Jafar sa'ad

Jafar sa'ad alhamdulillah ala kulli halin

writer........✏✏✏

📝📝📝📝📝
📚📚📚📚
📖📖📖
WhatsApp number

👉.08163635039
(6)

Bakar inuwa.....Pa.  11.     ...👉....   ............*_SALLA BIKI ƊAYA RANA_*A duk wanda ka duba yau inhar musulmi ne naƙ...
10/06/2026

Bakar inuwa.....

Pa. 11. ...

👉.... ............*_SALLA BIKI ƊAYA RANA_*
A duk wanda ka duba yau inhar musulmi ne na
ƙwarai zaka fuskanci farin cikin zagayowar
wannan rana ta salla bisa fuskarsa. Rana ce da
mafi yawan al'umma s**a ganta s**a kuma
sake ganinta. Sai dai hakan baisa ta
gunduresuba. A kowace shekara murnar
zagayowarta ake yara da manya tamkar lokacin
s**a fara riskarta.
Ƙarfe goma na safe tawagar ɗunbin al'ummar
musulmi dake a sassa da dama na babban birnin
ƙasar Bingo da ke a NAYA s**a kammala sallar
Edi. Bakin kowa a washe yana gaida ɗan
uwansa ko aboki. Yayinda irin su Raudha baƙi a
garin keta ƙoƙarin ganin sun fito da ga harabar
babban masallaci idin domin samun abun
hawansu. Dan kuwa dai aunty Hannah ce da
kanta ta kwaso ƙwai da kwarkwatar yaran gidan
ta taho dasu filin na idi.
Duk da a ƙurarren lokaci su Raudha s**azo
Bingo tsaf Aunty Hannah ta haɗama kowansu
kayan salla na gani na faɗa. Wanda a zahirin
gaskiya first lady ce ta bada maƙudan kuɗaɗe
domin yin hakan. Su dukansu matan sanye suke
cikin baƙaƙen abayoyi ƙirar Egypt, sai dai ta
kowa ta banbanta da kalar adon da yafi buƙata.
Kasancewarsu ƙyawawa jinin ƴaƴan larabawa
duk da ba kowanne a cikinsu ya biyo iyayen
nasu ba sai gasu ɗas tamkar wasu ƴaƴan
manyan mutane.
Tafe suke Yasmin da twins na surutu da bada
labarin yaran da s**a zauna kusa da su basu iya
salla ba su Fatisa na dariya. Sai Raudha da
kusan ke ƙarshe a bayansu tana tafiya a nutse
dan sam bata iya sauri ko garaje ba. Kanta a
ƙasa yake tana ɗan kallon yara daketa kaikawo
cikin shigar malam bahaushe abin sha'awa.
Kamar ance ta dubi gefenta idanunta karaf akan
wani matashin saurayi da kallonsa kawai baida
daɗin yi. Duk da ranar salla ce kuma shigar farar
jallabiya yayi fara ƙal a jikinsa saita banbanta da
jikin nasa. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci baiyi
k**a da mutanen kirki ba.
Gabanta ya faɗi ganin yana gyara wata ƴar
wuƙa dake a hannunsa sai ƙyalli takeyi. Abinda
ke manne a kunnensa ya kai hannu ya gyarama
zama alamar magana yakeyi da wani, dan
bakinsa sai motsi yake yayinda idanunsa ke
kallon saitin inda yake tunkara. Juyawa tai da
ƙyau itama tana duban wajen. Zuciyarta ta ɗan
harba sabida yin tozali da wani kamilallen
dattijon tsoho ƙyaƙyƙyawa. Duk da shekaru
sunja garesa hakan bai hana bayyanar cikar
k**alarsa da jin daɗi ba. Tsaye yake akan
ƙafafunsa cikin ɗanyar shadda fara ƙal da ko
ba'a faɗaba kasan an narka kuɗi wajen ɗinkata.
Ya sake damƙe hannun mutumin da suke tare
fuskarsa na sake ƙawatuwa da murmushi alamar
gaisuwa sukeyi irin wadda take nuna an daɗe
ba'a haɗu da mutum ba. Sake maido kallonta tai
ga saurayin nan daketa sake tunkararsu. A take
jikinta ya fara rawa, tanaji a ranta akwai abinda
saurayin ke ƙullawa mara ƙyau a zuciyarsa game
da kamilallen tsohon da takejin nutsuwa a
zuciyarta game da shi. Badan ta sansa kota taɓa
ganinsaba sai ɗazun da suke shigowa
massallacin idin da wani tsoho daya fisa tsufa
sosai ya kusa faɗuwa. Dakaga tsohon na ɗazun
kasan talakane, amma sai ga wannan dattijo ya
zaburo har shima yana shirin faɗuwa ya tare
tsohon a jikinsa yana masa sannu, kasa ɗauke
ido tai a kansu a ɗazun har s**a shige cikin
massallaci yana riƙe da shi. Kwarjininsa da cikar
k**alarsa da shekarunsa na girmane kawai
s**aja hankalinta da zuciyarta nason
taimakonsa, (sai dai ta yaya?). Ta ambata a
zuciyarta batare da tasan amsa ba. Farga da
saurayin na gab da kaiwa garesa ga shi zai juya
baya ya sakata zabura ta nufesa. Kusan a tare
s**a ƙarasa ga dattijon ita da saurayin.
Cikin ƙwarewar aiki na iya kisa saurayin ya kaima
Alhaji Hameed Harith Taura yanka da kakkaifar
wuƙar hannunsa gayama jini na wuce yanka ta
gefen ciki. Inda ya tabbatar idan ya yanka sai ya
mutu kuma. Sai dai kash, wuƙar na gab da kaiwa
kansa batare daya fargaba dan yayi k**ar zai
wucene Raudha tazo ta tare yankan ya sameta a
cinyarta sak**akon ɗan tsallen da tayi nason
cimmasa.
Wata irin ƙara ta saki da damƙe cinyarta da
hannu guda ɗayan kuma ta damƙo rigar jazuga
dake son sake kaima Alhaji Hameed Taura wani
yankan ganin wannan Raudha ta tare. Kusan duk
wanda ke a kusa da su a wajen sai da ya juyo, a
take kuma duk akayo kanta. Inda Alhaji
Sammani yay azamar janye Alhaji Hameed
Taura dan bashi kariya daga yunƙurin saurayin a
karo na biyu. Hakanne yasa saurayin fincike
rigarsa daga hannun Raudha datai ƙasa zata faɗi
ya arta cikin na kare (gudu).
Da sauri Alhaji Hameed ya kai hannu ya riƙo
Raudha jikinsa na rawa. Dan duk mai hankali ko
ba'a masa bayanin komaiba zai fahimci abinda
yay shirin faruwar. Sai dai kafin ma kowa ya
nema ba'asi wani yaro da bazai gaza shekaru
goma sha uku ba yake faɗin duk abinda ya gani.
Dan kuwa akan idonsa Raudha taima Alhaji
Hameed Taura garkuwa daga suƙar wuƙar
saurayin.
Cikin ƙanƙanin lokaci ahalin Alhaji Hameed Taura
s**a zagaye wajen, ga securitys da ƴan agaji
suma duk sun iso. Duk mai tausayi sai ya
zubarma Raudha hawaye ganin irin mugun
yankan da saurayin yay mata a cinya, dan ma
ansa abu an yane ƙafar dan har rigar ya tsarge.
A sume take jikin Alhaji Hameed Taura dake
cikin matsanancin tashin hankali. Musamman
yanda Yasmin tazo ta faɗa jikin Raudha tana
kuka da girgizata.
Isowar Ambulance ɗin da ake jirace tasa mutane
darewa ma'aikatan asibitin s**a iso wajen da
keken ɗaukar mara lafiya. Da taimakon Alhaji
Basheer Hameed Taura da shima jikinsa ke
rawar tashin hankalin abinda yaso samun
mahaifin nasa aka ɗora Raudha bisa keken har
cikin Ambulance ɗin.

