KDR Hausa News

KDR Hausa News KDR Hausa News 📰⚡
Tushen sahihin labaran Hausa
Gaskiya • Sahihanci • Labarai kai tsaye.

Dangidan Marigayi Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, Wato Yusuf Buhari Ya Amince Zai Fito Takarar Dan Majalisar Tara...
06/04/2026

Dangidan Marigayi Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, Wato Yusuf Buhari Ya Amince Zai Fito Takarar Dan Majalisar Tarayya Mai wakiktar Yankunan Sandamu/Daura Da Maiadu'a A jihar Katsina.

Wanne fata kuke Masa???

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da kafa wani sabon asusun jin kai domin tallafa wa jami’an rundunar sojin...
29/03/2026

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da kafa wani sabon asusun jin kai domin tallafa wa jami’an rundunar sojin ƙasar, musamman waɗanda s**a jikkata yayin aiki da kuma iyalan waɗanda s**a rasu suna hidimta wa ƙasa.

Sanarwar ta fito ne ta bakin mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, wanda ya bayyana cewa shugaban ya sanar da wannan shiri ne a ranar Lahadi yayin bikin cikarsa shekaru 74 da haihuwa.

A cewar sanarwar, wannan mataki na nufin karrama jarumtaka da sadaukarwar da sojojin Najeriya ke yi wajen kare ƙasar.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci Akanta Janar na Tarayya da ya buɗe asusu na musamman domin gudanar da wannan shiri. Haka kuma, ya yi kira ga gwamnonin jihohi, ‘yan majalisar dokoki, kamfanoni masu zaman kansu da sauran masu hannu da shuni da su bayar da gudummawa domin ganin shirin ya yi tasiri.

Ya ƙara da cewa, za a fitar da cikakkun bayanai kan yadda asusun zai gudana nan gaba.

Me zaku Ce Akai???

Anata yaÉ—a jita jitar Sheikh Sani Khalifa ya rasu a hannun jami'an DSS saidai a bangaren Fitaccen Lauyan Nigeriya Brr. A...
25/03/2026

Anata yaÉ—a jita jitar Sheikh Sani Khalifa ya rasu a hannun jami'an DSS saidai a bangaren Fitaccen Lauyan Nigeriya Brr. Abba Hikima cewa yayi:

Idan Labarin Mutuwar Sheikh Sani Khalifa Ya Tabbata, Akwai Tambayoyi Masu Nauyi Ga Gwamnati

Idan har rahotannin mutuwar Sheikh Sani Khalifa sun tabbata, to babu shakka gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta fuskanci manyan tambayoyi da nauyin alhaki a idon jama’a.

An k**a malamin cikin ƙoshin lafiya, amma kusan watanni uku kenan yana tsare ba tare da an ba shi beli ba. Wannan ya sa ake ta samun damuwa daga iyalansa da lauyoyinsa, musamman ganin yadda aka hana su damar ganawa da shi, duk da umarnin Federal High Court.

Rahotanni sun nuna cewa lafiyarsa na tabarbarewa yayin da yake tsare, amma babu bayani mai gamsarwa daga hukumomi. Idan har wannan ya kai ga rasa ransa, to wannan lamari zai zama babban abin dubawa game da yadda ake kula da haƙƙin ɗan Adam da kuma bin doka a ƙasar.

A irin wannan yanayi, wajibi ne gwamnati ta fito fili ta yi bayani mai gamsarwa ga al’umma. Rashin yin hakan zai ƙara jefa mutane cikin shakku da kuma rage amincewa da hukumomi.

Bugu da ƙari, zargin karya kundin tsarin mulki da kuma yin watsi da umarnin kotu lamari ne mai matuƙar tsanani. Ƙasa mai bin doka ba za ta iya ci gaba da tafiya cikin irin wannan yanayi ba tare da sak**ako ba.

A ƙarshe:
Gaskiya dole ta fito. Idan an samu kuskure, ya dace a ɗauki matakin gyara da kuma tabbatar da adalci — domin kare martabar doka da kuma haƙƙin kowane ɗan ƙasa.

Brr Abba Hikima.

Me zaku ce Akai???
Shin Da gaske Sheikh Sani Khalifa ya rasun kodai yana raye?

