12/05/2026
2027: INEC za ta ɗauki masu yiwa ƙasa hidima na shirin NYSC Miliyan 1.4 su yi aikin zaɓe
Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, ya bayyana cewa hukumar za ta tura mambobin yi wa kasa hidima na NYSC miliyan 1.4 domin gudanar da babban zaben shekarar 2027.
Farfesa Amupitan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa Darakta Janar na Hukumar NYSC, Birgediya Janar Olakunle Nafiu, a Abuja.
Ya ce domin zabukan gwamnonin jihohin Ekiti da Osun, da kuma zabukan cike gurbi a jihohin Nasarawa, Enugu, Rivers, Ondo, Kebbi da Kano, za a dauki kusan mambobin NYSC dubu 53 aiki.
Shugaban na INEC ya kuma yi alkawarin samar da ingantacciyar walwala tare da horaswa mai kyau ga mambobin NYSC yayin da ake tunkarar zabukan.
A nasa bangaren, Darakta Janar na NYSC ya yaba da hadin gwiwar da ke tsakanin hukumomin biyu, tare da tabbatar da cewa za su tabbatar mambobin NYSC sun kasance ba su nuna goyon bayan wata jam’iyya ba yayin gudanar da zabukan.