Da'irar Danmaigauta

Da'irar Danmaigauta Domin yadda abubuwan da s**a shafi addini, da'irar Danmaigauta, da Harkar muslumci a Nigeria.

29/10/2025
Tunatarwa:“Ni abinda ke bani takaici shi ne, wasu ana ta ce musu, abinda ya k**ata kar ku yi komai (na fuskantar azzalum...
17/10/2025

Tunatarwa:

“Ni abinda ke bani takaici shi ne, wasu ana ta ce musu, abinda ya k**ata kar ku yi komai (na fuskantar azzalumai), ku hada kai da hukumominku ne, ku yaɗa Shi'a. Wannan da'awar har wasu na sayen shi. Cewa, ku hada kai da hukumomi ku yaɗa Shi'a kawai.

“To, na ji, ana iya hada kai da hukuma. Amma ba kai za ka je wajen hukuma, ka ce, ya ke hukuma, ina son in hada kai da ke ba. Baka da matsayi kenan. Idan ita Hukumar ta ga cewa kana da matsayi, sai ta zo wajenka, tace ita tana neman haɗin kanka. Ko ba a lura ba? Sai ka ce, to amma da sharadi, za a yi kaza, za a yi kaza. Ka ga a nan kai kake da ta cewa. Amma ba ya zama su ne za su ganka a matsayin mare daraja kawai ka zo wajensu neman wani abu ne ba.

“Ka nuna musu baka bukatarsu sam, su ke da bukatar ka. Kaga kai za ka gaya musu sharudda. In aka kai ga wannan marhalan, to an samu cigaba. Amma a marhalan da suke ganin ku wadansu ababe ne da za su kawar, za su share ku ne su huta, to a wannan lokacin ku za ku dake ne (ku fuskance su da gwagwarmaya).

“Kun ga in mutum ya duba tarihin da'awar Manzon Rahma (S), a Makkah su Ƙuraishawa suna ganin za su murƙushe shi ne, kawai a murƙushe a daina da'awar sam-sam. Da abin ya yi ƙamari, sai s**a yi tunanin a yi kisa kawai. Musamman ma lokacin da ya rasa masu kare shi; ya rasa Abudalib (AS) babban mai kare shi. Da ya rasa Khadija (SA), sai s**a ce yauwa dama da dukiyarta yake tak**a da ita, yanzu babu ita. Sun yi biki sun sha giya sanadiyar rasuwar Khadija. Sannan kuma da Abudalib ya rasu s**a ce to ƙarshe ya zo, yanzu ba abinda zai hana mu kashe shi. Sai s**a shirya kashe shi. Sai Allah Ya kwace shi, ya yi Hijira.

“Sai s**a bi shi da yaki, aka yi karon Badar, s**a ji ba daɗi, s**a je Uhud za su yi ramakon gayya, sun yi barna, amma dai sun koma da tsoro. Da aka zo, Manzon Allah (S) zai shiga (Makkah) ya yi Umra, s**a ce ba su yarda ba, sai aka yi yarjejeniyar Hudaibiyya. Yarjejeniyar Hudaibiyya ya nuna cewa yanzu sun dauki (Annabi (S) a matsayin shi a karan-kansa ƙarfi ne daidai da su. Yanzu suna ganinsa a matsayin 'entity' na ƙashin-kansa, da kuwa suna ganinsa a matsayin yana ƙarƙashinsu ne, za su muttsike shi. Yanzu kuwa ya zama shi ma a matsayin daban yake, su daban suke, ana yarjejeniya ne a tsakani. Ko ba ku lura da wannan cigaban ba?

“To karshe kuma, da s**a karya yarjejeniyar, sai gashi sun zo su suke neman ko zai yiwu a yi kaza? Aka ce ai ina, tunda kun karya, dole kawai za a yake ku ne. Aka zo aka bi su, aka ritsa da su, s**a fito s**a daura hannuwansu a ƙeya, suna jiran za a fille musu wuya. Sai aka musu tagomashi, aka ce ku tafi. 'Izhabuu wa antum ɗulaqa'. To ka ga izza kenan.

