Nasirul Mahdy

Nasirul Mahdy Ma aiki (S.A.W.W) Yace "Duniya Bazata Kareba Harsai Daya daga Ahalina yazo ya cikata da Adalci , Kam

22/07/2025

Malam Zakzaky (H) Ya Dade Yana Kokarin Fadakar da Al'umma Abinda Ake shirya Masu na Zalunci, Sama Da Shekaru Goma Kenan Da Yin Wannan Bayani.

Ammar Muhammad Rajab Ya Rubuta CewaHar yau na kasa goge lambobin waɗannan mutanen nawa, kuma na kasa 'unfreinding' ɗin s...
13/07/2025

Ammar Muhammad Rajab Ya Rubuta Cewa

Har yau na kasa goge lambobin waɗannan mutanen nawa, kuma na kasa 'unfreinding' ɗin su a Facebook:

Ali Muazu
Ahmad Buhari
Khausar Yaqoub
Eedris Ibraheem
Alhafiz Ne an
Bukhari Muhammed Bello Jega
Nusaiba Yakubu
Ibn Abbas
Kabiru Kano (Malam Kabir Alkanawy).
Ibrahim Usman
Mustapha U. Saeed

Waɗannan kaɗan ne daga cikin mutane ne, wanda na san su a zahiri, ba ma kwashe mako ba mu yi magana ba, akwai wanda kusan koyaushe muna tare imma a wurin CAFE, ko a Unguwar su, ko a makaranta, ko a Husainiyyah. Kazalika wasun su kuma muna tare da su tun farkon soma Facebook ɗina a 2010, amma a ranar 12-14 ga watan Disambar 2015, Manjo Janar Buhari ya katse rayuwarsu ta hanyar zalunci.

Na yi kuka, na yi kuka, sai da na kwashe kwanaki 4 cur bana iya cin abinci sai dai na sha ruwa. Wani abu ne ya tsaya min a wuya, shi bai wuce ba, kuma shi bai fito ba saboda baƙin ciki. Na yi baƙin ciki kamar raina zai fita saboda gawarwakin da na gani da idona an yi Dalar su a Gyallesu. Har yau da zan sami ƙwararren mai zane zan iya kwatanta masa yadda na ga an jibge gawarwakin nan a Gyallesu domin ya zana min. Na daɗe ina mafarke-mafarke masu munin gaske. A lokacin babu wanda ya damu a ƙasar sai ƙalilan.

Na tuna wani ɗan uwa da aka harbe shi a wuya, ya riƙe wuyansa ga shi bai kai ga faɗuwa ba, ya ce min "ɗan uwa an harbe ni a wuya", na kalle shi na kasa ce masa komai, na kasa ba shi kowanne irin taimako domin a daidai lokacin ne sojoji s**a fara amfani da RPG a kawukan mu. Sun riga sun tunkaro gidan Jagora (H).

A gabana aka harbi Baba Abdullahi Abbas, amma tsugunawa na yi na taɓa shi na ji ba ya motsi, na kasa komai akan shi duk da kuwa muna wasa da shi sosai a lokacin rayuwarsa. Har wasu lokutan ma na kan raka shi ƙauyuka wa'azi.

Ɗago kaina ke da wuya na ga wani soja ya harbe Baba Yakubu Okene a daidai jikin gidan Jagora (H). Baba Yakubu Okene yana tsaye sanye da farare kaya, yana ɗaga hannu sama yana ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, kwatsam sojan nan ya harbe shi tau.

Na yi baya kaɗan na ga JALABI da tawagarsa sojoji sun buɗe musu wuta suna masu cike da yaƙini da imani. Ban san lokacin da na tsaya kamar gawa a tsaye ba, har yau ba zan iya tuna tunanin da na faɗa a lokacin ba.

