10/06/2026
Bakar inuwa.....
Pa. 11. ...
👉.... ............*_SALLA BIKI ƊAYA RANA_*
A duk wanda ka duba yau inhar musulmi ne na
ƙwarai zaka fuskanci farin cikin zagayowar
wannan rana ta salla bisa fuskarsa. Rana ce da
mafi yawan al'umma s**a ganta s**a kuma
sake ganinta. Sai dai hakan baisa ta
gunduresuba. A kowace shekara murnar
zagayowarta ake yara da manya tamkar lokacin
s**a fara riskarta.
Ƙarfe goma na safe tawagar ɗunbin al'ummar
musulmi dake a sassa da dama na babban birnin
ƙasar Bingo da ke a NAYA s**a kammala sallar
Edi. Bakin kowa a washe yana gaida ɗan
uwansa ko aboki. Yayinda irin su Raudha baƙi a
garin keta ƙoƙarin ganin sun fito da ga harabar
babban masallaci idin domin samun abun
hawansu. Dan kuwa dai aunty Hannah ce da
kanta ta kwaso ƙwai da kwarkwatar yaran gidan
ta taho dasu filin na idi.
Duk da a ƙurarren lokaci su Raudha s**azo
Bingo tsaf Aunty Hannah ta haɗama kowansu
kayan salla na gani na faɗa. Wanda a zahirin
gaskiya first lady ce ta bada maƙudan kuɗaɗe
domin yin hakan. Su dukansu matan sanye suke
cikin baƙaƙen abayoyi ƙirar Egypt, sai dai ta
kowa ta banbanta da kalar adon da yafi buƙata.
Kasancewarsu ƙyawawa jinin ƴaƴan larabawa
duk da ba kowanne a cikinsu ya biyo iyayen
nasu ba sai gasu ɗas tamkar wasu ƴaƴan
manyan mutane.
Tafe suke Yasmin da twins na surutu da bada
labarin yaran da s**a zauna kusa da su basu iya
salla ba su Fatisa na dariya. Sai Raudha da
kusan ke ƙarshe a bayansu tana tafiya a nutse
dan sam bata iya sauri ko garaje ba. Kanta a
ƙasa yake tana ɗan kallon yara daketa kaikawo
cikin shigar malam bahaushe abin sha'awa.
Kamar ance ta dubi gefenta idanunta karaf akan
wani matashin saurayi da kallonsa kawai baida
daɗin yi. Duk da ranar salla ce kuma shigar farar
jallabiya yayi fara ƙal a jikinsa saita banbanta da
jikin nasa. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci baiyi
k**a da mutanen kirki ba.
Gabanta ya faɗi ganin yana gyara wata ƴar
wuƙa dake a hannunsa sai ƙyalli takeyi. Abinda
ke manne a kunnensa ya kai hannu ya gyarama
zama alamar magana yakeyi da wani, dan
bakinsa sai motsi yake yayinda idanunsa ke
kallon saitin inda yake tunkara. Juyawa tai da
ƙyau itama tana duban wajen. Zuciyarta ta ɗan
harba sabida yin tozali da wani kamilallen
dattijon tsoho ƙyaƙyƙyawa. Duk da shekaru
sunja garesa hakan bai hana bayyanar cikar
k**alarsa da jin daɗi ba. Tsaye yake akan
ƙafafunsa cikin ɗanyar shadda fara ƙal da ko
ba'a faɗaba kasan an narka kuɗi wajen ɗinkata.
