ULR HAUSA TV

ULR HAUSA TV An Kafa Wannan Jarida ce Domin Kawo Ingantattun Labarai A Lungu da Sako Na Fadin Duniya

Dan siyasar jam’iyyar ADC, Saidu Atiku Abubakar, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar majalisar wakilai ta tar...
11/05/2026

Dan siyasar jam’iyyar ADC, Saidu Atiku Abubakar, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar majalisar wakilai ta tarayya domin wakiltar mazabun Birnin Kebbi, Kalgo da Bunza.

A cikin sanarwar da ya fitar, Saidu Atiku Abubakar ya ce ya yanke shawarar ne bayan sauraron bukatu da damuwar al’umma, musamman dattawa, matasa da mata, inda ya ce manufarsa ita ce yi wa jama’a hidima da gaskiya.

Ya bayyana cewa zai mayar da hankali wajen tabbatar da shugabanci mai adalci, bunkasa matasa da mata ta hanyar ilimi da samar da dama, inganta tsaro, lafiya da ababen more rayuwa, tare da tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki.

Dan takarar ya bukaci al’ummar mazabar da su ba shi goyon baya, addu’a da hadin kai domin gina makoma mai kyau ga kowa da kowa.

Saidu Atiku Abubakar ya kuma kara da cewa manufarsa ba wai shugabanci ba ne kawai, illa hidimtawa al’umma da ciyar da mazabar gaba karkashin jam’iyyar ADC.

Me za ku cs?

11/05/2026

SHIRIN HAJII DA UMMARAH NA YAU LITININ 11-05-2026

Jam’iyyar APC reshen Jihar Kano ta fara tantance masu neman tikitin takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar gabanin zaɓe...
11/05/2026

Jam’iyyar APC reshen Jihar Kano ta fara tantance masu neman tikitin takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar gabanin zaɓen fidda gwani.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Yusuf Yahuza daga ofishin Sakataren Tsare-tsare na jam’iyyar APC a Kano ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar 11 ga Mayu, 2026.

Me za ku ce?

Wa’adin da INEC ta bayar na mika rajistar membobin jam’iyyu ya cika, lamarin da ka iya hana wasu masu neman takara da ma...
11/05/2026

Wa’adin da INEC ta bayar na mika rajistar membobin jam’iyyu ya cika, lamarin da ka iya hana wasu masu neman takara da masu son sauya sheƙa shiga zaɓen 2027.

Ana nuna damuwa cewa rikice-rikicen cikin gida a wasu jam’iyyu na iya jefa makomar wasu ‘yan takara cikin rashin tabbas.

Duk da cewa wa’adin ya kare a ranar Lahadi, ana sa ran INEC za ta iya karɓar takardu a yau Litinin saboda Lahadi ranar hutu ce.

Me za ku ce?

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Nairobi na ƙasar Kenya domin halartar taron Africa-France Summit.Ana sa ra...
11/05/2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Nairobi na ƙasar Kenya domin halartar taron Africa-France Summit.

Ana sa ran shugaban zai tattauna da shugabannin duniya kan sabbin fasahohi, bunƙasa tattalin arziki.

Me za ku ce?

Jam’iyyar APC reshen Jihar Rivers ta fitar da jerin sunayen masu neman takara da s**a tsallake tantancewa da kuma waɗand...
11/05/2026

Jam’iyyar APC reshen Jihar Rivers ta fitar da jerin sunayen masu neman takara da s**a tsallake tantancewa da kuma waɗanda aka hana shiga zaben fidda gwani na 2027.

Daga cikin mutum 98 da aka tantance, 33 sun samu damar shiga zaben fidda gwani, yayin da aka hana 65.

Abin da ya dauki hankali shi ne, dukkan mutum 32 da ake ganin suna da alaka da bangaren Gwamna Siminalayi Fubara ba su tsallake tantancewar ba.

Me za ku ce?

Kwamitin tantance ‘yan takarar majalisar dokokin Jihar Rivers na jam’iyyar APC ya tantance mutum 98 masu neman tikitin s...
10/05/2026

Kwamitin tantance ‘yan takarar majalisar dokokin Jihar Rivers na jam’iyyar APC ya tantance mutum 98 masu neman tikitin shiga zaɓen 2027.

An gudanar da tantancewar ne a ranakun Asabar da Lahadi a birnin Port Harcourt, inda sakataren kwamitin, Tanko Yamowa, ya yaba da yadda masu neman takarar s**a nuna natsuwa da bin doka yayin gudanar da aikin.

Me za ku ce?

Yunkurin sake tsayawa takarar gwamnan Jihar Rivers na Siminalayi Fubara ya fuskanci tangarɗa bayan rahotanni sun ce ya f...
10/05/2026

Yunkurin sake tsayawa takarar gwamnan Jihar Rivers na Siminalayi Fubara ya fuskanci tangarɗa bayan rahotanni sun ce ya fice daga dakin tantance ‘yan takarar jam’iyyar APC da ke Abuja a ranar Lahadi.

Yayin da sauran gwamnoni masu ci s**a kammala tantancewa a ranar Asabar, shi kuwa bai samu nasarar kammala nasa ba.

Me za Ku ce?

Yan takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a jam’iyyar APC sun janye wa tsohon gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, domi...
10/05/2026

Yan takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a jam’iyyar APC sun janye wa tsohon gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, domin ba shi damar tsayawa takarar kujerar Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya a zaɓen da ke tafe, k**ar yadda gidan talabijin na ARTV ya rawaito.

Me za ku ce?

10/05/2026

"Zaben 2027 Jihadi ne za ayi Tsakanin Zulunci Da Adalci" Inji Shugaban Matasan ADC Reshen Jihar Kebbi.

👇👇👇👇👇👇

An miƙa Bello Bodejo, mai neman takarar kujerar Sanatan Taraba ta Tsakiya a jam’iyyar APC, ga hukumar EFCC a Abuja.Bodej...
10/05/2026

An miƙa Bello Bodejo, mai neman takarar kujerar Sanatan Taraba ta Tsakiya a jam’iyyar APC, ga hukumar EFCC a Abuja.

Bodejo, wanda shi ne shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal H**e, jami’an tsaro sun k**a shi ne a daren Alhamis bayan isarsa filin jirgin Danbaba Suntai da ke Jalingo.

Me za ku ce?

Address

No, 14 Sani Abacha Express Way Birnin Kebbi
Birnin-Kebbi
860101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ULR HAUSA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share