“In kun lura marhala-marhala ne; tun ana tunanin za a muttsike, aka zo aka ce, yanzu mun yi daidai wadaidai (kunnen doki) muke, yanzu kuma muna karkashinku ne. Ko ba ku lura ba? Da za mu muttsike ku, muka zo muka yi kunnen doki da ku, yanzu kuma ku ne a sama, mu a ƙasa, yanzu mun bi. To haka nan marhalan ya k**ata ya zama.

“Yanzu marhalan da muke ciki a nan kasar me (me azzaluman mahukunta) suke tunani? Ku gaya min. Za su muttsike mu ne, su huta. Sun yi, sun yi, sun yi, ba mu muttsiku ba. To, mun san kuma mu ba masu muttsikuwa ba ne! Murƙushe mu ba zai taba yiwuwa ba! Kuma ana nan, sai sun ce, to yanzu mun zama kunnen doki. Muke yauwa. Ana nan za ku zo ku ce, to mun bi. Dole ne! Wannan k**ar ya auku ne insha Allah. Amma wannan zai zama sak**akon dakewa ne.”

— Ɓangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ga daliban Hauzozin Ilmi daga ƙasashe daban-daban a gidansa da ke Abuja, ranar Talata 20 ga Jimadal Thani 1447 (14/10/2025).







17/10/2025

DALIBAN HAUZAH ILMIYYA SUN ZIYARCI JAGORA (H)Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)‘Yan uwa daliban Hauzah Ilmiyyah, d...
15/10/2025

DALIBAN HAUZAH ILMIYYA SUN ZIYARCI JAGORA (H)

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

‘Yan uwa daliban Hauzah Ilmiyyah, daga kasashen Iran, Iraq, Lebanon, Nijar da Mali sun gana da Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a gidansa da ke Abuja, a yammacin Litini, 20 ga Rabi’ul Thani, 1447 (14/10/2025).

Da yake jawabi ga maziyartan, Jagoran ya bayyana manufar ganawar, inda ya ce, don a tunatar da juna ne akan muhimmancin abinda s**a saka a gaba, ta yadda su kansu za su daura damara su dauki karatun da muhimmanci. “Ku san cewa kuna yin wannan (karatun) ne a matsayin sadaukarwa a madadin dukkanin al’umma.”

Jagora ya tunatar da su muhimmancin tsayuwa da karantar da mutane ilimi, ba kawai wa’azi irin yadda yanzu ake yayin masu wa’azi daban-daban a kasar nan suna yi a sigar hayaniya ba. Yace: “A zauna a yi karatu, a dauko littafi daga bango zuwa bango a karanta kowace kalma sanka-sanka a bi ta da bayani a wuce a sauke, sannan a dauko wani a sake sawa daga bango zuwa bango.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana musu cewa, yana da kyau yin ma mutanen gari wa’azi. “Wa’azin da zai iya hada kan al’umma da fahimtar al’umma Musulmi a matsayin abu guda, wannan yana da kyau, ba wanda zai rarraba su ba.” Ya jaddada cewa: “ Amma karantarwa shi ne ‘ahammus shay’i.”

Jagoya ya ce, mutum ba zai karantar da ilimi ba, har sai in ya yi karatu, shi kuma karatun ana sadaukarwa ne a dauki lokaci a yi shi. Inda ya bukaci da su zama misalin kendir, wanda yake kona kansa don ya haska waje. “Abinda ya k**ata ma’abota karatu su kasance kenan, su kona kansu don wasu su samu hasken ilimi.”

Ya kuma jaddada musu hadafin karatun a matsayin karatu don a karantar, inda ya ba da misali da yadda Malaman Zaure a kasar Hausa kan sadaukar su yi karatu mai zurfi don su karantar da sauran al’umma.

