Suzai Hausa Newspaper

إِنَّ اللَّهَ وَمَلَائِكَتَهُ يُصَلُّونَ عَلَى النَّبِيِّ ۚ يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا صَلُّوا عَلَيْهِ وَسَلِّمُوا ...
20/05/2026

إِنَّ اللَّهَ وَمَلَائِكَتَهُ يُصَلُّونَ عَلَى النَّبِيِّ ۚ يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا صَلُّوا عَلَيْهِ وَسَلِّمُوا تَسْلِيمًا

Allah sarkiAna wasu gyare-gyare da rushe-rushe aka birkito wata fila dauke da mutum sukutum yasha siminti da rodina.😭
18/05/2026

Allah sarki

Ana wasu gyare-gyare da rushe-rushe aka birkito wata fila dauke da mutum sukutum yasha siminti da rodina.😭

Da Dumi Dumi Kotu ta bayar da belin El-Rufai kan Naira miliyan 100Wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar da beli ga tsoho...
18/05/2026

Da Dumi Dumi

Kotu ta bayar da belin El-Rufai kan Naira miliyan 100

Wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta bayyana cewa an bayar da belin ne kan kudi Naira miliyan 100, tare da sharadin cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro da ke Abuja.

‎Bari ku ji wani abun haushi da takaici. ‎A shekarar 2014, Minimum Wage ₦18,000 ne. Shine mafi ƙarancin albashin da Good...
18/05/2026

‎Bari ku ji wani abun haushi da takaici.
‎A shekarar 2014, Minimum Wage ₦18,000 ne. Shine mafi ƙarancin albashin da Goodluck Ebele Jonathan ya sawa hannu a National Minimum Wage Act 2011.
‎💢A wannan lokacin, ₦18,000 daidai take da $109 saboda $1 daidai take da ₦165.
‎💢Mutumin da yake ɗaukar albashin ₦18,000 a 2014, a yanzu daidai take da mai ɗaukar albashin ₦149,400.
‎💢Mutumin da yake ɗaukar albashin ₦70,000 a 2014, a yanzu daidai yake da mai ɗaukar ₦583,516 saboda ₦70K a shekarar 2014 daidai take da $425.
‎💢Idan albashin ka ₦100,000 ne a 2014, a yanzu albashin ka daidai yake da mai ɗaukar ₦845,755 saboda ₦100k a shekarar 2014 daidai take da $616.

‎Idan kana ganin Minimum Wage na ₦70k ɗin da TNB ya sakawa hannu a yanzu wani abun arziƙi ne, ya k**ata ka koma baya ka kalli farashin duk wani abu daka sani a nan ne zaka tabbatar da cewa a yanzu BUSHASHIYAR GANDA ce kake ci ba romo. 70K daidai take da $51 a yanzu - wadda a 2014 kuma wannan ₦70k ɗin $425 ce should in case koda ka manta.
‎💢Bari na baka wani lissafi; idan kana ɗaukar albashin ₦70k a 2014, ga kayan da zaka iya siya da wannan albashin:

‎🤏Buhun Shinkafa Thailand 50kg ₦7,800
‎🤏Buhun Sugar BUA 50kg ₦8,500
‎🤏Buhun Flour BUA 50kg ₦8,700
‎🤏Buhun Siminti guda 4 ₦7,400
‎🤏Macaroni Golden Penny Carton 3 ₦6,000
‎🤏 Silver Spaghetti Carton 3 ₦6,000
‎🤏 Complete jarkar mai Kwalba 50 ₦12,500.
‎🤏Litre 11 na man Fetur ₦1,067
‎🤏 Sabon Generator Tiger ₦12,000.
‎💢Idan ka lissafa dukkan waɗancan kayan a shekarar 2014 zaka tarar kuɗin ya k**a ₦69,967 ne complete. Mai albashin ₦70 a 2014, zai iya siyan kayan da mai albashin ₦900,000 a yanzu bai isa ma ya tarki siya ba ko waye.

‎A ƙa'ida, a yanzu ya k**ata ace minimum wage na ƙaramin ma'aikacin Nigeria ya kasance ₦600,000 ne idan ka yi comparing ɗin sa da shekarar 2014. Albashin ƙaramin ma'aikacin gwamnati mai Minimum Wage na ₦18,000 a 2014 kaɗai shine zai siya maka dukkan waɗancan abubuwan dana lissafa maka a sama, a yanzu mai Minimum Wage na ₦70k a 2026 baban sa ko shine shugaban rundunar Custom na ƙasa bai isa ya sayi Buhun Shinkafa 2 ba komin iya cinikin sa wlh. Karka ɗauka gwamnati wani abun arziƙi ne ta yi, cigaban mai tonon rijiya ne. Malam k**ar kaine kake tafiya a jirgin sama sai aka dawo da kai kan wheelbarrow rana tsaka saboda tsabar jahilci. Wai fa a hakan ma har yanzu akwai jihohin da ita kanta wannan ₦70k ɗin ma ba'a biya. Can you imagine?. Amma a haka shugabannin Nigeria zasu mutu can zaka hango wani kazge da dogon bakin sa mai shegen zarni yana ganin k**ar ma saɓon Allah ne ko rashin godiyar Allah dan talakan Nigeria yace bai yafe ba😒. Allah sa wani ya same Ni face to face yace min na yafe. 😒🙏

