Sani Twoeffect Yawuri Online

Sani Twoeffect Yawuri Online Blogger
Media Influencer
Writer
Media Consultant
Publisher
Content Creator

16/12/2025
16/12/2025

✌✌

Wasu Ƴan-uwa na jini ga tsohon ministan shari'ar Najeriya Abubakar Cika Malami SAN su biyu sun sauya sheƙa daga jam'iyya...
16/12/2025

Wasu Ƴan-uwa na jini ga tsohon ministan shari'ar Najeriya Abubakar Cika Malami SAN su biyu sun sauya sheƙa daga jam'iyyar adawa ta ADC zuwa Jam'iyyar APC mai mulki a Jihar Kebbi:

Daga Sani Twoeffect Yawuri

Waɗannan kannan na tsohon ministan shari'ar Najeriya da s**a sauya sheƙa zuwa Jam'iyyar APC sune:

1. Mustapha Malami Khadi
2. Sa'adu Malami Khadi
Waɗannan ƴan uwan na tsohon ministan shari'ar Malami SAN sun sauya sheƙar ne tare da magoya bayan su sama da mutum dubu ɗaya.

A karɓar masu sauya sheƙar a wurin taron kungiyar direbobin NURTW da aka shirya domin nuna goyon bayan su ga cigaban Maigirma shugaban ƙasa Sanata Bola Ahmed Tinibu GCFR da Maigirma Gwamna Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu wanda ya gudana a masaukin shugaban ƙasa wato Presidential Banquet Hall Birnin Kebbi, shugaban jam'iyyar APC na jihar Kebbi Alhaji Abubakar Kana Zuru ya bayyana cewar masu sauya sheƙar sun ɗauki matakin da ya dace na sauya sheƙar zuwa jam'iyyar APC mai mulki a wannan lokacin.

Haka kuma yayi musu maraba da zuwa jam'iyyar APC tare da basu tabbacin yi musu adalci a jam'iyyar k**ar kowani ɗan jam'iyyar APC haka kuma Maigirma Gwamna zai cigaba da basu dukkannin tallafin da ya dace.

Haka kuma shugaban jam'iyyar APC na jihar Kebbi yayi amfani da wannan damar wajen bayyana wasu ayyukan alheri da Maigirma Gwamna ya gudanar a cikin shekaru biyu da k**a aiki da s**a haɗa da: ɗaukar ƙwararrun malaman makaranta mutum 2,000, ƙara adadin kudin abincin dalibai a makarantun Jihar daga miliyan 150 zuwa miliyan 300 da kuma ƙara shekarun ritayar malaman makaranta dadai sauransu.

Shima da yake nasa jawabin, Maigirma Gwamnan Jihar Kebbi Kwamared Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu ya bayyana cewar Gwamnatin sa ta cika alƙawarin da ta ɗaukar wa al'ummar jihar Kebbi a lokacin zaɓen shekarar 2023 da kaso 90 cikin 100.

Haka kuma yayi godiya ga kungiyar NURTW bisa irin goyon bayan da suke cigaba da nuna masa da kuma Gwamnatin sa tun farkon tafiyar har zuwa yanzu.

Haka kuma ya bayyana cewar tun kafin ya zama Gwamna a lokacin yana shugaban ƙungiyar Malaman makaranta ta NUT suna da kyakkyawar hulɗa da kungiyar direbobin ta NURTW.

Haka kuma Gwamnan yayi amfani da wannan damar wajen bayyana wasu ayyukan alheri da Gwamnatin sa ta gudanar da s**a haɗa da ingantawa raya babban birnin jiha domin yayi gogayya da sauran takwarorinsa na Jihohin Najeriya.

Haka kuma ya bayyana cewar Gwamnatin sa ta cika kasa 90 cikin 100 na alkawurran da s**a ɗaukar ma al'ummar jihar Kebbi.

Haka kuma ya bayyana cewar Gwamnatin sa ta ɗauki sabbin kwararrun Malaman Makaranta mutum 2,000, ta raba takin zamani da iri kyauta ga manoman jihar Kebbi, injimin ban ruwa da kuma raba tallafin kayan abinci a lokuta daban-daban domin ragewa al'umma raɗaɗin matsin tattalin arziki.

Haka kuma ya bayyana cewar yanzu haka Gwamnatin sa ta shirya tsaf domin raba Power tillers da maganin haki da takin zamani kyauta ga monaman Jihar Kebbi mutum dubu hamsin (50,000).