Daga ahalin gidan Taura har su aunty Hannah
kaiwa da komowa kawai suke na tashin hankali
a ƙofar ƙayataccen asibin na musamman da aka
kawota. Wanda tabbas badan dalili ba ko
katangarsa bai zama lallai Raudha ta taɓa
taɓawa ba harta ƙare rayuwarta. Da farko ƴaran
gidan Taura hankalinsu yafi tashine akan jin
kakansu aka kawoma harin ALLAH ya tsaresa.
Sai da s**aga hankalin Pa ɗinsu da kakan nasu
su kuma akan Raudhan yake sannan s**a ɗan
koma jimantawa. Koda za'a kawo Raudha
asibitin badan securitys da ke biye dasu har nan
ba da gida zasuyi wucewar su. Har mamakin
yanda Bappi da Pa suke a ruɗe sukeyi, sun san
yarinyar tayi ƙoƙarin kodan jarumtar da tayi na
tarar wannan azaba. Sai dai mafi yawansu sunaji
a ransu tayine dan neman suna ko kuɗi ko wani
abu daban koma tare take da saurayin. Dan sun
san haka kawai dai mutum bazai tarema wani
mutuwa ba babu dalili, ballema ƙaramar yarinya
irinta. Wasu ko a cikinsu gani suke koma bakin
saurayin da Raudha ɗaya ne, maybe akasi aka
samu kawai, ko kuma ƙaiƙayine ya koma kan
masheƙiya.
To koma dai miye Alhaji Hameed Taura da
ɗansa Alhaji Basheer Hameed Taura su ba haka
bane a nasu zuciyar. Ɗunbin tausayine na
Raudha da jinjinama ƙundunbalarta a ransu, sai
fatan ALLAH ya bata lafiya da taraddadin
wanene ya aiko saurayin ga wannan aikin? Dan
kuwa dai cikin hayaniyar mutane ya ɓace ɓat,
har s**a baro wajen securitys na nemansa ne
amma babu alamar zasu gansa.
Aunty Hannah da su Fatisa na rakuɓe a gefe
suma rayukansu fal mamakin abinda ya faru.
Dan sam babu wanda ya kula da sanda Raudha
ta tafi bama Taura kariya sai ƙararta s**aji, sai
ko sauran bayani a bakin mutane da s**a tsinta.
Yasmin dake kuka Alhaji Hameed Taura yazo ya
durƙusa gabanta, duk da tsufansa da matsayinsa
bai dubaba. Yasa hannayensa biyu yana share
mata hawayenta. Cikin lallashi yace, “Minene
sunanki?”.
“Yasmin!”.
Ta bashi amsa cikin shashshekar kuka.
“Oh mai sunan larabawa to kukan ya isa haka
ok? Kima aunty addu'a zata tashi lafiya kinji!”.
Kanta ta jinjina masa tana jan tagwayen ajiyar
zuciya. Tausayinta ya k**ashi matuƙa. Ɗunbin
k**annin daya gani tsakaninta da mara lafiyar
ya sashi hasashen ƴar uwartace. Hannunta yaja
ya zaunar a kusa da shi yana kai kallonsa ga
Muneera data koma can gefe tana waya k**ar
bataso a jita, da alama dai wani take sanarma
abinda ya faru. Ya san kuma bazai wuce
mamansu Gimbiya Su'adah ba. Dan tun ɗazun
yakejin kira na shigo masa waya ya tabbatar
Anne ce amma bai ɗauka ba. Yasan dai zuwa
yanzu labarin abinda ya faru ya karaɗe kowacce
kafar yaɗa labarai abinka da babban mutum.
Ko wane gidan tv ka kalla daga nuna sallar idi sai
zancen an kaima Alhaji Hameed Harith Taura
hari a filin idi. Yayinda hoton Raudha na kwance
cikin jini a hannunsa shima keta kai kawo.
Babu yanda Alhaji Basheer baiyi Bappi ya koma
gida ba amma yaƙi, ya tabbatar masa bazai iya
barin wadda ta fansar da lafiyarta a gareshi cikin
wannan halin ba ya iya komawa gida ya samu
nutsuwa. Dole ya ƙyalesa har lokacin da doctors
ɗin dake tare da Raudha s**a fito suna sanar
musu Alhmdllh ta farfaɗo. an kuma mata ɗinki a
wajen tare da alluran kariya daga gujewa wasu
cututtukan. Domin a bincikensu sun gano jikin
wuƙar akwai dafin maciji.
Wannan abu ya sake tayarma da Alhaji Hameed
da zuri'arsa hankali. Dan tabbas da an samesa
babu makawa zai iya rasa ransa kodan yanayin
jikin tsufa dake tare dashi..
*__________________________*
“Sai da nace maka yaron nan bazai iyaba Mr JK
amma ka dage akan ƙwararrene ta hanyar
wannan aikin”.
Ɗan takarar shugaban ƙasar NAYA a jam'iyyar
adawa ya faɗa cikin ɗunbin tashin hankali da
ruɗani yana nuna mutumin dake daura dashi a
ƙayataccen falon na alfarma. A tsakkiyar falon
kwanikane barbaje na abincin salla, sai sauran
mutane uku dake ta gefen hannun haggunsa
suma bisa kujerun rayukansu duk a ɓace.
Wanda aka kira Mr JK ya girgiza kansa cikin
takaici shima yana faɗin, “Karkaga laifina
Engineer. Ku kanku kunsan badan yarinyar can
data bashi kariyaba babu shakka sai aikin yaron
ya tafi dai-dai, sai yanzu na sake tabbatar da
Alhaji Hameed Taura ya wuce ifiritu sai dai
hatsabibi. Duk yanda muke tunanin cimmasa
cikin sauƙi abune mai wahala”.
Cikin sauran mutane ukun ɗaya ya amshe da
faɗin, “Tabbas abune mai wahala, sai dai ya
k**ata musan yarinyar nan ƴar uban wacece
ne? Sannan minene dalilinta na bashi kariya?.”
“Wannan yanada muhimmanci Alhaji Sale Sukini,
sai dai babban mai muhimmancin shine Alhaji
Hameed. Domin wannan abun daya faru babu
abinda zai ƙara masa sai farin jini ga jama'a. Ka
