Adam ibn Muhammad

Adam ibn Muhammad 1,Dalibin ilimi📚
2, Ni musulmi🕋
3, Shi'a sak.??✍️
4, bidi'a sam.??✊
5, Al'majirin sheak zakzaky✌️

A HEARTFELT COMPLAINT FROM STUDENTS OF Yobe State UniversityI am one of the students who were denied the opportunity to ...
20/05/2026

A HEARTFELT COMPLAINT FROM STUDENTS OF Yobe State University

I am one of the students who were denied the opportunity to sit for the Electrochemistry examination at Yobe State University, and this situation has deeply affected many of us emotionally and academically.

It is truly heartbreaking to witness how some lecturers in the Chemistry Department continue to treat students unfairly, as though the future and struggles of students no longer matter.

Most of the affected students are not fresh cases. Some are spill-over students for one session, others for two sessions, while some have spent even more years trying to complete their studies. A number of students struggled before their registration portals were eventually opened, yet after completing registration, they were still denied access to the examination simply because of attendance issues.

Honestly, this is unfair and unacceptable.

How can students be blamed for delayed registration processes?
How can students suffer for failures within the school system itself?

What hurts the most is the growing belief that certain lecturers seem more interested in frustrating students until they eventually give up on their education after spending seven to eight difficult years investing their time, energy, and their parents’ hard-earned money in pursuit of knowledge.

This is not discipline.
This is not proper education.
This is outright injustice.

We are calling on every individual who values education, student rights, and the future of young people to help amplify this message so it can reach the appropriate authorities.

Students deserve fairness, understanding, and justice — not intimidation or oppression.

A student is not a slave.
We are only demanding justice, not a favor.

Wasu mutane duk abin da basu fahimta ba sai su juya shi zuwa abin dariya da izgili. Wai saboda an ambaci consensus sai a...
16/05/2026

Wasu mutane duk abin da basu fahimta ba sai su juya shi zuwa abin dariya da izgili. Wai saboda an ambaci consensus sai ace “kwarfensu”? Wannan tunani ne na siyasar hayaniya ba siyasar hankali ba.

Consensus ba tsoro ba ne, hanya ce ta nuna kishin jam’iyya da neman haɗin kai domin a kauce wa rikicin cikin gida. Mutum mai hangen nesa baya kallon siyasa da ido na “ni kaɗai”, yana kallon zaman lafiyar jam’iyya da cigaban al’umma gaba ɗaya.

Sanata Ibrahim Mohammed Bomai ya fito karara ya ce yana nan ɗan takara, amma idan jam’iyya ta fitar da wani ta hanyar consensus zai mara masa baya. Wannan magana ce ta balaga da mutunci, ba maganar rauni ba. Domin mutum mai kishin jam’iyya baya rusa gida saboda son kansa.

Maganar gaskiya, wasu sun saba da siyasar hayaniya da zage-zage har suke ganin duk inda aka ga nutsuwa to akwai tsoro. A’a, siyasa ta gaskiya tana buƙatar haƙuri, hikima da haɗa kai. Ba dole sai an yi cacar baki ko rikici ba kafin a nuna ƙarfin siyasa.

Allah ya zaɓa mana shugaba mafi alkhairi wanda zai yi wa jama’a aiki da gaskiya. Amma a daina mayar da tattaunawar siyasa zuwa raini da izgili, domin mutunci da kishin al’umma sun fi hayaniya daraja.

Gaskiya Game da Iran da Siyasar Munafunci ta Kasashen YammaYunkurin da ake yi a baya-bayan nan na amfani da tsoratarwa d...
15/05/2026

Gaskiya Game da Iran da Siyasar Munafunci ta Kasashen Yamma

Yunkurin da ake yi a baya-bayan nan na amfani da tsoratarwa da yada jita-jitar wai akwai wata “fahimta ta musamman” tsakanin Amurka da China domin takurawa Iran, ba komai ba ne face tsohuwar dabarar siyasa ta Donald Trump wajen ɓoye gazawa da nuna ƙarfin da babu shi a zahiri. Lokaci ya yi da za a kalli gaskiyar lamari cikin idon basira.

1. Hakkin Iran na Fasahar Nukiliya ta Zaman Lafiya

Iran ta dade tana bayyana cewa shirinta na nukiliya na zaman lafiya ne, domin amfani da shi wajen samar da lantarki, binciken kimiyya da kuma harkokin lafiya — abubuwan da dokokin ƙasa da ƙasa s**a amince kowace ƙasa ta mallaka.