TIRKASHI 🤔 ‎Da Fara (Grasshopper) da Kyankyaso (Cockroach) duk tafiyar su ɗaya ce a kimiyya bambancin su kawai wurin kwa...
21/03/2026

TIRKASHI 🤔
‎Da Fara (Grasshopper) da Kyankyaso (Cockroach) duk tafiyar su ɗaya ce a kimiyya bambancin su kawai wurin kwana ne. Idan ka ci ɗaya ka ƙi cin ɗayan sam baka yi adalci ba saboda tamkar ka yi wariyar launin fata ne a kimiyyar halitta ta Biology. Fara ƙwai take yi sannan take kwana a jeji sak**akon babu wurin da zata kwana fiye da can ɗin. Hakazalika shima Kyankyason dai ƙwai yake yi amma shi ya zaɓi wurin da mutane suke ajiyar kayan da bazai musu amfani bane a matsayin nasa makwancin. Da Fara da Kyankyaso dukkan su 'yan Phylum Arthropods ne a Kingdom Animalia. Saboda haka sam abinda kake yi racism ne ya k**ata ka san wannan 😒.

Kaima zaka iya cin Kyankyaso tunda kana cin Fara???
‎
Daga ‎Salisu Yakubu RN RNT CT

TIRKASHI SHEIKH MANSUR SOKOTO YAYI ZAZZAFAN GARGADI GA MALAMAI MASU  TALLATA TINUBU DA SUNAN MUSLIM-MUSLIM 😲👇Kar malamin...
20/03/2026

TIRKASHI SHEIKH MANSUR SOKOTO YAYI ZAZZAFAN GARGADI GA MALAMAI MASU TALLATA TINUBU DA SUNAN MUSLIM-MUSLIM 😲👇

Kar malamin da ya ƙara tallata mana Muslim-Muslim ticket, ku tallata mana ayyukansu da alkhairinsu ga talakawansu

Shin abunda aka zaɓesu domin shi, kwalliya ta biya kuɗin sabulu?

Sheikh Prof. Mansur Sokoto ya faɗi haka ne yayin da ya yi watau huɗuba mai zafi akan halin da ƙasa ke ciki a wajen sallar idi.

Me zaku Ce Akai?

An tabbatar da mutuwar Ali Mohammad Naini, kakakin rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC), bayan wani harin s...
20/03/2026

An tabbatar da mutuwar Ali Mohammad Naini, kakakin rundunar Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC), bayan wani harin sama da aka kai a birnin Tehran a ranar Juma’a, 20 ga Maris 2026.

Rahotanni daga kafafen yada labarai sun bayyana cewa harin ya yi sanadin mutuwar Naini tare da wasu jami’ai, yayin da ake zargin cewa harin na da alaka da rikicin da ke kara tsananta tsakanin Iran da Isra’ila.

Majiyoyi sun ce, kafin mutuwarsa, Naini ya fitar da wasu kalamai masu zafi inda ya yi gargadi ga Amurka da Isra’ila, lamarin da ke nuna yadda rikicin ke kara daukar sabon salo.

Netanyahu Ya Ja Da Baya Kan Kai Hari Iran Bayan Gargadin TrumpFiraministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa...
20/03/2026

Netanyahu Ya Ja Da Baya Kan Kai Hari Iran Bayan Gargadin Trump

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta sake kai hare-hare kan cibiyoyin mak**ashin Iran ba, bayan wani gargadi da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi masa.

Wannan mataki na zuwa ne bayan wani hari da Isra’ila ta kai kan cibiyar iskar gas ta South Pars a Iran a ranar Laraba, wanda ya janyo martani mai zafi daga Iran. Rikicin ya haddasa tashin gwauron zabi na farashin gas da man fetur a kasashen Turai, abin da ya kara dagula kasuwar mak**ashi ta duniya.

A yayin da yake magana da manema labarai, Netanyahu ya musanta zargin cewa shi ne ke jan akalar shawarar Trump kan yadda zai tafiyar da rikicin da Iran.

Ya ce:
"Shin har yanzu akwai wanda ke tunanin cewa wani ne zai gaya wa shugaba Trump abin da ya k**ata ya yi? Haba mana.

Netanyahu ya kara da cewa Trump yana daukar matakai ne bisa abin da ya ga ya dace da muradun Amurka da kuma makomar duniya baki daya.

Ranar Juma'a Mutum Ya Je Idi Kuma Ya Je Sallar Juma'a, Idan Kuma Ya Zamana Dole Sai Daya Ne Mutum Zai Samu Zuwa, To Ya B...
19/03/2026

Ranar Juma'a Mutum Ya Je Idi Kuma Ya Je Sallar Juma'a, Idan Kuma Ya Zamana Dole Sai Daya Ne Mutum Zai Samu Zuwa, To Ya Bar Idin Ya Je Juma'a Saboda Ita Ce Farilla, Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi.