Bayan wannan sai da na kwashe fiye da wata 2 ina jin ƘARNIN JINI a kan duk abin da na taɓa a lokacin kwata-kwata shekaruna ba su wuce 22 ba. Saboda hidimar gawarwaki da muka yi duk jikin mu ya ɓace da jini. Ni dai har ga Allah, har ban son tuna GYALLESU.

Amma Jabberin a ranar farko da ya soma hira da ƴan jarida tun bayan hawansa mulki a 2015 wato a 'Presidential Media Chat', da ƴan jarida s**a tambaye shi kan waƙi'ar Zariya da mutanen da aka kashe, ba tare da nuna damuwa ko tausayawa ba, cikin ɗagawa da girman kai ya ce abin da aka yi daidai ne saboda dama shi ya bayar da umurni.

13/07/2025

Nasiha Ga Masu Zaluntar Raunana.

06/04/2025

SABON RAHOTO: Jami'an tsaro na Shirin kai hari Gidan Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) a Abuja.

Da gaske ne abun da kukeji na shirin faruwa a Abuja, Gamayyar jami'an tsaro Dss da Rundunar sojoji da sauran su, sun shirya domin kai harin ta'addanci kan muhallan 'yan uwa dana jagoran Harkar Musulunci Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) kamar yadda s**a Saba.

Tun kusan jiya s**a fara wannan mugun shirin har yau kuma da suke so su aiwatar da shirin nasu kamar yadda jaridar Sahara ta wallafa, Gwamnatin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu shi da Babban mai bashi Shawara akan tsaro Nuhu Ribadu shirin da sukeyi kenan akan Sheikh Zakzaky da almajiransa.

Charis
4:04

29/03/2025

AN GA JINJIRIN WATAN SHAWWAL!

Daga Ofishin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

بسم الله الرحمن الرحيم
وصلى الله على سيدنا محمد وآله الطيبين الطاهرين

Ya zuwa yanzu haka mun sami tabbacin ganin jinjirin watan Shawwal a Nguru, Potiskum, Damaturu, Geidam da Babban Gida duk a Jihar Yobe da Bajoga (a wani ƙauye mai suna Wawa) a Jihar Gombe. Har wa yau kuma an gani a wani gari mai suna Saran Dosa a Jihar Kebbi.

Har yanzu dai labarai na isowa garemu kuma muna ƙoƙaarin tantancewa. A duk waɗannan wurare jama'a masu yawa ne s**a gani. Don haka gobe Lahadi ta zama 1 ga watan Shawwal 1446, in sha Allah.

Allah Ta'ala Ya amshi ayyukan ibadodinmu da addu'o'inmu. Ya kuma maimaita mana na shekaru masu zuwa cikin ƙoshin lafiya da yalwar arziki.





29 Ramadan 1446
29/03/2025

08/04/2024

SANARWA:

Daga Ofishin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

بسم الله الرحمن الرحيم

اللهم صل على محمد وال محمد وعجل فرجهم

Ba mu sami labarin ganin jinjirin watan Shawwal ba a duk inda muka tambaya a faɗin Nijeriya a yau Litinin. Don haka za mu cika Ramadan kwana talatin. Jibi Laraba za ta zama 1 ga watan Shawwal 1445, watau ranar Sallah Ƙarama, in sha Allah.

Muna roƙon Allah Ta'ala ya amshi ibadodinmu ya kuma nuna mana na shekaru masu zuwa cikin ƙoshin lafiya da yalwar arziki.

تقبل الله منا ومنكم صالح الأعمال🙏





29/Ramadan/1445
08/04/2024

Nasir Isa Ali Jumhuriyar musulunci ta Iran ta tabbatar da shahadar sojojinta manya da kana su 7 tare da aiyana sunayensu...
02/04/2024

Nasir Isa Ali

Jumhuriyar musulunci ta Iran ta tabbatar da shahadar sojojinta manya da kana su 7 tare da aiyana sunayensu.