duba kaga cikin ƙanƙanin lokaci kowacce kafar
watsa labarai data yanar gizo ta ɗauka. yaya
kuke tunani idan rana tsaka ya fito da manufarsa
ta tsayawa takarar shugabancin ƙasar NAYA
kuma?”.
“Kuma gaskiya fa maganarka nakan hanya Alhaji
Badamasi. Domin barin Alhaji Hameed Taura a
raye tamkar hana yuwuwar nasararmuce. Babu
yanda zamu haɗa takara da shi a dubemu a
ƙasarnan, su kansu abinda s**a fahimta kenan
shiyyasa s**a jawoshi ya hau kujerar dan sauran
da s**a nuna sha'awa a jam'iyyar tasu duk
ruɓaɓɓune, babu wanda zai iya kawo kujerar.
Shiko duk da bawai siyasar ya bama ƙarfi ba
suna cewa gashi jama'a zasu amsa”.
Duk da ac dake aiki a falon hakan bai hana
Engineer zame hularsa ya hau fifita ba, dan wata
irin zufa ce ta ruɗani ke karyoma duka sassan
jikinsa. Ya tabbatar duk abinda abokan nasa
s**a faɗa shine gaskiya. Shiko a yanzu babu abinda yake buri da fata sama da shugabancin
ƙasar NAYA. yayi shekaru goma cif yana mulkin
bisa muƙamin gwamna. Yaji daɗi sosai ya koma
a kujerar majalissa itama shekaru biyar kenan,
yanzu kuma burinsa yakai ga kujerar daga ke
babu wata. A da hankalinsu kwance yake da
hangen nasara saboda waɗanda suke hasashen
jam'iyyar mai mulki zata bama takara duk
bazasuyi armashi ba. Sai dai labarin daya zo
musu sati kusan guda kenan akan zaman
shugaban ƙasa da Alhaji Hameed Taura da kowa
ke tunanin takara sukeson bashi ya ɗaga musu
hankali. Domin kuwa a majiya mai ƙarfi s**aji
hakan daga bakin wani munafikinsu dake cikin
mulkin na shugaban ƙasa a yanzun. Sun yarda
da shine bisa dalilin ba yaune karo na farko daya
kawo musu labariba kuma ta tabbata daga fadar
shugaban ƙasar na NAYA.
Zaman sake sabon ƙulli s**ai akan Alhaji
Hameed Taura da baisan sunayi ba ma.......... *_Tofa maƙiya ta ko ina🤔_*
*_GOVERNMENT HOUSE_*
Kamar yanda abokan adawa kecan suna
tattaunawa anan fadar ta shugaban ƙasar NAYA
ma hakanne. Dan kowannensu na kallon abinda
ya farunne ta fuskar siyasa. Alhaji Hameed Taura
mutumin kirkine da kowa ke yabon halayensa
tun ƙuruciya. Dan ko lokacin daya ɗan fara
bayyana kansa a siyasa mutane ƙalilanne s**a
soki hakan.
Su kansu rayuwar Alhaji Hameed Taura bawai
damuwarsu bace. Sai dai basa buƙatar rasata a
yanzu har sai sun cimma nasu burin sannan. Dan
haka zasu sake tsayawa tsayin daka wajen ganin
sun bashi kariya har su tsallake.
*_(ya ALLAH. Siyasa batai ba😱🚶🏻)._*
Duk da tare shugaban ƙasa yay salla da Alhaji
Hameed Taura a babban masallaci kuma har
abin ya faru bai koma gidaba hakan bai hanashi
sake sabon shiru shi da tawagarsa s**a nufi
asibitin da aka kai Raudha ba. Dan labari ya
samesu cewar Alhaji Hameed Taura na asibitin.
Dolene suma suje su nuna jimaminsu da bama
al'amarin muhimmanci tunda shima ya ɗaukesa
da girma.
*_TK SPECIAL HOSPITAL_*
Cikin ƙanƙanin lokaci asibitin ya ƙara samu
tsatstsauran tsaro a dalilin isowar shugaban ƙasa
da tawagarsa. Hakan bai bama kowa mamaki ba
saboda sanin amintakar dake tare da shugaban
ƙasar da Alhaji Hameed Taura. Dole aunty
Hannah ta ɓuya dan bata buƙatar shugaban
kasa yasan tanada alaƙa da Raudha a yanzun.
Bayan sun duba Raudha dake cikin ƙyaƙyƙyawar
kulawa shugaban ƙasa ya tilasta Alhaji Hameed
fitowa s**a ɗunguma zuwa Taura house tunda
jikin nata Alhmdllh. Da wannan damar suma
sauran yaran duk s**a gudu gida tunda daman
zaman kakansu sukeyi anan ɗin. Sai dai anbar
Raudha cikin tsananin tsaro da kulawa ta
kowanne fanni. Ga ƙyaututtukan maƙudan
kuɗaɗe da waɗanda s**a rako shugaban ƙasa
duk s**ai mata. Sai a lokacin su Aunty Hannah
s**a sami damar shiga s**a dubata da ƙyau
suma. Dan ɗazun Alhaji Hameed ne kawai ya
shiga da Pa.
Sun tausaya mata ƙwarai da gaske, dan ƙafar
tata ta matuƙar kumbura sai ma ratayeta akai
jikin wani ƙarfe. Barci takeyi ga jinin data zubar
ana ƙara mata. Kusan mintuna sha biyar akace
su fito dan ba'a buƙatar kowa ya zauna da ita
saboda gudun abinda zaije ya dawo. Hakan
yasa dole Aunty Hannah ta kwashi su Fatima
s**a koma gida suma. Dan tun ɗazun dama
Asabe ke kira da wayar hajiyar birni tana kuka
akan su sanar mata idan Raudha ta rasu ta
haƙura kawai. Dan duk wanda yaga Raudha a
hoton dake yawo babu tantama zai ce ta mutu
ne, musamman yanda jini yay faca-faca a jikinta
cikin ƙanƙanin lokaci. Danma baƙar rigace a jikin,
sai dai adon farin zare da akai mata yasaka jinin
bayyana ga idanun mutane..........✍
*_Tofa wannan fa shine ake kira ƙaddara ta riga
fata. Su aunty Hannah na neman ƙulla hanyar
dalili, ga dalilin wanda ya fisu sanin gaibu shi ya
ƙulla ta hanyar da basuyi zato ko tsammani ba.
Masu karatu yaya za'a kwashe kenan to?....

