11/05/2026
Dan siyasar jam’iyyar ADC, Saidu Atiku Abubakar, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar majalisar wakilai ta tarayya domin wakiltar mazabun Birnin Kebbi, Kalgo da Bunza.
A cikin sanarwar da ya fitar, Saidu Atiku Abubakar ya ce ya yanke shawarar ne bayan sauraron bukatu da damuwar al’umma, musamman dattawa, matasa da mata, inda ya ce manufarsa ita ce yi wa jama’a hidima da gaskiya.
Ya bayyana cewa zai mayar da hankali wajen tabbatar da shugabanci mai adalci, bunkasa matasa da mata ta hanyar ilimi da samar da dama, inganta tsaro, lafiya da ababen more rayuwa, tare da tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki.
Dan takarar ya bukaci al’ummar mazabar da su ba shi goyon baya, addu’a da hadin kai domin gina makoma mai kyau ga kowa da kowa.
Saidu Atiku Abubakar ya kuma kara da cewa manufarsa ba wai shugabanci ba ne kawai, illa hidimtawa al’umma da ciyar da mazabar gaba karkashin jam’iyyar ADC.
Me za ku cs?