Ya sake damƙe hannun mutumin da suke tare
fuskarsa na sake ƙawatuwa da murmushi alamar
gaisuwa sukeyi irin wadda take nuna an daɗe
ba'a haɗu da mutum ba. Sake maido kallonta tai
ga saurayin nan daketa sake tunkararsu. A take
jikinta ya fara rawa, tanaji a ranta akwai abinda
saurayin ke ƙullawa mara ƙyau a zuciyarsa game
da kamilallen tsohon da takejin nutsuwa a
zuciyarta game da shi. Badan ta sansa kota taɓa
ganinsaba sai ɗazun da suke shigowa
massallacin idin da wani tsoho daya fisa tsufa
sosai ya kusa faɗuwa. Dakaga tsohon na ɗazun
kasan talakane, amma sai ga wannan dattijo ya
zaburo har shima yana shirin faɗuwa ya tare
tsohon a jikinsa yana masa sannu, kasa ɗauke
ido tai a kansu a ɗazun har s**a shige cikin
massallaci yana riƙe da shi. Kwarjininsa da cikar
k**alarsa da shekarunsa na girmane kawai
s**aja hankalinta da zuciyarta nason
taimakonsa, (sai dai ta yaya?). Ta ambata a
zuciyarta batare da tasan amsa ba. Farga da
saurayin na gab da kaiwa garesa ga shi zai juya
baya ya sakata zabura ta nufesa. Kusan a tare
s**a ƙarasa ga dattijon ita da saurayin.
Cikin ƙwarewar aiki na iya kisa saurayin ya kaima
Alhaji Hameed Harith Taura yanka da kakkaifar
wuƙar hannunsa gayama jini na wuce yanka ta
gefen ciki. Inda ya tabbatar idan ya yanka sai ya
mutu kuma. Sai dai kash, wuƙar na gab da kaiwa
kansa batare daya fargaba dan yayi k**ar zai
wucene Raudha tazo ta tare yankan ya sameta a
cinyarta sak**akon ɗan tsallen da tayi nason
cimmasa.
Wata irin ƙara ta saki da damƙe cinyarta da
hannu guda ɗayan kuma ta damƙo rigar jazuga
dake son sake kaima Alhaji Hameed Taura wani
yankan ganin wannan Raudha ta tare. Kusan duk
wanda ke a kusa da su a wajen sai da ya juyo, a
take kuma duk akayo kanta. Inda Alhaji
Sammani yay azamar janye Alhaji Hameed
Taura dan bashi kariya daga yunƙurin saurayin a
karo na biyu. Hakanne yasa saurayin fincike
rigarsa daga hannun Raudha datai ƙasa zata faɗi
ya arta cikin na kare (gudu).
Da sauri Alhaji Hameed ya kai hannu ya riƙo
Raudha jikinsa na rawa. Dan duk mai hankali ko
ba'a masa bayanin komaiba zai fahimci abinda
yay shirin faruwar. Sai dai kafin ma kowa ya
nema ba'asi wani yaro da bazai gaza shekaru
goma sha uku ba yake faɗin duk abinda ya gani.
Dan kuwa akan idonsa Raudha taima Alhaji
Hameed Taura garkuwa daga suƙar wuƙar
saurayin.
Cikin ƙanƙanin lokaci ahalin Alhaji Hameed Taura
s**a zagaye wajen, ga securitys da ƴan agaji
suma duk sun iso. Duk mai tausayi sai ya
zubarma Raudha hawaye ganin irin mugun
yankan da saurayin yay mata a cinya, dan ma
ansa abu an yane ƙafar dan har rigar ya tsarge.
A sume take jikin Alhaji Hameed Taura dake
cikin matsanancin tashin hankali. Musamman
yanda Yasmin tazo ta faɗa jikin Raudha tana
kuka da girgizata.
Isowar Ambulance ɗin da ake jirace tasa mutane
darewa ma'aikatan asibitin s**a iso wajen da
keken ɗaukar mara lafiya. Da taimakon Alhaji
Basheer Hameed Taura da shima jikinsa ke
rawar tashin hankalin abinda yaso samun
mahaifin nasa aka ɗora Raudha bisa keken har
cikin Ambulance ɗin.
★
Daga ahalin gidan Taura har su aunty Hannah
kaiwa da komowa kawai suke na tashin hankali
a ƙofar ƙayataccen asibin na musamman da aka
kawota. Wanda tabbas badan dalili ba ko
katangarsa bai zama lallai Raudha ta taɓa
taɓawa ba harta ƙare rayuwarta. Da farko ƴaran
gidan Taura hankalinsu yafi tashine akan jin
kakansu aka kawoma harin ALLAH ya tsaresa.
