Nagartacciya

Nagartacciya Idan kana neman managartan labarai na gaskiya kuma da dumi duminsu maza garzayo shafin jaridar nagartacciya.

Marigayi Hassan Sarkin Dogarai...Takaitaccen Tarihin Marigayi Hassan Sarkin Dogarai Shahararren Dogarin Sarkin a Tarihin...
16/09/2025

Marigayi Hassan Sarkin Dogarai...

Takaitaccen Tarihin Marigayi Hassan Sarkin Dogarai Shahararren Dogarin Sarkin a Tarihin Najeriya na Wancan Zamani

An haifi Hassan Adamu a garin Kano a shekarar 1925, wanda aka fi sani da Hassan Sarkin Dogarai, shi ne Sarkin Dogarai na uku a zamanin Marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero.

Ana kiran sa da suna “Bishiya” saboda tsayin sa, Girman jikin sa, karfi, da kuma kallo mai ban tsoro, wanda hakan ya sanya ya jagoranci rundunar Dogarai masu rawani da bulalai a kan dawakai.

Marigayi Alhaji Hassan Adamu ya samu wannan mukami ne a shekarar 1990, lokacin da Marigayi Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero ya naɗa shi a matsayin Sarkin Dogarai.

Kafin naɗin Hassan, Sarki Ado Bayero ya naɗa wasu mutum biyu a wannan mukami Na Sarkin Dogarai, wato Marigayi Sarkin Dogarai Dan Wudil, da kuma Marigayi Sarkin Dogarai Adamu.

Amma banbancin su dashi shi ne, Hassan bai fito daga gidan sarauta ba.
A hakikanin gaskiya ma shi asalin sa Direba ne, daga bisani ya zama bawa ga Galadiman Kano, Marigayi Alhaji Tijjani Hashim.

Tijjani Hashim ya fara naɗa Hassan a matsayin Shamaki, kuma wannan ne ya bashi damar fara shiga fada da mukami a gidan sarauta.

A shekarar 1990, bayan rasuwar Sarkin Dogarai na lokacin, Galadiman Kano Tijjani Hashim ya bukaci Sarki Ado Bayero da ya naɗa Hassan a matsayin Sarkin Dogarai, kuma Sarki ya amince.

Hassan ya shahara sosai wajen jarumtaka, ƙarfi da kuma Aminci marar misaltuwa ga Marigayi Sarkin Kano Ado Bayero

Shahararren mawakin Hausa Alhaji Mamman Shata Katsina, ya kwarzanta Hassan da wasu kirari masu ratsa zukatan jaruman maza a cikin wata waƙarsa daya rera masa a cikin shekarun 90s, mai suna "Hassan Sarkin Dogarai", wadda ta ƙara masa suna a ko’ina cikin Kasar nan.

Alhaji Hassan ya rasu a shekarar 2007, kuma iyalansa sun koma gidansa da ke unguwar Sagagi a Kano, inda s**a ci gaba da rayuwar su.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya sanya Aljannah Firdausi ta zama makomar sa. Ameen

—Ko ka dena yin Mining da Airdrop to ka shiga kayi Claiming wannan 2Tokens ɗin da $Efsane suke bayarwa da yayi daidai da...
26/06/2025

—Ko ka dena yin Mining da Airdrop to ka shiga kayi Claiming wannan 2Tokens ɗin da $Efsane suke bayarwa da yayi daidai da $12 (Estimated Listing Price)

$Efsane Airdrop jerin Tokens ɗinsu kenan. Idan kayi participating ka samu kyautar $12 nan take worth of $EFS token ɗinsu. Su kuma Gems ɗin kullum suke rabawa masu daily check-in.

A yanzu shine project ɗin kawai da nasan suna biyan mutanan da suke yi musu Daily Check-in, saɓanin wasu projects ɗin da suke sa mutane su saka kuɗinsu gurin siyan GasFee ko kuɗin sign in domin validating na transaction.

Idan kaso, bayan kayi participating ka samu kyautar $12 ɗinka ba, shikenan ba dole sai kana daily check-in ba. Kawai sai kajira ta fashe ka cire.