Follow me for more..... Jafar sa'ad.

Yar macheeeee..Part.   11.     ....👉....   "Kada ki ce zaki dauki burgewa akan nawarayuwar ni da Yarana muna bukatar Uwa...
10/06/2026

Yar macheeeee..

Part. 11. ....

👉.... "Kada ki ce zaki dauki burgewa akan nawa
rayuwar ni da Yarana muna bukatar Uwa a cikin
gidan nan, don Allah ki mana alfarman ki zauna
a gida, ina matukar kishinki!" Ya fada yana kamo
hannuna, ji nayi k**ar zan yi kuka wani ya fada
min abin da yake ranshi wanin ma Tafida da
k**ar wuya gurguwa da auren nesa. Kasa
magana nayi ya kai ni wani daki yana faɗin.
"Wannan shine dakina, yayi kyau ko na sauya
domin dakuna uku ne a nan bangaren, naki
dakuna hudu saboda baki da wasu laluran.
Bangaren dayan kuma akwai dakuna uku shima
k**ar nawa." "Duk yaushe ka yi gidan nan?"
Hannunshi ya kai gefen fuskata. Yana murmushi
ya ce talla aka kawo min lokacin muna abuja,
shine na gayawa Deen ya shi kuma ya gayawa
Abba. Kafin na turo kudin ma Abba ya biya sai
na maidawa Abba kudinsa, amma kin san me?
Ko da aka zo saka sunan mamallakin gidan
Abba sunanki ya saka." Murmushi nayi sai na
kasa magana, ya fito dani zuwa daya dakin yana
cewa. "Duk wani abu na gidan Deen ya zuba
min su." "Saboda baka da lokaci ne?" Gyada
min kai yayi yana jan hancina. "Bani da lokacin
da xan zauna nayi ta wannan aikin, shi da
Matarshi da kanwarshi Jalilah s**a min wannan
aikin." Murmushi yayi yana faɗin. "Ina tsoron
kada wata rana na juyawa Deen baya." "Idan
haka ya faru zai maka uzuri! Domin shi
ma'abocin uzuri ne!" Murmushi yayi wanda
tunda muka fara zaga gidan shine akan fuskarshi, muna gama
zaga cikin gidan ya ce min. "Muje ki ga
bangarenki!" "Na gaji sallah isha zan yi na
kwanta jikina duk ciwo yake!" "Wai ki ce zan yi
tausa kenan?" Ya fada yana kashe min ido daya,
parlourn muka dawo muka shimfida abin sallah,
ya shiga bandakin parlour yayi alola nima anan
nayi alola, shi ya jamu sallah isha da tarawee,
muna idarwa na kasa hakuri nace mishi. "Kayi
sauka ne kai ma?" Saboda yadda yake jan
kira'a. Addu'a ya shafa yana faɗin. "Eh nayi na
fara a Nijeriya zuwana Sudan Deen ya saka ni a
gaba sai da na hada sittin hankalinsa ya kwanta.
" "Gaskiya ya kyauta mana!" Jan kumatuna yayi
yana faɗin. "kwarai kuwa ya kyauta min tunda
Allah ya haɗa ni da Hafiza!" Janyo ni yayi muka
kwanta a parlourn ina jikinshi kwance. D'ago kai
nayi ina kallonshi. "Yan mata bar kallona, ni naki
ne duk wacce zata zo tow sudinki zata samu;"
rufe fuskana nayi a kirjinshi ina dariya. "Naji
kamshin turaren Tina a jikinki dazun gaya min
yadda kika gudu daga garina." A hankali na
warware mishi kome, murmushi yayi yana faɗin.
"Yarinyar nan baki da tausayi!" Ya tashi zaune,
"Ni sau nawa ka tausaya min?" Na tambaye shi,
"kishin yadda Abba yake sonki, yake kuma
damuwa da ke yasa ni jin haushi, taya ni da ya
dace ya bawa kulawa ya koma nawa Yar mage
kulawa!" Ya fada ina kallonshi. "Ni ce ma
mage?" Shafa kaina yayi yana faɗin. "Yes ke
magena ce, idan ban yi kishin magena ba waye
zan yi kishi. Ke magena ni muzurunki!" Ya fada
yana rungume ni, dariya nayi ina kara k'amkame
shi. "yaushe zaki min dambu ne?" Kallon
bakinshi nayi na matsa a hankali na kai bakina,
janyo ni nayi na zauna a jikinshi muna fuskarta
juna. "Duk lokacin da kake bukata kazo ka
ɗauka." Bakina ya k**a da hakorinsa. A hankali
ya sake yana faɗin. " Ba zata zaki min kuka ne
k**ar crybaby!" "Dake ka saba ganin kuka a
idanuna ba!" Wayarshi ce tayi ƙara ya duba
Mahmoud ya gani dauka yayi yana faɗin. "ya
dai?" "Tafida dama na kira ne zamu zo da
madam ku gaisa!" "Bana nan wallahi idan na
dawo zan gaya maka sai ku zo mu sha ruwa
tare" "ok na gode amma kana ina ne?" *Ka koyi
boye mana kome hatta ni bana bukatar sanin
privacy dinka!* inji Deen ya gaya mishi. "Eh tow
bana kusa gaskiya!" "Tow ba damuwa, ko kana
tare da yar baka ce?" "Me kace?" Ya tambaye
shi a fusace. "yar baka nace ko kana tare da ita
ne?" "Daga yau kada na kara jin ka ambaci
Ummu da wanann sunan, Mata ta ce kuma
Uwar Yarana, idan kuma ka sake raina zai b'aci
zan yi hukunci." "Tow kayi hakuri na ga dai a
bakinka naji!" "Eh a bakina ka ji na tab'a aibanta
matarka? Ko na tab'a baka shawara ka cutar da
ita?"
"Tafida kayi hakuri ban san ranka zai b'aci ba,