Sai da s**aga hankalin Pa ɗinsu da kakan nasu
su kuma akan Raudhan yake sannan s**a ɗan
koma jimantawa. Koda za'a kawo Raudha
asibitin badan securitys da ke biye dasu har nan
ba da gida zasuyi wucewar su. Har mamakin
yanda Bappi da Pa suke a ruɗe sukeyi, sun san
yarinyar tayi ƙoƙarin kodan jarumtar da tayi na
tarar wannan azaba. Sai dai mafi yawansu sunaji
a ransu tayine dan neman suna ko kuɗi ko wani
abu daban koma tare take da saurayin. Dan sun
san haka kawai dai mutum bazai tarema wani
mutuwa ba babu dalili, ballema ƙaramar yarinya
irinta. Wasu ko a cikinsu gani suke koma bakin
saurayin da Raudha ɗaya ne, maybe akasi aka
samu kawai, ko kuma ƙaiƙayine ya koma kan
masheƙiya.
To koma dai miye Alhaji Hameed Taura da
ɗansa Alhaji Basheer Hameed Taura su ba haka
bane a nasu zuciyar. Ɗunbin tausayine na
Raudha da jinjinama ƙundunbalarta a ransu, sai
fatan ALLAH ya bata lafiya da taraddadin
wanene ya aiko saurayin ga wannan aikin? Dan
kuwa dai cikin hayaniyar mutane ya ɓace ɓat,
har s**a baro wajen securitys na nemansa ne
amma babu alamar zasu gansa.
Aunty Hannah da su Fatisa na rakuɓe a gefe
suma rayukansu fal mamakin abinda ya faru.
Dan sam babu wanda ya kula da sanda Raudha
ta tafi bama Taura kariya sai ƙararta s**aji, sai
ko sauran bayani a bakin mutane da s**a tsinta.
Yasmin dake kuka Alhaji Hameed Taura yazo ya
durƙusa gabanta, duk da tsufansa da matsayinsa
bai dubaba. Yasa hannayensa biyu yana share
mata hawayenta. Cikin lallashi yace, “Minene
sunanki?”.
“Yasmin!”.
Ta bashi amsa cikin shashshekar kuka.
“Oh mai sunan larabawa to kukan ya isa haka
ok? Kima aunty addu'a zata tashi lafiya kinji!”.
Kanta ta jinjina masa tana jan tagwayen ajiyar
zuciya. Tausayinta ya k**ashi matuƙa. Ɗunbin
k**annin daya gani tsakaninta da mara lafiyar
ya sashi hasashen ƴar uwartace. Hannunta yaja
ya zaunar a kusa da shi yana kai kallonsa ga
Muneera data koma can gefe tana waya k**ar
bataso a jita, da alama dai wani take sanarma
abinda ya faru. Ya san kuma bazai wuce
mamansu Gimbiya Su'adah ba. Dan tun ɗazun
yakejin kira na shigo masa waya ya tabbatar
Anne ce amma bai ɗauka ba. Yasan dai zuwa
yanzu labarin abinda ya faru ya karaɗe kowacce
kafar yaɗa labarai abinka da babban mutum.
Ko wane gidan tv ka kalla daga nuna sallar idi sai
zancen an kaima Alhaji Hameed Harith Taura
hari a filin idi. Yayinda hoton Raudha na kwance
cikin jini a hannunsa shima keta kai kawo.
Babu yanda Alhaji Basheer baiyi Bappi ya koma
gida ba amma yaƙi, ya tabbatar masa bazai iya
barin wadda ta fansar da lafiyarta a gareshi cikin
wannan halin ba ya iya komawa gida ya samu
nutsuwa. Dole ya ƙyalesa har lokacin da doctors
ɗin dake tare da Raudha s**a fito suna sanar
musu Alhmdllh ta farfaɗo. an kuma mata ɗinki a
wajen tare da alluran kariya daga gujewa wasu
cututtukan. Domin a bincikensu sun gano jikin
wuƙar akwai dafin maciji.
Wannan abu ya sake tayarma da Alhaji Hameed
da zuri'arsa hankali. Dan tabbas da an samesa
babu makawa zai iya rasa ransa kodan yanayin
jikin tsufa dake tare dashi..