Airdrop Link: https://222u.com/en_US/internal/register/?inviteCode=HBCG5W

Iya da Phone number ɗinka ko Gmail zakai register sai ka saka Password. Babu bukatar kayi wani KYC ko wani kafin su baka Airdrop token ɗin nasu guda biyu. Idan kana so, sai kayi participating da duka accounts ɗinka.

Ƙarin haske:

GEM—Wato na farkon shi ba'a iya Converting zuwa USDT sai dai zuwa Token ɗinsu mai suna $EFS.

GEM CASH—Wato shi wannan nan take ana iya Swapping ɗinsa zuwa USDT. Idan yakai adadin da ake bukata, sai kayi withdraw ɗinsa zuwa ko wacce Exchange ka siyar.

EFS—Wato wannan shine (Native Token) ɗinsu, wannan ake tunanin ranar 22nd July 2025 ɗinnan zasuyi Launching ɗinsa. Nan take zaka samu kyautar guda biyu idan kayi register.

*Initial Issue Price: $3
*Estimated Listing Price: $6

Stated that by their team.

USDT—Wato wannan shine abunda kowanne Ɗanɓaiwa yake nema a yanzu.😁 Wato idan kayi aiki tukuru ka haɗa (Team Members), a kullum idan ka shiga cikin site ɗin zakaga kana samun kyautar GEM Cash. Masu community ko nace Referrals, zasu fi saurin tara USDT ɗin. Dan haka, kayi ƙoƙarin haɗa Team Members koda babu yawa.

Register

Ƙungiyoyin mata sama da 100 sun baiwa Akpabio da majalisar dattawa hakuri akan zarge-zargen Natasha Kungiyar mata ƴan gw...
13/03/2025

Ƙungiyoyin mata sama da 100 sun baiwa Akpabio da majalisar dattawa hakuri akan zarge-zargen Natasha

Kungiyar mata ƴan gwagwarmaya ta ƙasa, NWCGG, mai wakiltar kungiyoyin mata 100, ta mika sakon dannar ƙirji ga shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, da kuma majalisar dattawan Najeriya kan zargin da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi.

Sun mika sakon hakurin ne yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a Jiya Talata.

Da ta ke magana a madadin kungiyoyin, Dokta Cecilia Ikechukwu ta yi Allah-wadai da zarge-zargen Sanata Natasha, inda ta bayyana hakan a matsayin "cin mutunci da rashin ta-ido"

A cewarta, abin da Natasha ta yi ya jawo wa matan Najeriya abin kunya tare da kawo cikas ga kokarin mata ‘yan siyasa da s**a yi aiki tukuru don samun amana da mutunta ‘yan Najeriya.

Hakika Kokarin Gwamna Zulum Na Tallafawa Al'ummarsa Abin Yabawa Ne Gwamnan bayan ya rabawa mutane 100,000 kayan abinci a...
13/03/2025

Hakika Kokarin Gwamna Zulum Na Tallafawa Al'ummarsa Abin Yabawa Ne

Gwamnan bayan ya rabawa mutane 100,000 kayan abinci a birnin jahar Borno.

Sannan gwamnatin jihar Borno ta sake kaddamar shirin ciyarwa na buda baki wa mutane kimanin 46,000 a kullum a cikin gundumomi 22 na birnin jahar Borno an tsara wurare kusan 230 inda za a dafa abinci da kunu da sauran kayan bude baki wa mutane masu karamin karfi

Karkashin jagoracin maikatar addinin jahar Borno masu anguwanni 110 ne zasu saka Ido suga yadda shirin rabawa al umma kayan bude bakin zai gudana a Gundumomi 22 dake cikin birnin

Allah Ya sakawa Maigirma Gwamnan Engr Babagana Umara Zulum da alheri

Daga Shettima Muhammad Mashamari Ward

YANZU-YANZU: Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha Majalisar Dattawa a yau Alhamis ta dakatar da Sanata Natasha...
06/03/2025

YANZU-YANZU: Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha

Majalisar Dattawa a yau Alhamis ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghen na tsawon watanni 6 sakamon rikicin ta da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio.