Saboda haka, kalaman Trump na cewa “ba za a bari Iran ta mallaki makamin nukiliya ba” ba sabon abu ba ne. Wannan tsohuwar magana ce da aka saba ji daga mahukuntan Amurka domin tsoratarwa da kuma hana ƙasashe masu cin gashin kansu bunƙasa cikin ’yanci.

2. Mafarkin Amurka da Hakikanin Matsayin China

Abin dariya ne a yi tunanin cewa China za ta sadaukar da dangantakarta ta tattalin arziki da tsaro da Iran saboda muradun Amurka. China na daga cikin manyan ƙasashen da s**a dogara da mak**ashin Iran, kuma ta sha bayyana adawarta ga takunkuman bangare guda da Amurka ke kakabawa sauran ƙasashe.

Don haka, ikirarin Trump na cewa akwai “kusancin fahimta” tsakaninsa da Xi Jinping kan Iran ya fi k**a da wasan siyasa domin nuna cewa yana da goyon baya. A zahiri kuwa, China na ci gaba da kare muradunta da kuma hulɗarta da Iran a yankin Gabas ta Tsakiya.

3. Mashigar Hormuz da Ƙarfin Iran

Mashigar Hormuz na ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin safarar mai a duniya, kuma Iran ta nuna cewa tana da ikon kare yankinta da muradunta idan aka matsa mata.

Idan duniya na son kaucewa rikicin tattalin arziki da tashin farashin mak**ashi, mafita ita ce mutunta yarjejeniyoyin ƙasa da ƙasa da kuma daina siyasar matsin lamba, ba ci gaba da nuna ƙarfin iko da barazana ba.

Kammalawa

Duniya ta wuce zamanin da ƙasa guda za ta dinga juya akalar sauran ƙasashe ta hanyar tsoratarwa da takunkumi. Iran ta nuna juriya, ƙarfin guiwa da kuma samun kawaye masu tsayawa tare da ita.

Siyasar matsin lamba ta Trump ta gaza a baya, kuma alamu na nuna cewa za ta sake gazawa. Lokaci ya yi da za a daina yaudarar jama’a da hotunan bogi na haɗin kai tsakanin Amurka da China domin takurawa Iran.



Muddin har Isa Ali Pantami yana da wannan buri na gaskiya a zuciyarsa, kuma abinda yake fada daga zuciya yake yi domin c...
14/05/2026

Muddin har Isa Ali Pantami yana da wannan buri na gaskiya a zuciyarsa, kuma abinda yake fada daga zuciya yake yi domin ci gaban al’umma, to babu shakka zai iya kawo babban gyara a jihar Gombe.

Malam Pantami shugaba ne mai hangen nesa, ilimi, kwarewa da kuma gogewar shugabanci. Ba irin ‘yan siyasar da kawai maganar kamfe s**a sani ba ne, illa mutum mai manufa da kishin jama’a.

Leadership quality da experience suna da matukar muhimmanci wajen cigaban kasa da al’umma. Idan aka baiwa nagari dama, tabbas za a ga canji mai amfani ga talakawa da matasa.

Allah Ya kawo mana shugabanni nagari masu tsoron Allah da kishin jama’a.

JAGORAN MATASA ✊

Da zafinta🔥🔥🔥🔥🔥“Fantami dai sai ya tsaya ya kalla. Ashe duk abin da ake ta surutu akai, malamai ne gaba ɗaya — bambanci ...
07/05/2026

Da zafinta🔥🔥🔥🔥🔥

“Fantami dai sai ya tsaya ya kalla. Ashe duk abin da ake ta surutu akai, malamai ne gaba ɗaya — bambanci kawai ɗaya yana Tijjaniyya, ɗaya kuma Izala. Amma abin da ya fi muhimmanci shi ne gaskiya da riƙon amana. Domin mutum mai harshe biyu ko a kasuwa ba a yarda da shi, b***e a harkar siyasa.

Mu kuwa muna nan daram a kan tafarkin Shehi da nasiharsa. Insha Allahu, gidan gwamnatin Gombe zai karɓi Maulidi, Wazifa da Hailala cikin farin ciki da haɗin kai. Wannan ba faɗa ba ne, wannan ayari ne na soyayya ga addini da malamai. Kuma a wannan fage, ayarin Shehu zai ci gaba da tafiya da izinin Allah.”
Adam ibn Muhammad

07/05/2026
An samu wani lamari mai tayar da hankali inda aka zargi wani matashi da ya yaudari wata yarinya ta hanyar amfani da kafa...
05/05/2026

An samu wani lamari mai tayar da hankali inda aka zargi wani matashi da ya yaudari wata yarinya ta hanyar amfani da kafafen sada zumunta.