Jagora ya gargadi daliban ilimin akan tsayawa kyam akan tafarkin addini, ba tare da karkata ga azzalumai ba. Ya ce: “Abinda (wasu) suke ta kokarin su nuna mana shi ne, a zauna lafiya da hukuma. Mu ba mu ce ba za mu zauna lafiya da hukuma ba, amma a wane unwanin? A unwanin muna yaransu? Haihata! Haihata minnaz zilla! Haihata!”

Ya bayyana cewa, amma idan zama lafiya da su din a muna matsayin daidai da su ne, suna ganin mu ma ‘entity’ ne, suna bukatarmu, har suna neman abu a wajenmu, to Masha Allah, ka ga cigaba ne wannan. “Amma ka je a wulakance, k**ar masu zuwa rarakan nan, har da cewa wai su ba a san da su ba, ba a yi da su, alhali suna da yawa suna da kaza, amma ba a wakiltansu…. To kaskanci ne wannan.”

Shaikh Zakzaky ya ce, abinda yanzu ake ta kitsa ma mutane kenan, su zauna lafiya da azzalumai. “Ban ki ba, idan mutum ya ga shi yanzu ba zai iya tsayawa kyam ya yi gwagwarmaya ba, ya koma waje daya ya ce koyarwa zan yi. Ba zan zarge shi ba.”

Ya ce: “Amma ya koyar din ne kawai, kada ya bude bakinsa ya ce masu gwagwarmaya laifi suke yi. Tunda shi ba zai iya ba, ya ja bakinsa ya tsuke, ya shiga lungu ya koyar. Ba zai iya wannan ba? To ya yi wannan din, amma kar ya zo ya ce, wadannan da suke wannan abin su bari.”

Ya kara da cewa: “Kowa ya yi nasa. Sadaukarwa ne, in ba za ka sadaukar ba, wani zai yi. An fahimta ai.”

Jagora ya ce, masu ganin cewa zama da mahukunta lafiya shi ne ‘aula’. Sai in ce, da haka nan ne, da Imam Husaini (AS) ya zauna lafiya da Yazidu, da ba a cire masa kai ba. Kuma na san ba za ka fi shi ganin maslahar al’ummar nan ba. Yace: “Yanzu irin wannan da’awar, su suna ganin k**ar mu ne muke jefa kanmu a cikin wahala, mu muka ja ma kanmu.”

Don haka ya jaddada kira ga daliban ilimin akan lallai su san hadafin da ya kai su karatun. Wanda yace, hakan muhimmin abu ne. Ya yi musu nasiha akan su tsayu da karban karatu ne daga Malaman da suke karatu a wajajensu, amma su bar musu Fikirorinsu matukar ba ya dace da Fikirar da suke kai ne ba. “Da yake akwai masu Tunani daban daban a Hauzozi, a yi karatun kawai. Luga ne, ya iya Luga, ya koya maka Luga. Fiqihu ne ya iya, ya koyar. Usul ne ya iya, ya koyar. Amma ra’ayinka daban nasa daban, ya rike ra’ayinsa ka rike naka. Allahumma sai dai in ra’ayin naku iri daya ne, amma ba ka je ne a canza maka tunani ba. Yana da muhimmanci ka san diban karatun za ka yi don ka amfana, wani ya amfana da kai.” Ya jaddada.





14/10/2025

Shahid Ahmad! Muna tunawa da kai a yau 13 ga watan Oktoba wadda ta yi daidai da ranar haihuwarka a shekara ta 1990. Yau ...
13/10/2025

Shahid Ahmad! Muna tunawa da kai a yau 13 ga watan Oktoba wadda ta yi daidai da ranar haihuwarka a shekara ta 1990. Yau shekara 35 (ƙidayar shamsiyya) ke nan cur da haihuwarka. Duk da cewa ka bar mu da gangan jikinka shekaru goma sha ɗaya da s**a gabata, mun san cewa, kai da ƴan'uwanka, kuna nan rayayyu a wajen Ubangijinku; kuna cin arzikin Sa.