Hakan ya zo ne bayan bincike da kwamitin da Majalisar ta kafa na bincike kan dambarwar, wanda ya samu Natasha da laifin karya dokokin majalisar.

A cewar shugaban kwamitin, Sanata Neda Imasuen, an dakatar da Natasha na tsawo watanni 6 kuma dakatarwar ta fara daga yau 6 ga watan Maris.

APC ta dakatar da mashawarcin gwamnan Kebbi bisa razana manyan baƙi da maciji APC ta dakatar da Kabir Sani-Giant, mai ba...
04/03/2025

APC ta dakatar da mashawarcin gwamnan Kebbi bisa razana manyan baƙi da maciji

APC ta dakatar da Kabir Sani-Giant, mai baiwa gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris shawara kan harkokin mulki da siyasa, ba tare da bata lokaci ba bisa razana manyan baƙi a gidan gwamnati.

Wata sanarwa dauke da sa hannun sakataren jam’iyyar a jihar Kebbi, Sa’idu Muhammad-Kimba, ta sanar da dakatarwar a Birnin Kebbi a jiya Lahadi.

Ya bayyana cewa a ranar 8 ga watan Fabrairu, Sani-Giant ya kawo maciji gidan gwamnati, inda ya rika razana manyan baƙi da ke wajen.

Muhammad-Kimba ya ce wannan hali na iya jefa jam’iyyar kunya da kuma bata sunan jam’iyyar

Ya kara da cewa abin da Sani-Giant ya yi ya saba wa kundin tsarin mulkin APC.

A cewarsa, jam’iyyar ta dauki wannan dabi’ar tasa a matsayin abin kunya da kuma zubar da mutunci.

"Dakatar da shi na nan har sai an ci gaba da gudanar da bincike da kuma yiwuwar daukar matakin ladabtarwa, wanda zai kai ga kora idan aka maimaita," in ji Mista Muhammad-Kimba.

ABIN TAUSAYI: Tsananiɲ Râshin Lafiya Ta Sa Malam Bashir Ahmad Sani (Dan-Fili) Bai San Ma An Søma Azumi BaMalam mutum ne ...
04/03/2025

ABIN TAUSAYI: Tsananiɲ Râshin Lafiya Ta Sa Malam Bashir Ahmad Sani (Dan-Fili) Bai San Ma An Søma Azumi Ba

Malam mutum ne mai kokarin yada addinin musulunci da lafiyarsa, dukiyarsa, da kuma iliminsa tsawon shekara-da-shekaru, kuma Alhamdulillahi ya yi wa addinin musulunci hidima sosai.

A nan unguwarmu ta Koko Road Malam yake gudanar Tafsir a kowace shekara, kuma bana tunanin a jihar Sokoto akwai Malamin da al'umma ke son jin wa'azinsa kamar shi, domin daga lokacin da ya bude Tafsir al'umma za su ciki unguwarmu ta Koko Road ta ina domin sauraren wa'azinsa.

Sai dai abin tausayi a wannan karo Malam ya yi fama da rashin lafiyar da har ta kai ya manta da yaushe ne za a dauki Azumi, domin shi kansa bai san halin da yake ciki ba, bai gane wanda ya je duba shi.

Kamar yadda ya bayyana, Malam ya ce da ya samu tashi shekaranjiya a tunaninsa har yanzu akwai sauran sati biyu ne kafin Azumi, sai ya ji cewa ai gobe za a tashi da Azumi.

Karshen zance dai Malam ya ce a yanzu komai bai shirya domin yin Tafsir ba, domin rashin lafiyar da ya kwanta ya kashe kudade masu yawa, baida abinda zai shirya Tafsir, amman dudda haka zai daure ya yi saboda an saba kuma al'umma sun kosa a fito a fara.

Daga karshe Malam ya nemi 'yan uwa musulmi da su taimaka masa da abinda Allah ya h**e misu domin samun damar yin Tafsir cikin kwanciyar hankali.

Ubangiji Allah ya baiwa Malam lafiya, tabbas duk abinda ya saka Malam neman taimako to yana cikin wani hali ne.

S-bin Abdallah Sokoto

Address

Dutse

Telephone

+2347065881131

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nagartacciya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share