A wata takardar da ta fitar a daren jiya litini, rundunar ta bayyana cewar janarori biyu da matsakaita da kananan hafsoshi 5 jumilla su 7 ne s**a rasa rayukansu a harin dabbancin da israila ta kai kan karamin ofishin jakadancin Iran dake Damascus.

Ga sunayensu kamar haka:

Janar Muhammad Rida Zahedi
Janar Muhammad Hadi Hajirahimi

Hussain Amanollah
Mahdi Jalalati
Muhsin Sadeqati
Ali Agababaei
Ali Salihi Ruzbehani.

Rundunar IRGC ta bayyana cewar duk cikarsu suna aiki ne da rundunar Qudus, kuma sune mashawarta ga yan gwagwarmayar musuluncin dake fafatawa yanzu haka a Gazza da Lubnan.

Wannan harin ya nuna gazawar Israila da Amurka a fagen daga, kuma ya tabbatar da rashun nasararsu ko daya, don haka s**a aikata wannan domin huce haushinsu kan Iran.
Rundunar ta bayyana cewar ramuwarta na nan take me zafin gaske.

Tuni dai sabbun kwamndoji sun karbi aikin kuma sun dora daga inda magabata s**a tsaya.

Nasir Abu Muhammad

Alhamdulillah.Ofishin Maulana Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) sun sanar da cewa an ga wata, don haka gobe ɗaya ga watan Rama...
10/03/2024

Alhamdulillah.

Ofishin Maulana Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) sun sanar da cewa an ga wata, don haka gobe ɗaya ga watan Ramadan.

10/03/2024

Shehu Abu Bakara ya rubuta cewa

BAZA FA MU TABA GYARUWA BA!

ina duba wasu tsoffin rubututtuka na da Facebook suke dawo da su lokaci zuwa a lokaci a matsayin tunatarwa, sai na yi karo da labarin da na rubuta na wani mutum da yaje karbar bashin abinci amma me shagon ya hana shi saboda yana bin shi wasu kudi da be dawo da su ba ya koma gefe yana kuka wani bawan allah yazo ya saya masa rabin kwanon shinkafa amma koda s**a zo gare shi sai s**a tarar har rai yayi halin sa,

Cikin rubutun na ga wanda na rubuta na wani yaro da yayi amfani da yunwar gidan su budurwar shi wacce tazo neman temakon sa saboda qanin ta dan yaye sun wuni babu abinci ya saya musu, yace ya mayar da yarinyar tamkar takalmin sawar sa, yasa ko ya cire a duk lokacin da yake so,

Da labarin mahaifin da dan shi ya mutu an je yi masa ta'aziyya yake fadawa aminin sa cewa shi fa kukan sabo yake yiwa dan na sa, amma a cikin zuciyar sa yana murna ne cewa ya samu sauqin ciyarwa, wandannan labaran fa duk a lokacin ana sayar da shinkafa ne kwano nera 900,
Izuwa yau da ake sayar da ita nera 3300 kuma mu din ne muke rayuwa ba wasu aka sauya ba! muna kuma sayen ta haka mun haqura, shin ko ka iya tunano cewa wannan shinkafar da ake sayar mana da ita nera 3300 lokacin da aka noma ta ana sayen buhun taki 24k man yin ban ruwa 370 mandako na diesel nera 800 nawa kake jin za'a sayar da wacce za'a noma a gaba lokacin da buhun taki ake sayar da shi 48k sannan man ban ruwa700 da man dako 1700 a halin yanzu? Kaga kenan dole ne a shekara me zuwa mu sayi shinkafa 6600 kwano kenan! Kuma haka zamu haqura mu saya! Saboda bamu shirya gyaruwa ba!