Muna tunawa da ku kullum a zukatanmu da addu'o'inmu.

Muna roƙon Allah Ta'ala ya ba mu guzurin isowa inda ku ke.

Shahid Ahmad 13th October 1990 - 25th July 2014

JAGORA YA GANA DA WAKILAN 'MEDIA FORUM'Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) Da yammacin Asabar 11 ga Rabi'ul Thani, ...
04/10/2025

JAGORA YA GANA DA WAKILAN 'MEDIA FORUM'

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yammacin Asabar 11 ga Rabi'ul Thani, 1447 (4/10/2025) Jagora, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gana da wakilan bangaren 'Media Forum' na Harkar Musulunci a gidansa da ke Abuja.

A yayin ganawar, Jagora ya fara da bayani akan Media, da yadda ta riƙa bunƙasa, inda ya bayyana samuwar Social Media a matsayin cigaba a daidai wannan lokacin. Sai dai ya koka da yadda mutane ke amfani da shi ba bisa yadda ya dace ba, ta yadda ake ƙirƙira musu abin cecekuce su yi ta fama, maimakon su mai da hankali akan abin da ya fi amfani.

Shaikh Zakzaky ya ƙarfafi muhimmancin dawo da jaridar Turanci da ake da ita mai suna Pointer Express, wanda ya bayar da tarihin kafuwarta daga farko har zuwa lokacin da ta durkushe a karo na biyu. Ya kuma nuna muhimmancin karfafa isar da sako a shafukan sadarwa k**ar Website, da shafukan sada zumunta, k**ar Facebook, X (Twitter), Instagram da sauransu, musamman da yarukan Ingilishi, French da kuma in dama ya bayar har da Larabci da Farsi.

Jagora ya jaddada jan hankali akan yadda ya dace a rika yin raddi. Ya ce, in aka samu mutum ɗaya ya yi magana akan abu ya gamsar, to ya wadatar, ba sai kowa ya sa baki har a shagaltar da mu da wannan abin ba. Ya bayyana yadda wasu ke bude shafuka da sunan 'yan uwa su yi ta abinda bai k**ata ba. Ya ce, ya k**ata Media Forum su fahimci yadda za su magance shirin maƙiya.

Harwayau, ya bayyana dacewar Media Forum ta kwakkwafe 'yan uwa ta hanyar yin tsari, da irshadi zuwa ga abinda shi ne daidai. A nan ne ya yaba wa Tiktok Team, kan yadda suke isar da saƙo ta hanyar yayyanka jawabai suna ɗorawa a shafukan Tiktok, inda ya ja hankali akan a riƙa sanin daidai gaɓan magana, inda ya dace a fara, da inda za a datse magana a yayin yankowa.

Jagora (H) ya bayyana manufar Media Forum a matsayin samar da tsari mai kyau na isar da sako a cikin 'yan uwa na Harka Islamiyya, kuma saƙo ya isa zuwa ga al'umma. Inda ya lissafa wasu ayyuka daban-daban da ya dace Media Forum din su tsayu da shi.

A karshe, Jagora (H) ya ja hankali akan yin aiki saboda Allah. Ya ce, aiki tare ya gaji matsaloli, da kushe, da guna-guni. Yace: "Amma in kana yi saboda mutane ne sai ka fasa in ka ji s**a, in kuwa don Allah ka ke yi, sai ka cigaba da abinka.”

Bayan jawabin Jagora (H), an assasa kwamiti mai dauke da mutane takwas, a matsayin masu kula da lamarin Media Forum a matakin baiɗaya (Centrallly), inda s**a ayyana Ammar Muhammad Rajab a matsayin shugaban Kwamitin na Media Forum. An baiwa kwamitin dama, su tsara ayyuka, da ayyana masu gudanar da Lajanar ta Media Forum a bangarori daban-daban na sassan Harka gabaɗaya.






