12/08/2026
TUNAWA DA WAFATIN MANZON ALLAH (S.A.W.A.) A DA'IRAR DANJA
Danja — 12 ga Agusta, 2026
A ranar Laraba, 12 ga Agusta, 2026, al’ummar Musulmi Ali majiran Sayyid zakzaky H na garin Danja sun gudanar da zaman juyayin na musamman domin tunawa da wafatin Manzon Allah Muhammad (S.A.W.A.), tare da tuno irin bakin cikin da iyalan gidansa s**a shiga a lokacin da rashin lafiyarsa ta tsananta har zuwa fitar ransa.
An gudanar da zaman juyayin ne daga ƙarfe 3:00 na rana zuwa 8:30pm na dare, bayan kammala sallar La’asar, inda mahalarta s**a hallara domin sauraron jawabi da darussa kan kwanakin ƙarshe na rayuwar Manzon Allah (S.A.W.A.) da kuma abubuwan da s**a biyo bayan wafatinsa.
Anfara ne da azah mai ratsa zukuta wanda matasa s**a jagoranta bayan nan sai ziyarar Annabi (SAWW) daganan kuma sai jawabin Malama Maryam Tukur bayan takammala sai jawabin jagora (H)
A cikin jawabinsa, ya mayar da hankali ne kan irin tsananin bakin ciki da Imam Ali (A.S.), Sayyida Fatima al-Zahra (S.A.), da sauran Ahlul Baiti (A.S.) s**a shiga yayin da rashin lafiyar Manzon Allah (S.A.W.A.) ke tsananta.
Ya bayyana yadda wannan lokaci ya kasance mai matuƙar raɗaɗi ga iyalan Annabi (S.A.W.A.), musamman ganin cewa suna fuskantar rabuwa da wanda shi ne jagora, uba, kuma Manzon Allah da s**a fi so.
Haka kuma, an saurari jawabin kan wasiyyar da Manzon Allah (S.A.W.A.) ya bari ga Imam Ali (A.S.), da irin nauyin da ya rataya a kansa bayan wafatin Manzon Allah (S.A.W.A.).
Bayan wafatin Manzon Allah (S.A.W.A.), ya yi bayani kan yadda Imam Ali (A.S.) ya kasance cikin waɗanda s**a jagoranci jana’izar Manzon Allah, ciki har da wanke shi,sa likkafani, gudanar da sallarsa da kuma binne shi.
Ya kuma nuna yadda wannan lokaci ya kasance ɗaya daga cikin mafi girman lokutan baƙin ciki a tarihin Ahlul Baiti (A.S.), domin rasuwar Manzon Allah (S.A.W.A.) ta kasance babban rashi ga al’ummar Musulmi baki ɗaya.
An saurari jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) ne, wanda aka gabatar a matsayin babban darasin da ya ƙara haskaka abubuwan da s**a shafi kwanakin ƙarshe na rayuwar Manzon Allah (S.A.W.A.), dangantakarsa da Ahlul Baiti (A.S.), da kuma abubuwan da s**a faru bayan wafatinsa.
Jawabin ya kasance mai jan hankali, inda aka tunatar da mahalarta cewa tunawa da wafatin Manzon Allah (S.A.W.A.) ba wai kawai tunawa da wani tarihi ba ne, a'a, dama ce ta komawa ga koyarwarsa da kuma fahimtar matsayin Ahlul Baiti (A.S.) da rawar da s**a taka wajen kare saƙon Musulunci.
Zaman juyayin ya kasance cike da yanayin alhini da tunani, inda mahalarta s**a nuna girmamawa da juyayi ga Manzon Allah (S.A.W.A.) tare da tunawa da irin musibar da ta sami iyalansa bayan wafatinsa.
An kammala taron da addu’a ga Manzon Allah (S.A.W.A.), Ahlul Baiti (A.S.), da kuma addu’ar Allah Ya ƙara haɗa kan al’ummar Musulmi, Ya ba su ikon bin tafarkin ManzonSa da riƙe da koyarwarsa.
# JawadmediaDanja — 12/08/2026