Masu haqurqurtar damu ina nufin malamai wallahi da basa samun sauyi a cikin rayuwar su, ace tana tafiya ne irin tamu wacce sai ka fita ka samo, basa iya mallakar mota basa iya daukar dawainiyar rayuwar su da iyalin su yadda ta kamata kamar mu din nan! wallahi da zaku ji sun fito muku da ruwayoyi gangariya cewa annabi yayi umarni kayiwa azzalumin jagora bore,

Ka duba baya ka auna daga shigowar demokaradiyya malaman ka da suke hanaka yin zanga zanga gidaje da filaye da shagunan kasuwa nawa s**a s**a mallaka wadan da abaya basu dasu? Kana jin ko kai kake mallakar abinda malaman addini suke mallaka baza ka yarda ayi zanga zangar ba, wannan ya nuna ashe duk wanda ya taka tudu sai ya kaucewa fadar gaskiya don kada jin dadi ya yanke masa,

JAHILI KAMAR RAW MATERIAL YAKE me ilmi yana iya sarrafa shi ta hanyar da yake so,
Wannan ce ta sanya kullum kai talaka kake azabtuwa, kuma samun ka yana tsaye waje daya koma yana komawa baya, amma malamin ka yana qera sabbin gidaje da aurataiyar matasan mata yana kuma yi maka nasiha kayi haquri haka Allah ya qaddara maka! Can kuma zaka Ji shi akan mumbari ya kasa haquri yana zargin wani malamin da s**a yi taro aka tara musu kudi ya cinye, anan be yarda cewa haka Allah ya qaddara masa cewa za'a yi taro za'a tara kudi sheikh wane zai cinye don haka ya rungumi qaddara ba!

Kullum qaddara me kyau da marar kyau a jikin talaka take,

KAFIN MU SAMI 'YANCI SAI MUN NEMI 'YANCI (2)A Rubutunmu na Farko Munyi bayanin yadda masu Bautar da Al'umma suke karanta...
28/02/2024

KAFIN MU SAMI 'YANCI SAI MUN NEMI 'YANCI (2)

A Rubutunmu na Farko Munyi bayanin yadda masu Bautar da Al'umma suke karantar ta ciki da bai, kafin su bautar da ita, ta yadda Bazasu sami Turjiya ba daga waɗan da suke Bautarwar, inda wasu da ake bautarwar ma su kansu Basusan ana bautar dasu ba.

Matakin Da Masu mulkin mallaka suke bi domin tabbatuwar mulkinsu.

To bayan Masu mulkin mallaka sun karanci Al'ummar da suke yiwa mulkin mallaka to akwai hanyoyin da suke bi domin Tabbatar da wannan mulkin nasu, daga karantar Al'ummar da Sukayi, tunda sunsan Karfin Al'ummar da kuma Raunin ta.

Hanyoyin da 'Yan Mulkin Mallaka suke bi wajen Sarrafa Al'ummar Nigeria, Africa dama duk inda suke mulkin mallaka a duniya.

Tsarin Mulki: Soja Ko Farar Hulla ko Sarauta.
Wajen Tsarin Mulki suna samar da tsarin mulki ne da bazai taɓa cin karo da Muradunsu na mulkin mallaka ba, koda kuwa su waɗan da ake mulka suna tsammanin suna da 'yanci , to duk abinda zasuyi bazai wuce iyakar da 'Yan Mulkin Mallaka s**a shata musu ba, inde kuwa basu tsallaka wannan iyaka ba, to tsarin mulkin bazai amfani al'ummar ba.

