Arewa Hausa Report

Arewa Hausa Report Arewa Hausa Report zata na kawo muku labarai iri iri a Fadin Duniyar nan
ku kasance tare damu...

Labarin Sirri Game Da Kin Amincewa Malam El-Rufai Ya Zama Minista.Labarin da muke samu shi ne Janaral TY Danjuma na daya...
11/08/2023

Labarin Sirri Game Da Kin Amincewa Malam El-Rufai Ya Zama Minista.

Labarin da muke samu shi ne Janaral TY Danjuma na daya daga cikin wadanda suke kokarin hana a ba Malam Nasir El-Rufai minista, kuma yana amfani da Sanata Remi Tunubu, matar Shugaban Kasa ne wurin cinma burinsa. Laifin El-Rufai a wurin T.Y Danjume bai wuce maganar Muslim- Muslim Ticket da ya yi a Kaduna kuma wanda hakan ya taimaka aka yi a Kaduna. Abin da suke nuna wa Shugaban Kasa shi ne in aka ba El-Rufai minista hakan yana iya jefa Nijeriya cikin tashin hankali.

Sannan, Kungiyar Kiristoci ta CAN da na Shi’a na amfani da Shehu Sani wurin hada zanga zanga da kuma rubuta ‘petition’ din da aka kai Majalisar Dattawa. A labarin da muka samu, da farko tsohon sanatan ya so ya yi amfani da Mr La ne wurin mika takardar a majalisa amma Sanata Mr La ya ki amincewa shi ne ya yi amfani da na Kogi West.

Baya ga wadannan, akwai kuma wadanda ke yakin El-Rufai saboda suna tunanin in ya masto kusa da shugaban kasa zai hana su rawar gaban hantsi. Akwai masu son yin takarar Shugaban Kasa kuma suna son duk yadda za a yi su hana duk wani babba daga Arewa da zai iya shugaban kasa yin karfi a kusa da shugaban kasa Tinubu. Daya daga cikin masu yakin El-Rufai a boye shi ne Kashim Shettima, Mataimakin Shugaban Kasa. Duk wadannan masu yaki da El-Rufai a boye saboda hana shi yin karfi suna amfani da Nubu Ribado ne.

Sannan sanin kowa ne matsalar wutan lantarki a Nijeriya na daya daga cikin abin da ke mayar da kasar baya kuma yake kara jefa kasar cikin kangin talauci musamman Arewa. Kuma manyan kasar nan su suke siye da wadannan kamfanonin raba wutan lantarki. Saboda haka sun san El-Rufai in ya zama mininstan wutan lantarki sai ya karya su. Sai ya gwamnati ta kwace kaddarorrinsu kamar yadda ya kudirta wurin tantance shi a majalisa. Saboda haka, su ma sun fito da karfinsu na ganin sun hana El-Rufai zama minista.

In kun lura duk cikin sunayen da aka tura na ministoci daga Arewa babu jajirtacce irin El-Rufai saboda asara

Arewa Hausa Report

Yanzu masu gidajen mai sai sun haɗa mutum biyu ko uku suke iya sayan mota guda, to ta ina za a tunkari wannan matsala, i...
11/08/2023

Yanzu masu gidajen mai sai sun haɗa mutum biyu ko uku suke iya sayan mota guda, to ta ina za a tunkari wannan matsala, inda ganin sai dai mu haƙura mu kulle gidajen man, in ji IPMAN

GARI YA WAYE: Barka da Juma'atu babbar rana,  A wancan lokacin kuna yara, me ku ka so ku zama idan kun girma? Burin naku...
11/08/2023

GARI YA WAYE: Barka da Juma'atu babbar rana, A wancan lokacin kuna yara, me ku ka so ku zama idan kun girma?

Burin naku ya cika?

Ina Tausayin Tinubu Saboda Yasa Gaggawa Akan Maganar Nijar, Cewar Manjo Hamza Al-Mustapha"Ba zai yiwu kana maganar diplo...
11/08/2023

Ina Tausayin Tinubu Saboda Yasa Gaggawa Akan Maganar Nijar, Cewar Manjo Hamza Al-Mustapha

"Ba zai yiwu kana maganar diplomasiya amma kuma kana bayar da umarni irin na soja ba, idan anaso dimukuraɗiyya ta ɗore sai da hankali da bin dokoki da girmama juna." Inji Al-Mustapha

AN ZALUNCI WANNAN MATASHIN.Sunan matashin Abdullahi Tukur Abba, dan jihar Adamawa wanda jami'an tsaron "Operation Faraut...
11/08/2023

AN ZALUNCI WANNAN MATASHIN.

Sunan matashin Abdullahi Tukur Abba, dan jihar Adamawa wanda jami'an tsaron "Operation Farauta" s**a mishi dukan tsiya har Allah ya dauki ransa.

Da farko an zargi matashin da sace waya iPhone 7 a gidan makwabcinsu dake unguwar Wuro Chakke, makwabcin ya kira jami'an "Operation Farauta" s**a dauke shi s**a je s**a mishi dukan tsiya har ya fita daga hayyacinsa.

S**a dawo dashi gidansu daure da ankwa jina-jina domin ya nuna musu inda ya boye wayar, da s**a shigo dashi gidan, sai Abdullahi ya fadawa mahaifinshi cewa, shi bai dauki wayar ba, kawai ya amsa musu ne domin ya ceci rayuwarshi, saboda suna shirin ka*she shi da duka.

Bayan an chaje gidan ba'a samu wayar ba sai Abdullahi ya fadi kasa yana aman jini, take mahaifinshi ya kaishi asibiti, likitoci sun shaidawa iyayan yaron da cewa dukan da aka mishi an fasa mishi har marenansa, wanda shine yayi sanadiyar rasuwarshi. Sai daga baya aka gano cewa ba Abdullahi ne ya saci wayar ba.

Hakika an zalunci Abdullahi, fiye da wuce kima, Abdullahi matashin yaro ne a wannan shekarar ya kammala sakandiri.

Muna kira ga Gwamnatin jihar Adamawa karkashin jagorancin Gwamnan jihar Adamawa Governor Ahmadu Umaru Fintiri da hukumar 'yan sanda ta jihar, da su gaggauta daukan mataki akan wa 'yanda s**a zalunci Abdullahi, don gudun kara aukuwar irin hakan anan gaba.

Wallahi nayi matukar tausayawa wannan matashin, Don Allah mu taimaka da Sharing har sakon ya isa ga Gwamnatin jihar domin daukan mataki akan su, domin sun zalunci Abdullahi.

Arewa Hausa Report

11/08/2023

Barka da Safiya

Arewa Hausa Report

"Babban kuskure ne tura dakarun ECOWAS Nijar, ina manyan mu ƴan Arewa kar ku bari a rusa mu tare da Nijar ƴan uwan mu- c...
11/08/2023

"Babban kuskure ne tura dakarun ECOWAS Nijar, ina manyan mu ƴan Arewa kar ku bari a rusa mu tare da Nijar ƴan uwan mu- cewar - Fadila H Aliyu

Address

Fct Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Hausa Report posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Hausa Report:

Share