amma yaushe ka fara sonta?" Wani ashar ya
lailayo ya maka mishi take ya kashe wayar
domin Allah ya gani yana bala'in shakkar Tafida.
Jifa da wayar yayi, na bi wayar da sauri na
dauko ina faɗin. "Ji k**ar an ce min yar wuta."
Na shiga duba wayar ina kallonshi. "ka godewa
Allah da wayar bata fashe ba!" Na mika mishi
wayar ina rike hannunshi, shafa bayan hannun
nake. "Kada ka damu tun ina Yarinyar na taso da
kushen mutane, wannan ba sabon abu ba ne."
"Ummu idan baki yafe min ba Allah sai ya kona
ni!" "Ba zai kona ni saboda na bawa kare da
dokin damar cin zarafinki." Kwantar da kaina
nayi a gefen kafadarshi, ina murmushi. Na
fahimci Tafida ya sauya sosai, amma tijara yana
nan babu abinda ya bari, wurin sha daya na dare
ya haɗawa Yaran madara, muka basu, sannan
nayi musu wanka da ruwan dumi. Kafin muka
wuce dakin na kwantar da su, ban daki ya shiga
ya jima kafin ya fito daure da Towel. "Taso
muje!" "A'a jeka kawai!" Zuwa yayi ya dauke ni
cak, sai ban dakin, ya sauke ni yana faɗin. "Kina
tsammanin zaki kwanta min a haka ne!" Kayan
ya shiga cire min, yana faɗin. "Malama babu
bakin magana ne!" Ya cire rigar ya ajiye can
gefe, sai pant da bra! Juyo ni yayi na rufe
idanuna. "Cancadi, wannan bra din yayi min
kyau, gaskiya ina son irinsu." Ya kai hannu yana
ɓalle pin din. Ni dai bance mishi kome ba yana
gamawa ya kai hannun kan abin da yake jan
hankalinsa. (😡😒 Ni rashin mutuncin Tafida
ya fara isata.) Ban iya lokacin da muka dauka a
banɗakin ba, amma tabbas naji k**ar yau na
fara haduwa da d'a namiji, koda muka dawo
daki sha biyu ta wuce, a bangaren Tafida kuwa
tunda muka dawo dakin, ya makale min domin
ba zance wani abu, ina jin labarin ayu amma yau
naga makwafin ayu. Ban san yadda xan fada ba,
amma tunda ya manne min bawan Allah nan
daga ni har shi idanunmu biyu har aka kira sallah
farko. Yana makale a jikina yana jin k**ar zan
kwace na gudu. A hankali yake bin kome tun
kiran sallah farko, farko yake jan tafiyar a hankali
cikin sanyi da kulawa, ban tab'a sanin halinshi na
zahiri ba sai yau, yau ya fito min a mutum dinsa,
na kuma fahimci waye shi. Kallon fuskarshi nayi
cikin rawan murya na ce mishi. "Yallabai!" Bude
idanunshi da s**a ji ja ya zuba min. "asuba tayi
kada mu rasa sahur!" Kamar dama jiran
maganata yake kafin na rufe baki ya shiga aikin
da ban san yana da karfin yinsa ba. Ni dai a
hannunshi na ji a jikina, sai da na fashe da kuka
saboda yadda ya fita hayacinsa haka yasa ni jin
k**ar Tafida baya mu'amalar aure da
Sa'adiyya, domin da yanayi da kuzarinsa ba xai
yi yawa kuma ya dauki lokaci haka ba, sai da
muka kusan makara ya kyale ni, kasa tafiya nayi
domin kafaffuna k**ar ba zasu dauke ni ba,
haka ya riko ni zuwa banɗaki nayi wanka asalima
zama nayi cikin ruwan dumin, a gurguje na fito
na samu ya hada min tea mika min yayi da zafi-
zafi na sha sannan ya ce min! "Sannu kin ji!"
Dake ina bakin gadon daure da towel, kasa
kallonshi nayi ina gama sha ya mika min farfesun
jiya, kafin ya wuce yayi wanka sannan ya fito
shima yayi sahur. Ganin ina bawa Yaran nono ya
dawo bayana ya zauna tare da saka hannunshi
dukka biyu a kasan cikina. "Ina tumbin?"
Murmushi nayi nace mishi. "Ya koma!" Shiru yayi
kafin ya sumbaci dokin wuyata. Muna zaune a
wurin aka sake kiran sallah, amsa Mufid yayi ya
kwantar da shi sannan ya amshi Mufidah ma,
kafin ya ciro min doguwar rigana, muka yi
raka'atul fijr. Muna idarwa ana shiga sallah
asuba, a tare muka yi sallah, bayan mun idar
mun jima muna addu'a, da azkar sai da rana ya
fara fitowa na rarrafa domin sai yanzu na ji kafar
ya min tsami. Gadon na hau na kwanta don
wallahi jikina ciwo yake, musamman yadda ya
makale yaki kome don rashin kirki, na juya xan
harare shi. Ware idanun yayi yana faɗin. "me
nayi kuma ake hararana da alamu ana zagina a
rai kenan, tow na yafe miki, yar aljannata!"
Kwanciya nayi ya dawo bakin gadon ya zauna
tare da rike hannuna yana murzawa, murmushi
muke sakarwa juna, a hankali barci yayi gaba da
ni, shima gadon ya hau ya kwanta a bayana,
tare da janyo ni jikinshi. Ban da azumi babu abin
da zai hana shi komawa ruwa shi ya san abin da
ya ji ya kuma tab'a ya ji. A hankali shima barci
yayi gaba da shi, wato ranar Tafida tun kafin yau