Rahotanni sun nuna cewa matashin ya fara hulɗa da yarinyar ne da sunan soyayya tare da yi mata alkawarin aure. Daga bisani ya je ya same ta, inda aka ce ya yi anfani da wannan damar wajen lalata da ita.

Bayan wani lokaci, sai ya janye daga batun aure. Yarinyar kuma ta ci gaba da rayuwarta har ta samu wani wanda ya nuna niyyar aure.

Sai dai, ana zargin cewa tsohon saurayin ya fara yi mata barazana da wani bidiyo na sirri da s**a yi a baya, yana cewa zai wallafa idan ta cigaba da shirin aurenta.

Duk da haka, wanda zai aureta ya nuna fahimta tare da amincewa, muddin ba a watsa bidiyon ba.

Abin takaici, ana zargin cewa a daidai lokacin da ake dab da ɗaura aure, sai aka watsa bidiyon a kafafen sada zumunta, lamarin da ya jawo babbar illa ga rayuwar yarinyar.

A halin yanzu, ana ci gaba da tuntubar iyayen yarinyar domin ɗaukar matakin shari’a akan wanda ake zargi.



MUHIMMAN SAKON DA YA KAMATA A FAHIMTA
• Yaudara da amfani da bidiyo wajen barazana babban laifi ne.
• Watsa bidiyon sirri ba tare da izini ba (revenge p**n) haramun ne kuma laifi ne a doka.
• Bai dace a dora laifi gaba ɗaya kan yarinya ba—ya k**ata a duba gaskiya da adalci.

A halin yanzu ana yawan magana kan wani bidiyo da ya yaɗu a kafafen sada zumunta. Duk da haka, har yanzu ba a samu sahih...
05/05/2026

A halin yanzu ana yawan magana kan wani bidiyo da ya yaɗu a kafafen sada zumunta. Duk da haka, har yanzu ba a samu sahihin bayani da ke tabbatar da ainihin dalilin fitar da bidiyon ba, ko kuma cikakken bayani kan mutanen da ke ciki.

Bincike ya nuna cewa hotuna ko bidiyo a irin wannan yanayi na iya zama an gyara su ko kuma an fitar da su ba tare da cikakken bayani ba, wanda hakan ke iya jawo ruɗani da yanke hukunci ba bisa gaskiya ba. Haka kuma, ba daidai ba ne a bayyana sunaye ko zargin wasu mutane ba tare da hujjoji masu ƙarfi ba.

Saboda haka, ana kira ga jama’a da su:
• Guji yaɗa jita-jita
• Tabbatar da sahihancin labari kafin rabawa
• Mutunta martaba da sirrin mutane

Ana jiran karin bayani daga sahihan tushe domin tabbatar da gaskiya da adalci.

Allah yakara mah malam lapia da nisan kwana
04/05/2026

Allah yakara mah malam lapia da nisan kwana

LABARI NA GAGGAWA 🚨Rahotanni sun nuna cewa kwamandan rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC), wato Ahmad Vahid...
02/05/2026

LABARI NA GAGGAWA 🚨

Rahotanni sun nuna cewa kwamandan rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC), wato Ahmad Vahidi, ya amince da wani babban shiri na gaggawa idan aka sake barkewar rikici.

A cewar waɗannan rahotanni, cikin awanni 24 na farko, ana iya harba kusan mak**ai masu linzami (missiles) 1,000 tare da jirage marasa matuƙi (drones) har 3,000.

Ra’ayina: A ganina, akwai kusan kashi 30% na yiwuwar United States ta sake shiga wannan yaƙi.

Amman koma me zan kawo maku labari kan hakan Insha Allah
Adam ibn Muhammad✍️✍️

02/05/2026

Al’ummar Jihar Yobe yak**ata mu farka mu gane cewa wasu mutane kullum burinsu shi ne su mayar da mulkin jiharmu mai albarka k**ar gadonsu. Amma yanzu Yobe ta fara fita daga jahilci, mutane sun fara wayewa.

Abin takaici, akwai wanda yake zaune a daki yana son ya dinga ba mu umarni, k**ar shi ne yake da ikon zabar mana shugabanci. A lokacin mulkinsa, banda raba kan al’umma, babu wani abin a zo a gani da ya kawo jin dadin talaka.

Gaskiya ne, mu tambayi kanmu: shin akwai wani babban aiki guda daya da ya yi a lokacin da yake sanata da za a iya nunawa a fili?

Address

Damaturu
620001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adam ibn Muhammad posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share