*__________________________*
“Sai da nace maka yaron nan bazai iyaba Mr JK
amma ka dage akan ƙwararrene ta hanyar
wannan aikin”.
Ɗan takarar shugaban ƙasar NAYA a jam'iyyar
adawa ya faɗa cikin ɗunbin tashin hankali da
ruɗani yana nuna mutumin dake daura dashi a
ƙayataccen falon na alfarma. A tsakkiyar falon
kwanikane barbaje na abincin salla, sai sauran
mutane uku dake ta gefen hannun haggunsa
suma bisa kujerun rayukansu duk a ɓace.
Wanda aka kira Mr JK ya girgiza kansa cikin
takaici shima yana faɗin, “Karkaga laifina
Engineer. Ku kanku kunsan badan yarinyar can
data bashi kariyaba babu shakka sai aikin yaron
ya tafi dai-dai, sai yanzu na sake tabbatar da
Alhaji Hameed Taura ya wuce ifiritu sai dai
hatsabibi. Duk yanda muke tunanin cimmasa
cikin sauƙi abune mai wahala”.
Cikin sauran mutane ukun ɗaya ya amshe da
faɗin, “Tabbas abune mai wahala, sai dai ya
k**ata musan yarinyar nan ƴar uban wacece
ne? Sannan minene dalilinta na bashi kariya?.”
“Wannan yanada muhimmanci Alhaji Sale Sukini,
sai dai babban mai muhimmancin shine Alhaji
Hameed. Domin wannan abun daya faru babu
abinda zai ƙara masa sai farin jini ga jama'a. Ka
duba kaga cikin ƙanƙanin lokaci kowacce kafar
watsa labarai data yanar gizo ta ɗauka. yaya
kuke tunani idan rana tsaka ya fito da manufarsa
ta tsayawa takarar shugabancin ƙasar NAYA
kuma?”.
“Kuma gaskiya fa maganarka nakan hanya Alhaji
Badamasi. Domin barin Alhaji Hameed Taura a
raye tamkar hana yuwuwar nasararmuce. Babu
yanda zamu haɗa takara da shi a dubemu a
ƙasarnan, su kansu abinda s**a fahimta kenan
shiyyasa s**a jawoshi ya hau kujerar dan sauran
da s**a nuna sha'awa a jam'iyyar tasu duk
ruɓaɓɓune, babu wanda zai iya kawo kujerar.
Shiko duk da bawai siyasar ya bama ƙarfi ba
suna cewa gashi jama'a zasu amsa”.
Duk da ac dake aiki a falon hakan bai hana
Engineer zame hularsa ya hau fifita ba, dan wata
irin zufa ce ta ruɗani ke karyoma duka sassan
jikinsa. Ya tabbatar duk abinda abokan nasa
s**a faɗa shine gaskiya. Shiko a yanzu babu abinda yake buri da fata sama da shugabancin
ƙasar NAYA. yayi shekaru goma cif yana mulkin
bisa muƙamin gwamna. Yaji daɗi sosai ya koma
a kujerar majalissa itama shekaru biyar kenan,
yanzu kuma burinsa yakai ga kujerar daga ke
babu wata. A da hankalinsu kwance yake da
hangen nasara saboda waɗanda suke hasashen
jam'iyyar mai mulki zata bama takara duk
bazasuyi armashi ba. Sai dai labarin daya zo
musu sati kusan guda kenan akan zaman
shugaban ƙasa da Alhaji Hameed Taura da kowa
ke tunanin takara sukeson bashi ya ɗaga musu
hankali. Domin kuwa a majiya mai ƙarfi s**aji
hakan daga bakin wani munafikinsu dake cikin
mulkin na shugaban ƙasa a yanzun. Sun yarda
da shine bisa dalilin ba yaune karo na farko daya
kawo musu labariba kuma ta tabbata daga fadar
shugaban ƙasar na NAYA.