Seyi Tinubu ya bukaci 'yan Nijeriya da su kara amincewa da salon jagorancin mahaifinsa, yana mai bayyana shi a matsayin ...
17/03/2026

Seyi Tinubu ya bukaci 'yan Nijeriya da su kara amincewa da salon jagorancin mahaifinsa, yana mai bayyana shi a matsayin wanda ya zabi ya tsaya kai da fata wajen gyara kasar, maimakon yin shakulatin bangaro da ita, k**ar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Shin zaku Sake zaɓar Tinubu A kakar Zaɓe Mai Zuwa??

Sejjil missile wani makami ne mai linzami mai matsakaicin nisan kai da Iran ta ƙera domin ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar.Ra...
15/03/2026

Sejjil missile wani makami ne mai linzami mai matsakaicin nisan kai da Iran ta ƙera domin ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar.

Rahotanni daga masana harkokin tsaro sun nuna cewa makamin Sejjil na iya kai hari har kusan kilomita 2,000, lamarin da ke ba shi damar kaiwa wurare da dama a yankin Gabas ta Tsakiya. Makamin yana amfani da solid fuel, wanda ke ba shi damar a harba shi cikin sauri ba tare da jinkiri ba.

An fara gwada makamin a hukumance a shekara ta 2008, kuma tun daga lokacin Iran ta ci gaba da inganta shi domin ƙara ƙarfinsa da ingancinsa. Haka kuma, makamin yana da matakai biyu (two-stage missile), wanda ke taimaka masa wajen isa nesa cikin sauri.

Masana tsaro na ganin cewa Sejjil na daga cikin muhimman mak**an dabarun Iran, saboda yana iya taka rawa wajen ƙarfafa ƙarfin kariyar ƙasar da kuma ƙara tasirin ta a yankin.

Sai dai kuma, ƙasashen yamma ciki har da United States sun sha bayyana damuwa kan ci gaban irin waɗannan mak**ai, suna cewa hakan na iya ƙara tayar da hankali a yankin.

A taƙaice, makamin Sejjil na daga cikin manyan mak**an linzami da Iran ta ƙera domin ƙarfafa tsaron ƙasar, kuma yana ci gaba da zama muhimmin batu a muhawarar tsaro a Gabas ta Tsakiya.

TA’ASAR DORAYI: Gwamnatin Kano Ta Shirya Gurfanar da Matasan da Ake Zargi da Kisan Matar Aure da ’Ya’yanta 6Gwamnatin ji...
12/03/2026

TA’ASAR DORAYI: Gwamnatin Kano Ta Shirya Gurfanar da Matasan da Ake Zargi da Kisan Matar Aure da ’Ya’yanta 6

Gwamnatin jihar Kano ta kammala dukkan shirye-shirye domin gurfanar da wasu matasa da ake zargi da hannu a kisan wata matar aure da ’ya’yanta shida a unguwar Dorayi Chiranchi da ke cikin jihar.

A ranar Laraba ne gwamnatin ta gabatar da takardun tuhuma a gaban kotun majistiri da ke No-man’s-land, inda aka gabatar da wasu matasa huɗu da ake zargi da aikata laifukan.

Babban Sakatare a Ma’aikatar Shari’a ta jihar Kano, Barrister Salisu Muhammad Tahir, ya shaida wa kotu cewa gwamnati ta kammala bincike tare da rubuta takardun tuhuma, domin gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban Babbar Kotun Jiha mai hurumi.
Mutanen da aka gurfanar sun haÉ—a da Umar Auwal, Yakubu Dayyabau, Isyaku Yakubu da kuma Umar Ali, inda ake zargin su da haÉ—a baki wajen aikata kisan kai a wasu unguwanni daban-daban na jihar Kano.

Takardun tuhumar sun nuna cewa matasan ana zargin su da kashe wata mata tare da ’ya’yanta shida a unguwar Dorayi Chiranchi, sannan kuma ana zargin sun kashe wata mata tare da abokiyar zamanta a unguwar Tudun Yola.

Haka kuma akwai zargin cewa an yi wa wata ƙaramar yarinya fyade, wacce daga bisani ta rasu bayan an zarge su da kwakwule mata idanu, lamarin da ya kara tayar da hankalin al’umma.

Lauyoyin gwamnati sun bayyana wa kotu cewa an riga an kammala shirya tuhume-tuhumen, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban Babbar Kotun Jiha domin ci gaba da shari’ar.

👉 Ku bayyana ra’ayoyinku a sashen sharhi: Me ya k**ata a yi domin dakile irin waɗannan munanan laifuka a cikin al’umma?

Yanzu Yanzu: Ana Jita-Jitar Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan Dare, zai fice daga jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar APC. Me z...
09/03/2026

Yanzu Yanzu: Ana Jita-Jitar Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan Dare, zai fice daga jam'iyyar PDP zuwa jam'iyyar APC.

Me za ku ce Akai?

Address

Dutse

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KDR Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KDR Hausa News:

Share