11/RabiuThani/1447
04/10/2025

Yau Lahadi 28/09/2025, Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya amshi baƙuncin Gidajan Malamai daga birnin Zazzau da s**a h...
29/09/2025

Yau Lahadi 28/09/2025, Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya amshi baƙuncin Gidajan Malamai daga birnin Zazzau da s**a haɗa gidan Kona, gidan sarkin Ladanai, gidan Sheikh AbdulQadir Banufe, gidan Alhazawa, gidan marigayi Sheikh Aliyu Mai Yasin wanda Sheikh Muhammad Zakir Shamsuddeen (Young Sheikh) ya wakilta, Gidan Limamin Zabi Gidan Limamin Dogarawa da kuma Malam Sunusi Mai Ashafa, da gidan Sheikh Ibraheem Kakaki.

Malaman sun jajantawa Jagora (H) bisa ga waƙi'ar buhari (L) na shahadar Almajirai da Ƴaƴansa, sannan sunyi Addo'ar Allah ya amshi shahadar su.

Jagora (H) ya yi masu ta'aziyyar wasu malaman da aka rasa ya roki Allah ta'ala ya gafarta masu, sannan ya aika da saƙon gaisuwa ga sauran ƴan'uwa da masoya.







28/09/2025

Tunatarwa“Kun ga lokacin Annabi aka samu irin wadannan mutanen, kuma aka tafi tare da su; masu raunin imani, da masu zuc...
27/09/2025

Tunatarwa

“Kun ga lokacin Annabi aka samu irin wadannan mutanen, kuma aka tafi tare da su; masu raunin imani, da masu zuciya da ƙaƙo, da kuma tsantsan munafukai, amma duk an yi tafiya da su. Har da Tabuka ma an je da su, don a Tabuka sun yi maganganu amma an tafi da su. To, tafiya ya gaji wannan kenan. Amma muhimmin abu shi ne ya zama akwai wasu masu Iklasi waɗanda yake da ba don su ba, ba abin da zai tabbata. To mu samun masu Iklasin ne ya dame mu. Don kwasan duuu din mutane wannan kar ya dameka, ko ba komai in abin ya yi ƙarfi ba wani duuu din da ba zai zo ba. Kuna tsammanin akwai wanda ba zai zo ba in abin ya zama ɗaukaka? Kowa zai zo.

“Amma lokacin da yake wahala ne, in ka ga wani ya zo yana ɗan abubuwa, yana irin na tatsuniyar kura ce, ‘daga baya da baya na ka tsaya, in na ji kaya-kaya in noƙe.’ Sai ya yi irin wannan, ranar Waqi’a a noƙe, in ba Waki’a a dawo. In aka ga alamar Waki’a a bace, in ta baje a dawo, ai ta cika baki.

“An samu irin wannan a lokacin Annabi (S) ai. ‘Fa’iza zahabal kaufu salaqukum bi alsinatin hidadin ashihhatan alal khair.’ (Ahzab: 19) Wato, idan tsoro ya tafi, sai su zo su yi felen-felen su dameku da feƙaƙƙen baki don kwadayin abin duniya. Idan kuwa tsoro ya yi tsanani za su yi burin (ina ma) suna ƙauye suna tambayar labarinku.

“Wannan ba ana faɗin abin da mai yiwuwa su yi bane, akwai wadanda s**a je ƙauye ne s**a maƙe, suna tambayar an kashe Annabi? An kashe shi? Su sun fella a guje sun yi ƙauye, amma kuma da aka tabbatar cewa komai lafiya lau sai s**a dawo fele-felen da baki suna cewa, haba! Ai rannan irin yadda s**a dafki Mushrikai Malam! Nan kuwa suna kauye a ɓoye. Amma suna cewa; ai in ka ga irin yaƙin da na yi rannan, habawa Malam. Ai dama mu ba gudu ba ja da baya! Domin neman abin duniya wanda ya haɗa da dukiya (ganima) da muƙami. Wasu suna ce ganima kawai, nace baya ga ganima har da matsayi. Suna son ace su ne manya.