‎Salisu Yakubu RN RNT

Malam wallahi ka boye sirrinka daga mutane! Daga jiya zuwa yau mutane dayawa sun yi farin ciki da jin labarin cewa dan m...
18/05/2026

Malam wallahi ka boye sirrinka daga mutane!
Daga jiya zuwa yau mutane dayawa sun yi farin ciki da jin labarin cewa dan majalisar tarayya daga jihar Plateau Hon. Yusuf Gardi ya rasa damar sake komawa majalisa a zaben share fage na shiga babban zabe, wato Primary election.

Shin ko kun san dalilin da yasa su ke jin dadi da murna?

Babban bakin cikinsu shine Yusuf Gardi ya samu kudi ya auri Layla Uthman suna rayuwar jin dadi, suna ci suna sha suna zuwa duk inda su ke son zuwa a duniya suna hutawarsu. Wannan shine babban bakin cikin wasu da ke jin dadin faduwarsa zaben share fage.

A tunani irin na su idan kudin Yusuf Gardi su ka kare Layla Uthman baza ta zauna da shi ba, aurensu zai mutu ta sake fitowa yawon zauranci.

Jama'a dan Allah mu ji tsoron Allah mu cire hasada, dan Allah mu gane cewa auren Sunnah su ka yi ba zaman dadiro bane, mu gane cewa kowa da arzikin da Allah ya kaddare shi da ya samu a duniyar nan.

Ni dai wallahi ina masa fatan samun matsayin da ya zarce wanda yake akai yau, ina rokon Allah kara masa arziki, mu kuma da mu ke nema Allah ya ba mu halaliyarmu.

S-bin Abdallah Sokoto

Innalillahi Wa'inna Ilairraji'un😭 Yashiga mota kano line lfy qlau akayi lodin motar dashi sunfara tafiya kadan kawae aka...
18/05/2026

Innalillahi Wa'inna Ilairraji'un😭
Yashiga mota kano line lfy qlau akayi lodin motar dashi sunfara tafiya kadan kawae akaga ya sunkuya yarasu.

Allah yaso anyi cike ciken da ake kafin atafi ana rubuta number da address wasu dake cikin motar dakuma wanda yake ciki yayi posting yace sunata kiran yan uwansa kowanne aka kira yace yanada uxuri aeki yake.

Nace anya ba wani abu yasa xebar gida ba xuciyar sa ta buga!? Allahu a'alam amma Yak**ata a bincika wasu yan uwan kuma kuji tsoron Allah wlhy koda da wani abu kutum yawuce wannan wulaqanchi.😭💔

Yanxu fa nan gawarsa ce ahaka :Innadillahi wainnahilaihi rajiun dan Adam ba komae bane Allah yasa mucika da imani don darajan annabi 😭😭😭😭😭😭

Wannan na daga nau'in ciwon ƙodar dake bibiyar family, wato na gado ne, kuma bashi da magani, galibi rayuwarsu takaitacc...
18/05/2026

Wannan na daga nau'in ciwon ƙodar dake bibiyar family, wato na gado ne, kuma bashi da magani, galibi rayuwarsu takaitacciya ce, yana bayyana immediately s**a cika 30years ko kafin ma 30 ɗin, yawanci daga nan kuma ba wata tafiya bace me nisa. Koda anyi dashen ƙoda baya tasiri domin abinda ke lalata ta a jikin mutum yake.

Ko a wannan sahar na haɗu da masu wannan larurar, mutum na farko guraren 2016 ne, tun daga 2017 ban qara jidaga garesa ba, account dinsa ma ba'a hawa, haka naita magana shiru har shekara da shekaru s**a juyo ba labari. Bazan mamaki ba idan yaƙi ne ya cinye Maza, koda yana raye wancan lokacin zuwa yanzu 10years bisa ilimi ya k**ata ace yana kabari kam, Amma Allah ne ke da ikon komi.

Polycystic kidney Disease kenan, Ya Allah ka baiwa dukkan marasa lafiya afuwa, idan ciwon shine silar ajalinsu ya Allah ka saukaka musu jinya, kasa ranar mutuwarsu ta zamto ranar farin cikinsu.

A lura da lafiya. A kuma godewa Allah, ina qara jaddada muku talauci ba shine karshen tashin hankali ba, a qalla ka tuna wani yana can kila ya fika komi a wajen Allah amma yana dauke da ciwon da shima yasan tamkar an samasa EXPIRY DATE ne.