ya mikawa Deputy koma ya ce mishi sai
Monday.
***
A bangaren Mama tunda ta sauka ta kira uwani
s**a gaisa ta ce mata. "Ina Ummu!" "Yaronta bai
da lafiya, sun kai shi asibiti ita da Deen wayarta
kuma kin san tun tafiyarta ta saba barin shi a
gida!" "Tow Masha Allah idan na samu lokaci
zan na kiranku, yanzu lokaci ne na ibada a
kwanakin karshe xan mika lamarin Ummu da
naku ga Ubangiji, in sha Allah kafin na dawo zan
yi addu'a sosai Ubangiji ya kawo miki miji na gari
mijin marainiya kin ji Uwanina!" "Tow Uwata sai
kin dawo Allah ya baki ikon mana addu'a!" S**a
yi sallama. Mama tana son Uwani sosai irin so na
gaskiya nan takewa Uwani yarinyar ma tana son
Mama. Haka Mama da ta kira Baba Bulama
shima ya gaya mata ai Ummu danta bai da lafiya
ne, ganin duk bakinsu daya yasa Mama ta
yarda, bata san cin amanarta s**a yi ba.
***
Karfe daya da rabi na farka, na samu yaran an
musu wanka sai wasa suke da junansu, idan ba
mafarki ba ina ga har nono Tafida ya ciro ya
basu amma dake barci ya ci karfina ban iya
bude idanun ba. "sleep beauty!" Make hannunshi
nayi ina faɗin. "Kai da Yaranka sai da kuka
shanye min nono ko?" Na fada ina gyara zaman
rigar jikina. "Ayya sun tashi na rasa yadda xan yi
shi ne na gyara ki na basu kowanne ya k**a,
suna gama sha na dama masu madara s**a
sha, kin ga har wanka nayi musu!" "Yaushe ka
dawo Nanny!" "Taso na hada miki ruwan wanka
kin ji!" Tashi nayi na ga yaran aka wani abin
wasan Yara. Yana tsaye yana kad'awa Mufidah
da take bangala mishi baki, na zo na rungume
shi ta baya, karatu Tinah. "Good afternoon My
Yallabai!" Wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana
faɗin. "Qurratul-Ayn! Kin tashi lafiya?" Juya mishi
idanun nayi na wuce banɗaki, na leko yana
tsaye inda na barshi. "Baby bani jakata akwai
brush da toothpaste!" "Akwai sabi na bude
mana!" Murmushi nayi na ce mishi. "Ban gani
ba!" "Don Allah ki rike wannan muryan taki,
wallahi ban shirya yin sittuna ba!" Ya shigo ban
dakin ya dauka tare da matsa min. "fita kafin ka
karya mana azumi!" Na fada a sanyaye. "Idan
aka ga na suma kece wallahi!" Murmushi nayi na
rufe ban dakin nayi wanka sosai, sannan na fito,
shi da Yaranshi suna can parlour, na gyara jikina
kafin na fito, muryanshi da naji da Deen yasa na
koma dakin, sai kuma na saka Babban hijab na
fito na gaishe da Deen, sai Hararata yake yana
faɗin. "Ke bana ce kada ki fito ba!" "Ka ji guntun
dan iska, ita Kanwata ce yayar Jalila ce, ka saka
Ammah ce ta haife ta dan iska kawai! Ummu ina
fatan bai miki kome ba ko?" Ya tambaye shi
yana nad'e hannun rigarshi. Dariya s**a bani na
girgiza kai ina faɗin. "Bai min kome ba! Ya
Sadika tana lafiya ta kusan sauka kan yanzu ko!"
"Eh wallahi ina kyautata zaton karshen watan ko
farkon sabon wata!"
"Allah ya raba lafiya! Yallabai kitchen nake son
shiga na maka aikin kafin na tafi!" "Ba fa zaki tafi
yau ba, sai wata sati!" Rufe bakina nayi da
hannayena, wani irin tsoron Mama ya dirka min
k**ar an wurgo dutse daga sama. "Ka rufa min
asiri!" Murmushi yayi ya ce min. "Allah da gaske
wayar mana na saka an sace shi a can Saudiya
amma fa za a dawo mata da shi, kiyi hakuri
Alhaji Bulama da Babanki sun sani, hankalin
Mama ya kasu gida biyu tana ibada kuma kafin
faruwar haka tayi waya da Mijinta da kuma
Uwani, ki fahimci wani abu ina son mu kasance
tare shi yasa na zabi haka amma kiyi hakuri da
abin da nayi, wallahi bani da zabi ne ina son na
zauna da ke na wasu kwanaki kafin ta dawo
Please!" Hawaye ne ya zubo min. "Yanzu kawai
don ka zauna da ni sai ka sakata a zullumi bata
yi magana da kowa ba." "Mama ba irin sauran
iyaye ba ne, Mama tayi magana da kowa kafin
na saka.aka dauke wayar amma bari Deen ja ce
yarinyar ta maida mata wayarta." Juyawa nayi
zan koma dakin ya ce min. "Ki shirya zan mai
dake gidan!" Yadda yayi maganar sai naji
hankalina ya tashi, haka na wuce dakin na zauna
ina jin kuka yana zuwa min.
"Kana burge ni Tafida, kai tsaye kake lamarinka.
Na ji dadi da kake fadar gaskiya ba ƙaramin aiki
bane fadarta." "Deen tafiya zata yi fa!" "Ba zata
tafi ba, yanzu ka je kace ta shirya zaka fita.
Sallah juma'a zaka ajiye ta a gidansu!" Ya kuwa
mike, ya nufi dakin Deen sai dariya yake mishi
yana wasa da Yaran kaunar da yakewa Iyayen