“To, ba za a rasa wannan ba, amma mu abinda muke so ya zama kai ka zaɓa wa kanka wanne kake so. Kun san a karatunmu na Nahjul Balagha da ya wuce, kun san wani abu da Abdurrahman Bin Auf ya yi, kun ji yadda Miqdad bin Aus ya masa ko? Miqdad zai je gidan Imam Ali (AS) sai ya haɗu da Abdurrahman Bin Auf a hanya, sai ya k**a hannunsa ya riƙe, yace Abdurrahman, wannan abin da ka yi in saboda Allah ka yi, Allah ya ba ka ladan duniya da lahira. In kuma saboda duniya ka yi, Allah ya ba ka arziƙi mai yawa. Sai Abdurrahman yace, tsaya ka ji. Miqdad yace masa, ba ni buƙatar in ji komai. Sai ya yi gaba abinsa. Yace me za ka fada min? Wato bani buƙatar in saurare ka.

“Nace ai kuwa ya yi masa nasiha, tunda yace in don duniya ne Allah ya sa ya samu duniyar sosai, in kuma don Allah ne Allah Ya ba shi ladan duniya da lahira, in kuma don duniya ne ya bashi duniyar da yawa. To, ya masa mummunan addu’a ne? A’a. Da ace ya ce ne, in don duniya ne Allah ya raba ka da duniyar, sai ace ai ya masa mummunan addu’a. To sai yace, in don duniyar ne Allah ya ba shi ita sosai.

“Abin nufi, kai yanzu za ka zaɓawa kanka ne, kai ‘yan wanne ne? Kar ka damu da wane me ya zaɓawa kansa, kai ne za ka yi tunanin kai me za ka zaɓawa kanka? To, in ka zaɓawa kanka Lahira, irinka ne ake ganin dabi’a ta canza a wajenka. Domin wanda ke da 'ghaya' na Lahira, yake hanƙoron can, shi nan (duniya) bai cika damunsa ba, kuma ba za ka ga yana ƙorafi kan abubuwa ba.

“Amma lallai kam mun san akwai abubuwa da daman gaske, wadanda suke ana ta nasiha don a gyaggyaru, amma mun san ba za a gyaru duka ba. Kuma lallai ba muna neman kowane mutum lallai ya zama gyararre ba ne, amma dai in aka samu gyararru masu yawan gaske, ba sai kowa da kowa ba, amma masu yawan gaske, wani adadi da za mu iya cewa yanzu mun shirya, to za mu iya cewa Ok. Amma yanzu adadin da za mu ji cewa ‘it's ok’ ɗin ne ba mu da su.”

— Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin rufe Tadrib din 'yan uwa Mata (Sisters), a ranar 20/9/2015 a Fudiyya Islamic Center, Zaria.







26/09/2025

Shahid Ali Haidar! Muna tunawa da kai a yau 22 ga watan Satumba wadda ta yi daidai da ranar haihuwarka a shekara ta 1999...
22/09/2025

Shahid Ali Haidar! Muna tunawa da kai a yau 22 ga watan Satumba wadda ta yi daidai da ranar haihuwarka a shekara ta 1999. Yau shekara 26 ke nan cur da haihuwarka (a ƙidayar shamsiyya). Duk da cewa ka bar mu da gangan jikinka shekaru goma da s**a gabata, mun san cewa, kai da ƴan'uwanka, kuna nan rayayyu a wajen Ubangijinku; kuna cin arzikin Sa.

Muna tunawa da ku kullum a zukatanmu da addu'o'inmu.

Allah Ta'ala ya ba mu guzurin isowa inda ku ke.

Shahid Ali Haidar 22nd September 1999 - 14th December 2015

Address

Danmaigauta
Danja

Telephone

+9647840313248

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da'irar Danmaigauta posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Da'irar Danmaigauta:

Share