✍🏻
Ibrahim Y. Yusuf

Ruwan Sama Da Iska Mai Karfi Sun Kwarfe Fitilun T**i A Kano, Bayan Kwana Hudu Da Kaddamar Da SuDaga Saifullahi Lawal Ima...
18/05/2026

Ruwan Sama Da Iska Mai Karfi Sun Kwarfe Fitilun T**i A Kano, Bayan Kwana Hudu Da Kaddamar Da Su

Daga Saifullahi Lawal Imam

Wani ruwan sama tare da iska mai karfi sun kwarfe fitilun t**i da dama a kananan hukumomin Takai da Sumaila dake jihar Kano, kwanaki hudu kacal da kaddamar da su.

Lamarin wanda ya girgiza al’umma ya faru ne yayin da ake cigaba da samun ruwan sama tare da iska mai ƙarfi a wasu sassan jihar Kano, inda sabbin fitilun t**in da aka girka s**a kasa jurewa ƙarfin iskar, lamarin da yasa da dama daga cikin sandunan fitilun s**a fadi kasa a tsakiyar hanya da T**i.

Rahotanni daga mazauna yankunan sun bayyana cewa fitilun t**in da aka kaddamar domin inganta hasken hanya da sauƙaƙa zirga-zirga sun lalace cikin kankanin lokaci, abin da ya janyo ce-ce-ku-ce da tambayoyi daga jama’a kan ingancin aikin da aka gudanar.

Wani mazaunin yankin Takai ya bayyana cewa “Abin takaici ne a ce cikin kwanaki hudu kacal da kaddamar da aikin, yanzu fitilu sun ruguje saboda iska. Wannan yana nuna akwai bukatar bincike akan ingancin aikin.”

Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin basu fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da faruwar lamarin ba.

Al’umma da dama sun bukaci mahukunta da masu ruwa da tsaki su gudanar da bincike tare da tabbatar da ingantaccen aiki a duk wasu ayyukan more rayuwa da ake gudanarwa domin kaucewa asarar dukiyar gwamnati da kuma kare rayuka.

Daga Gaza… Labari mai girgiza zuciya 💔 An gano gawar wani bawan Allah… gawar da ta shafe kwanaki a ƙarƙashin ƙasa, cike ...
26/04/2026

Daga Gaza… Labari mai girgiza zuciya 💔

An gano gawar wani bawan Allah… gawar da ta shafe kwanaki a ƙarƙashin ƙasa, cike da alamomin tsananin wahala.

Ya ji rauni ne yayin ƙarshe na fitar da jama’a daga arewacin Gaza… sannan ya kwashe kwanaki uku yana zubar da jini shi kaɗai, babu taimako, babu kowa a kusa da shi… 😢

Da ya fahimci cewa babu sauran mafita, sai ya tattara ƙarfin da ya rage masa… ya kwanta cikin sujada, ya miƙa rayuwarsa ga Ubangijinsa 🤲
💔 Abin da ya fi taba zuciya: An same shi a wannan yanayi na sujada… kusa da wata bishiya 🌳

Ya ma bar alama ga iyalansa ya ɗaure zobensa da zare a jikin reshe 💍
Kamar yana cewa, Idan kuka neme ni… nan zan kasance.

A yau, bayan Sallar Juma’a, an yi masa jana’iza cikin hawaye da alhini… 🕋

🤲 Allah Ya yi rahama ga dukkan shahidan Musulunci

🤍 Allah Ya ba iyalansu haƙuri da juriya

📢 Ku yada labarinsu… kada a manta da su.

📌 Marayu da iyalan shahidai amana ne a wuyanmu — kada mu barsu su kaɗai.
Allah ne mafi taimako. ☝🏻

AMURKA TAJI GARGADIN DA CHINA TAYI MATA...Jiya an jiyo Ministan tsaron China Admiral D**g Jun yana gargadar Amurka akan ...
14/04/2026

AMURKA TAJI GARGADIN DA CHINA TAYI MATA...

Jiya an jiyo Ministan tsaron China Admiral D**g Jun yana gargadar Amurka akan ko da wasa kar suyi kuskuren cewa zasu dakatar da jiragen ruwam China masu jigilar danyen man fetur da zasu wuce ta mashigar Hormuz bayan da s**a dauko fetur daga Iran...

A safiyar yau agogon Iran an hango katoton jirgin ruwan China maisuna The Rich Starry dauke da danyen man fetur sama da ganga miliyan biyu ya shige ta inda sojojin Amurka s**a sanya gate amma ba abun da sojojin na Amurka s**a yiwa jirgin China...

Ta tabbata Amurka taji gargadin da China tayi mata a jiya ....

To Madallah hakan Normal ne, duk wani abun da zai kunyata Amurka dadinsa muke ji...

Address

Zamfara
Bungudu

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Suzai Hausa Newspaper posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share