Haka kuma Gwamnan ya ƙara da cewar yanzu haka Gwamnatin sa tana cigaba da gina wasu hanyoyi a ƙauyuka da birane a Malando zuwa Warah a ƙaramar hukumar mulki ta Ngaski da kuma wasu sassa na yankin ƙaramar hukumar mulki ta Bagudo.

Gwamnan ya ƙara da cewar, wannan ababen da s**a faɗa sunyi, ba karya kuma babu yaudarar al'umma a ciki, wanda yake ganin ba gaskiya bane zai iya bincikawa ya gani.

Gwamnan ya bayyana cewar sun samu makarantun jihar Kebbi cikin wani yanayi maras kyau inda s**a ɗauki ɗamarar tabbatar da gyara su da samar da kayan aiki.

Gwamnan ya bayyana cewar wasu mutane basu farin ciki da irin ayyukan alheri da suke gudanarwa, amma wannan bazai sa suyi ƙasa a guiwa ba wajen tabbatar da cigaba da gudanar da ayyukan alheri da zasu inganta rayuwar al'ummar jihar Kebbi.

Daga karshe yayi godiya ta musamman ga kungiyar direbobin ta NURTW bisa irin gudunmawa da goyon bayan da suke basu ba tare da gajiyawa ba.

Tun a farkon taron dai, kungiyar ta NURTW ta jaddada goyon bayan ta ga shugabancin Maigirma shugaban ƙasa Sanata Bola Ahmed Tinibu da kuma Maigirma Gwamna Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu a zaɓen shekarar 2027 mai zuwa idan Allah ya kaimu.

Da yake nasa jawabin, shugaban ƙungiyar direbobin NURTW na kasa Alhaji Najeem Usman Yasin, ya bayyana cewar sun kawo ziyara jihar Kebbi ne domin suyi godiya da jinjina ta musamman ga Maigirma Gwamna bisa irin ayyukan alheri da yake cigaba da gudanarwa a ɓangarori daban-daban da kuma irin gudunmawar da yake baiwa mambobin ƙungiyar ta NURTW.

Haka kuma ya bayyana cewar babu wata jiha a Najeriya ta take baiwa mambobin ƙungiyar kulawa ta musamman k**ar jihar Kebbi.

Haka kuma ya bayyana cewar bayan Sanata Adams Oshiomole, kaine mutum na biyu da kungiyar kwadago ta ƙasa take alfahari dashi.

Haka kuma ya bayyana cewar suna farin ciki da irin goyon bayan da al'ummar jihar Kebbi suke baiwa Maigirma Gwamna Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu.

Shugaban ƙungiyar ya kuma bayyana cewar yayi yawo a faɗin Najeriya, babu Jihar da ta gina tashar mota k**ar Maigirma Gwamnan Jihar Kebbi.

Shugaban ƙungiyar yayi kira ga mambobin ƙungiyar dasu tabbatar sun yanki katin zaɓe ko sabunta shi domin basu damar zaɓen shugaba Bola Ahmed Tinibu GCFR da Maigirma Gwamna Dakta Nasir Idris Ƙauran Gwandu a zaɓen shekarar 2027 mai zuwa tare da bayar da kuri'u sama da wanda s**a bayar a shekarar 2023.

Da ya juya ɓangaren tsaro, shugaban ƙungiyar direbobin ya yabawa Maigirma Gwamna bisa irin kokarin da yakeyi wajen inganta harkokin tsaro a fadin jihar Kebbi tare da kuma kwarin guiwar da ya nuna wajen tambayar bahasin wanda ya bayar da umarnin janye sojoji a lokacin da aka sace ɗaliban makarantar sakandaren mata ta Maga a ƙaramar hukumar mulki ta Danko-Wasagu.

A lokacin wannan taron a kaddamar sabon shugaban ƙungiyar direbobin tifa na jihar Kebbi ƙarƙashin Jagorancin kungiyar ta NURTW tare da sauran shugabannin kungiyar.

Haka kuma ƙungiyar ta baiwa Maigirma Gwamna kyautar karramawa bisa irin ayyukan alheri da yake gudanarwa a fadin jihar Kebbi.

Haka kuma a lokacin taron an karɓi ƙannan tsohon ministan shari'ar Najeriya da s**a sauya sheka zuwa Jam'iyyar APC

Signed Ahmed Idris

13/12/2025

A Leader by Example: Comrade Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu, Gwarzon Daular Usmaniyya.
Kebbi State 001

Address

Birnin-Kebbi

Telephone

+2348094147776

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sani Twoeffect Yawuri Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share