a makon da ya gabata kaɗai adadin ya kai kusan mutane 12,000.

Tsofaffi ne s**a fi fuskantar barazanar

Binciken ya nuna cewa tsofaffi ne s**a fi fuskantar illar tsananin zafin rana. Daga cikin mutanen da s**a mutu, kimanin 7,040 na da shekaru 85 ko sama da haka.

Haka kuma, mutane kusan 3,450 da s**a mutu suna tsakanin shekaru 75 zuwa 84, yayin da wasu 2,170 ke tsakanin shekaru 65 zuwa 74.

Rahoton ya ce an samu mafi yawan mace-macen ne sak**akon tsananin zafin da aka fuskanta a ƙarshen watan Yuni, lamarin da ya ƙara jawo damuwa kan yadda sauyin yanayi ke ƙara tsananta matsalar zafi a sassan Turai.

Gwamnatin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta dakatar da duk wani aikin haƙar ma’adanai a yankin Zamboi, bayan wani mummunan...
20/08/2026

Gwamnatin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ta dakatar da duk wani aikin haƙar ma’adanai a yankin Zamboi, bayan wani mummunan zaftarewar ƙasa da ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100.

Ministan Ma’adanai da Nazarin Ƙasa da Duwatsu na ƙasar, Rufin Benam, ne ya sanar da matakin bayan ziyarar da ya kai yankin da lamarin ya faru a ranar Laraba.

Ko da yake hukumomin ƙasar ba su fitar da adadin mutanen da s**a mutu a hukumance ba, wani jami’in yankin Garou-Boulai da ke kan iyakar ƙasar ya shaida wa BBC cewa an riga an gano gawarwaki aƙalla 107 daga cikin ƙasa.

Lamarin ya kuma shafi wasu ƴan ƙasar Kamaru da ke makwabtaka da yankin. Gwamnan yankin Gabashin Kamaru ya tabbatar da cewa aƙalla ƴan ƙasar Kamaru uku ne s**a rasa rayukansu sak**akon zaftarewar ƙasar.

Hukumomi na ci gaba da gudanar da ayyukan ceto da bincike domin gano sauran mutanen da ka iya kasancewa ƙarƙashin tarkacen ƙasar.

Address

No 144 Kawon Mai Gari, Mal Shuaibu Street Kano

700001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TNU Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to TNU Hausa:

Shortcuts

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share