Zaman sake sabon ƙulli s**ai akan Alhaji
Hameed Taura da baisan sunayi ba ma.......... *_Tofa maƙiya ta ko ina🤔_*
*_GOVERNMENT HOUSE_*
Kamar yanda abokan adawa kecan suna
tattaunawa anan fadar ta shugaban ƙasar NAYA
ma hakanne. Dan kowannensu na kallon abinda
ya farunne ta fuskar siyasa. Alhaji Hameed Taura
mutumin kirkine da kowa ke yabon halayensa
tun ƙuruciya. Dan ko lokacin daya ɗan fara
bayyana kansa a siyasa mutane ƙalilanne s**a
soki hakan.
Su kansu rayuwar Alhaji Hameed Taura bawai
damuwarsu bace. Sai dai basa buƙatar rasata a
yanzu har sai sun cimma nasu burin sannan. Dan
haka zasu sake tsayawa tsayin daka wajen ganin
sun bashi kariya har su tsallake.
*_(ya ALLAH. Siyasa batai ba😱🚶🏻)._*
Duk da tare shugaban ƙasa yay salla da Alhaji
Hameed Taura a babban masallaci kuma har
abin ya faru bai koma gidaba hakan bai hanashi
sake sabon shiru shi da tawagarsa s**a nufi
asibitin da aka kai Raudha ba. Dan labari ya
samesu cewar Alhaji Hameed Taura na asibitin.
Dolene suma suje su nuna jimaminsu da bama
al'amarin muhimmanci tunda shima ya ɗaukesa
da girma.
*_TK SPECIAL HOSPITAL_*
Cikin ƙanƙanin lokaci asibitin ya ƙara samu
tsatstsauran tsaro a dalilin isowar shugaban ƙasa
da tawagarsa. Hakan bai bama kowa mamaki ba
saboda sanin amintakar dake tare da shugaban
ƙasar da Alhaji Hameed Taura. Dole aunty
Hannah ta ɓuya dan bata buƙatar shugaban
kasa yasan tanada alaƙa da Raudha a yanzun.
Bayan sun duba Raudha dake cikin ƙyaƙyƙyawar
kulawa shugaban ƙasa ya tilasta Alhaji Hameed
fitowa s**a ɗunguma zuwa Taura house tunda
jikin nata Alhmdllh. Da wannan damar suma
sauran yaran duk s**a gudu gida tunda daman
zaman kakansu sukeyi anan ɗin. Sai dai anbar
Raudha cikin tsananin tsaro da kulawa ta
kowanne fanni. Ga ƙyaututtukan maƙudan
kuɗaɗe da waɗanda s**a rako shugaban ƙasa
duk s**ai mata. Sai a lokacin su Aunty Hannah
s**a sami damar shiga s**a dubata da ƙyau
suma. Dan ɗazun Alhaji Hameed ne kawai ya
shiga da Pa.
Sun tausaya mata ƙwarai da gaske, dan ƙafar
tata ta matuƙar kumbura sai ma ratayeta akai
jikin wani ƙarfe. Barci takeyi ga jinin data zubar
ana ƙara mata. Kusan mintuna sha biyar akace
su fito dan ba'a buƙatar kowa ya zauna da ita
saboda gudun abinda zaije ya dawo. Hakan
yasa dole Aunty Hannah ta kwashi su Fatima
s**a koma gida suma. Dan tun ɗazun dama
Asabe ke kira da wayar hajiyar birni tana kuka
akan su sanar mata idan Raudha ta rasu ta
haƙura kawai. Dan duk wanda yaga Raudha a
hoton dake yawo babu tantama zai ce ta mutu
ne, musamman yanda jini yay faca-faca a jikinta
cikin ƙanƙanin lokaci. Danma baƙar rigace a jikin,
sai dai adon farin zare da akai mata yasaka jinin
bayyana ga idanun mutane..........✍
*_Tofa wannan fa shine ake kira ƙaddara ta riga
fata. Su aunty Hannah na neman ƙulla hanyar
dalili, ga dalilin wanda ya fisu sanin gaibu shi ya
ƙulla ta hanyar da basuyi zato ko tsammani ba.
Masu karatu yaya za'a kwashe kenan to?....
Follow me for more..... Jafar sa'ad.