Yaran ya shafi yaran sosai, don yana jinsu k**ar
na shi.
A bakin gadon na zauna ina shashekar kuka,
domin nasan ba wani sauyawan da yayi, yayi
min laifi k**ata yayi yazo ya rarrashe ni amma
yace wai na shirya zai ajiye ni a gida, wato yaci
moriyar ganga, duk sai naji na tsani kaina da ban
biyo shi ba da ba zai min haka ba, haka na
cigaba da kuka, ban kawo a raina zai zo din ba
sai gashi ya turo kofar, wani irin sanyi naji ya
tsirga min, na d'ago kai ina kallonshi shima
kallona yaƙe. "Allah ya huci zuciyarki, nayi laifi a
yafe min dama can ni tsohon mai laifi ne, kuma
na kara aikata bayan laifi ayi hakuri ba zan kuma
ba." Ban kalle shi ba, na cigaba da share kwalla
da yake zuba min, "Tow tunda ba zaki min
magana ba, bari na hada kayanki na kai ki gida!"
"Dama ka kawo ni ne ka min koran kare!" *Yes i
hit the point!" Narke min yayi cikin rarrashi ya ce
min. "a'a tashi na kai ki gida don Allah, wannan
abin da nayi ina jin kunyar kallon idanunki!" Ya
fada yana me durkusawa a gabana ya zuba
hannunshi akan cinyoyina. "Ni dai kada garin son
zama dani kayi ta aikata kuskure bayan kuskure,
ka rufa min asiri kada kayi wani abin da zai tab'a
rayuwarmu bakiɗaya." Na fada ina kuka, "ita
mahaifiyata ce, dole naji wani abu na ga k**ar
ba sona kake ba, dama can na san Babu so
kawai muradi ne ta zuciya...." hannunshi ya saka
ya rufe min bakina. "Don Allah ki daina fadar
haka wallahi bana jin dadi, nima Uwata ce,
yanzu haka na saka za a maida mata wayarta
ba zan kara wasa da rayuwar wani saboda ke
ba, amma kiyi hakuri ba zan kara ba kin ji!"
Gyada kai nayi ina share hawayen da yake zuba
min. "Kiyi hakuri xan tafi sallah kada na makara!"
"Allah ya tsare muje na tayaka shirya." Gaban
closed din shi muka nufa na cire mishi wani
babban kaya shadda ce fara sal, sai hular da zai
haka da kayan, sai takalmi da links zamana da
shi a abuja, baya saka babban kaya dai ranar
Juma'a. Amma kusa na haddace shigarshi.
Yadda yaga ina taya shi saka kayanshi ba tare
da na damu ba, ya ce min."Ina tunanin ko idan
kika dawo na barki a nan ne ba sai kin je
government house!" Shafa kumatunshi nayi ina
faɗin. "Duk yadda kace yallabai na!" Jan hancina
yayi yana faɗin. "An gama yarinyar nan hancinki
Mufid ya dauka. Mufidah nawa!" Ya fada yana
haɗe rai. Dariya nayi ina faɗin. "Kuma laifi ne
don haka ya faru?" "Kawai dai kishi nake da kika
raba shi Abba ya dauki hancinki Ita Uwata kika
barta da irin nawa hancin!" "Ba ka ga yadda
yaran s**a zamo kalanka ba!" "Hmm kuma haka
ne kin fini gaskiya!" Ya fada yana rike hannuna,
"ki so ni koda dan ne, ni dai nasan ina miki
mahaukacin so ne! Ummu Hadiyya ina sonki
sosai, irin son da nake jin ban yiwa kowa irinsa
ba." Girgiza kai nayi ina faɗin. "'Lokaci yana tafi
kace fada zaka je sallah!" "Eh anan nake zuwa
tunda na zama gwamnanku!" Jan kumatunshi
nayi ina faɗin. "Ka kyauta!" "Gobe asabar zamu
shiga Biu ki shirya da wuri fa." Kallenshi nayi
kafin na ce mishi. "Gobe kace amma kana ce
min na shirya da wuri!" Na fada ina yaƙe. Mika
mishi hular da yake hannuna nayi ya kansa ya
kafa, wurin turaren shi na nufa na ciro na fara
fesa mishi yana murmushi. "Na gode zan tafi mai
xan sayo miki!" "Duk abin da ka gani ya maka
kyau ina so nima zan min kyau!"
"Hmm ji nake k**ar kada na tafi!" "Muje maza
Yayana yana jiranka, ka wani bar mishi renon
Yaranka!" Muka fito ina gefenshi, "Nanny sannu
da kokari ka ji!" "Kam uban can ni ne Nanny?"
Deen ya fada da karfi yana nuna kanshi. "Lallai
tafiya daga dan iska sai kai, a rashin mutunci ni
zaka kalli tsabar idanuna kace min Nanny ka
ɗauke ni dan daudu ne!" Yadda Deen yake tijara
sai naga sam haka bai damu Tafida ba, asalima
sumbatar goshin yaran yayi yana faɗin. "Kuyi
hakuri Abbanku yana ta ihu, sai na dawo Yarann
Daadi da Abba! Idan ka gama basu dariya muje
don Allah!" Wayarshi ce tai ƙara ya kalla yana
sake tsaki yayi ya ce. "Deen ya zan yi da Asiya
ne?" "Ina ruwan sly Queen!"
Juyowa yayi ya kalle ni, "wata cousin dina ce!" "
ka gaya mata me k**a fatalwa kin san an bashi
mace dan iska ya ce baya so!" "Deen kada ka ja
min bala'i don Allah!" "Yaya Deen kace dama
can amanata kuke ci?" "A'a ban dani dan iska
dai yake cin amanarki!" Ya nuna tafida da hannu,
