05/08/2026
Yadda Salatin Annabi (SAW) ya zama sanadin biyan bashin wani da ake shirin ɗaurewa Labari mai ban al'ajabi daga Kano.
Salatin Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) na yaye baƙin ciki da damuwa, kuma Allah yana sanya mafita ga masu yawaita yin sa.
An taɓa samun wani bawan Allah da ake bin sa bashi. Alƙali ya shaida masa cewa idan ranar shari'a ta yi bai biya bashin ba, za a ɗaure shi, domin yana ganin kamar da gangan yake ƙin biya.
Da ranar ta zo, sai ga mutumin ya bayyana da kuɗin bashin cif, sababbi ƙal. Lokacin kuwa zamanin kuɗin Murtala ne, waɗanda a wancan lokaci manyan kuɗi ne.
Alƙali ya tambaye shi:
"Yaya aka yi ka samu wannan kuɗin?"
Mutumin bai ce komai ba, sai Alƙali ya ce:
"Malam, ka ba mu labarin yadda abin ya faru."
Sai mutumin ya ce:
"Salatin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) na riƙa yi. Daga bisani na ga Annabi (SAW) a mafarki, ya ambaci sunan wata unguwa, sannan ya ce in je wani takamaiman gida. Ya ce zan samu wanda zai ba ni kuɗin."
Ya ci gaba da cewa:
"Da safe na tafi daidai wurin. Ina isa sai na ga wani mutum tsaye, yana kallona. Da ya gan ni sai ya ce, 'Yauwa, ka ƙaraso.' Nan take ya miƙa mini kuɗin a cikin kwali cif, bai ƙara cewa komai ba, sai ya juya ya tafi."
Da jin wannan labari, Alƙali ya ce cikin raha:
"To Malam, ai sai ka ba ni wani abu daga cikin kuɗin nan, ni ma in sami albarka."
Wannan Alƙalin da abin ya faru a gabansa shi ne da kansa ya ba ni wannan labari. Har ma ya ambaci sunan unguwar da abin ya faru a cikin birnin Kano. Idan na faɗi sunan Alƙalin da kuma unguwar, mutane da yawa za su san su.