16/07/2026
Gwamna Buni ya bukaci al'ummar Masarautar Ngazargamu su haɗa kai domin ci gaban masarautar
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni (CON, COMN), ya yi kira ga al'ummar Masarautar Ngazargamu da su zauna cikin zaman lafiya da haɗin kai tare da bai wa sabon Sarkin Ngazargamu, Alhaji Mahmud Ibn Mustapha, cikakken goyon baya domin samun nasarar jagorancinsa da kuma ci gaban masarautar baki ɗaya.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yau yayin da sabon Sarkin Ngazargamu tare da wakilan masarautar s**a kai masa ziyarar godiya a Fadar Gwamnati.
Ya jaddada cewa zaman lafiya da haɗin kai su ne ginshiƙan ci gaba, yana mai cewa ba za a iya samun ci gaba mai ɗorewa ba sai an tabbatar da zaman lafiya tsakanin al'umma.
Gwamna Buni ya ce Masarautar Ngazargamu ta yi fice wajen kasuwanci da kuma ilimin addinin Musulunci, yana mai ƙarfafa al'ummar yankin da su ci gaba da kare wannan kyakkyawan tarihi tare da ƙara bunƙasa shi domin amfanin al'umma.
A nasa jawabin, Wazirin Ngazargamu, Alhaji Baba Kankare, wanda ya yi magana a madadin masarautar, ya gode wa Gwamna Buni bisa amincewa da zaɓin da al'ummar masarautar s**a yi na naɗa Alhaji Mahmud Ibn Mustapha a matsayin sabon Sarkin Ngazargamu.
Ya ce matakin da gwamnan ya ɗauka ya nuna girmamawa ga ra'ayin al'umma, tare da bayyana matuƙar godiya ga gwamnatin jihar bisa wannan goyon baya.