"Ka aurota!" Na fada zan juya, "Ni fa ba dan iska
ba ne, kuma abu daya gare ni kin ga ya wuce
daya ne? Da zaki ce na aurota!" "Yallabai ko
bance ka aurota ba, wajibi ne auren mata sama
da daya, Allah ya baka budi da rufin asiri in dai
ba son zuciya ba, ai kana da damar rike mu
mata hudu!" "Ummu Hadiyya ki fita idanuna na
rufe. Auren ce miki aka yi da sauki ne da shi da zan rike mace
sama da daya Hadiyya ki fito Ki gaya min bakya
bukatar zama da ni mana!" Murmushi nayi na
wuce shi don nasan ya cika haka s**a fita, a
waje ya amsa wayar yana me bude mata tsohon
littafinsa na tijara, jin tana kuka yasa shi
sasauatawa ya tambaye ta me ya faru, bai
karasa ji ba ya kashe wayar ya nufi massalaci
yana zargin Deen da hada mishi husuma me
Deen zai yi ban da dariya.
Bayan fitarsu nayi alola na zo nayi sallah, sannan
na kunna wayata na kira Uwani na gaya mata ba
zan dawo ba, ta ce min ai Baba ya gaya mata.
Murmushi nayi sannan na kashe wayar na ja
Yarana muka shiga kitchen, mamakin yadda aka
zuba kome na zamani nayi, ina cikin aiki wurin
karfe biyu da arba'in da biyar, ya kira ni. "Ummu
Hadiyya! Akwai matsala!" "Ina tare da kai babu
wata matsala gaya min me nene?" Daga can na
ji Deen yana faɗin. "wallahi billahi azim ba zata
zauna a inda Ummu take ba, ka kaita gidan
Abba ko ko gidan Hajiya ba zata zauna ba,
Ummu tana buƙatar ka kana bukatar Ummu,
meye amfanin kebewan da kayi ba don ku huta
ba ne, Yaran nan wallahi ban da suna shn mama
da na rabaku dasu, ko ka kaita gidan Maryam
amma ban da Ummu."
"Wai me ke faruwa ne?" Kashe wayar yayi.
Mamaki ya kara k**ani na kira Tafida, "zan kira
ki!" Kashe wayar yayi..
**
A can kuwa Abin da ya faru, Asiyah ta sab'a
lamba, domin ta tabo Saadiya a daidai lokacin
da take cike da Tafida, abun da ya faru kuwa,
tun da Tafida ya bar gidan bai gaya mata zai tafi
bude sabon t**i a wani kauye ba, take cika take
batsewa domin a bakin yan gulmanta take jin
labarin, har dare aka sha ruwa babu Tafida, ta
kira Deen lokacin yana waya da ya gama ya
kashe wayar domin shi dai bai da amsar da zai
bata, wurin karfe hudu na asuba k**ar ance ta
fito ta hango Asiyah ta fito k**ar daga ɓangaren
Tafida, haka yasa ta kara kallon sosai ganin ta ga
sun sake rungumar juna, kafin ta wuce inda take
zama, tana ganin ya shiga Mota ya bar gidan.
Jikinta yana tsuma kawai ta fito da gudu lokacin
Asiya ta shiga bangaren da take ta rufe kofarta,
komawa tayi ta shirya har karfe daya na rana
Asiya bata fito ba, sai wurin karfe biyu ta fito. Ai
kuwa Sa'adiyya tayi wuf da ita tayi ta bugata da
kasa, tana bata kashi. Sannan ya yakushe mata
fuska tana ihu karuwa kwartuwa me bin mijin
wasu. Yadda kuka san mahaukaciya haka aka
dauke Sa'adi baby akan Asiyah, duk abin ba
dadin gani. Da ta samu ta shige dakinta ta kira
Tafida tana kuka, shiri tayi amma bata zata
wannan me kalar samudawan zata mata mugun
duka haka ba, sai gashi ta yakushe mata fuska,
sai da tayi kukan bakin ciki, bayan sallah juma'a
Tafida yazo gidan ganin har lokacin Sa'adiyya
tana ihun sai ta kashe Asiyah yasa Tafida kallon
Deen. "Ku sake ta ku je!" Suna barin wurin ya
nufeta. Aikuwa farar shaddan jikinshi ta damke
wuyar rigarsa da ta yaga har kasa. "gaya min me
nayi maka zaka ci amanata, ashe karuwa ka
ajiye a gidanka, shine ka hanani hakkina, wallahi
ba zan yarda ba muje ka bani hakkina nima na
haihu k**ar Ummu." "Kin ga nan ba k**ar da
can baya bane, ko ina akwai jami'an tsaro
Please mu shiga daga cikin gidan!" Dake tana
ganin girman Deen haka s**a shiga rarrashinta
da tambayar me ya faru bakincikin ya hanata
fadar abin da ya faru sai kuka da rantsuwar
matukar bai d'aga Asiyah a gidan ba zai samu
gawarta, dakyar Deen ya kwantar da rigimarta,
sannan yazo ya ga Asiyah sai da yaji babu dad'i.
Yarinyar fuskarta ya kumbura. Shine yake
tunanin ya kawo ta wurin Ummu ta yi jinya, Deen
yace karya kenan. Ba zai yiwu lokacin da ya
samu zai kula da kanshi da iyalinsa yace zai
karawa kanshi yan sa'ido ba, don haka yasan
yadda zai yi da ita......

Follow me for more... Jafar sa'ad.

Address

Bulkachuwa
2233

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jafar sa'ad posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share