Zabar Shugaba:
Wajen Zabar Shugaba da zai jagoranci wannan tsarin da 'Yan Mulkin Mallaka s**a yiwa sitamfi wanda bazai amfani Al'ummar kasar ba, suna tabbatarwa Shugaban Zaiyi biyayya ne ga Tsarin da aka bashi (Na mulkin mallaka) Kuma bazai ketare iyakar da aka shimfida ba.
domin tabbatar da biyayyar Dan takarar wannan kujera ta mulki to dole yaje can kasashen 'Yan Mulkin Mallaka domin amsa tambayoyin da Zasuyi masa, wanda daga nan zasu gane Zaiyi biyayya ko A'a.
Shiyasa Lokacin Zabe ko nadin sarauta zakuga ana rige rigen zuwa kasashen waje tarukan tattaunawa, To
idan Mai Neman Mulkin Zaiyi biyayya to sai a bashi damar takara, idan yaci mulki su saka shi cikin rabon arzikin da zasu deba daga kasarsa, Sannan su bashi kariya shi da iyalansa daga tuhumar cin hanci da rashawa, Sai yayi Komai ba komai, Anan duniya, idan bazai yi biyayya ba kuma to wajen zaben fidda gwanima dakyar ya wuce inka ya wuce to bazai wuce Babban Zabe ba, Inko duka 'Yan takarar sun yarda da sharadinsu to sai su zabi wanda Zaifi yin biyayya su bashi mulki.
inko bayan yahau kan mulki ya nemi bijirewa, to sun shirya yadda zasu kau da wanna mai mulkin, ta hanayar amfani da turakun tsarin mulkinsu da yake jagoranta.
Irin wadannan turakun Mulkin sun hada da Soja, Majalisa, da sauransu.

Tsaron Kasa:
Kasashe'Yan Mulkin Mallaka basa taba bari tsaron kasashen da suke mulka yabar hannunsu.
sune suke Bada training ga Askarawa na kasa, suke sayar mata da makamai, suke kula da cibiyoyin tsaron kasar da sunan masu bada shawara, suke Bada umarni wajen ayyukan tsaro na wanan kasa, dan haka duk yadda za'ayi Kasar tsaronta yana tafin hannunsu.
Idan sunso sai su samar da rashin tsaro domin biyan wasu bukatunsu kuma babu wanda ya isa ya samar da tsaron.
Duk sirrin Kasa yana hannunsu. dan haka dolen masu rike da mulkin kasar suyi musu biyayya sau da kafa.
Abin takaicin ma Duk training din da zasu bawa sojan wannan kasa to marar amfani zasu bashi, haka duk makamin da zasu bashi to shima marar amfani zasu bashi domin karma yayi tunanin kalubalantar su wata rana.

Tattalin Arziki:
Kasashe 'Yan mukin mallaka, Sune suke Tasarrufi da tattalin arziki na ƙasashen da suke mulka, sune suke da Bankin Bada Lamuni na Duniya Wato (IMF) sune suke da Bankin Duniya da yake tsarawa dukkan sauran Bankunan ƙasashe yadda Zasuyi aikinsu wato (World Bank), sune suke da cibiyar hada-hadar kudade ta duniya wato (World Trade Center) sune suke da Hanyar musayar kudi a tsakanin Bankunan duniya wato (SWIFT) sune suke da Kudin da dole idan zakayi cinikayya ta kasuwanci sai dashi wato(Dollar) Koda kasuwanci Kasa zatayi to Saide ta siyar ko ta sayo kaya ta amfani da kuɗin kasashe'Yan Mulkin Mallaka.
dade sauransu.
Shiyasa sai talaka ya rasa Meye Dalilin da yasa kudin kasarsa kullum yake rage daraja.
duk wadannan cibiyoyin kayan aikine na tabbatar da Mulkin Mallaka ga kasashen da ake yiwa mulkin mallaka.
Dolen kasa tayi biyayya ga dokoki da Muradun 'Yan Mulkin Mallaka, inkuma taki su saka mata takunkumi (su hanata cinikayya a duniya)

Sanna Har yau dinnan Kasashen da Ba'ayi masu mulkin mallaka to basu da yawa ko Goma dakyar su kai.

Nan Munyi takaitaccen Bayani ne akan abubuwa da s**a shafi kasa kai tsaye , wanda su masu mulki sun san dasu, kuma sunayin biyayya ga Iyayen Gidansu 'yan Mulkin Mallaka, to amma Meyasa Koda talakawa sun gane anayin mukin kasar sune ba domin su talakawa su sami saukin Rayuwa ba, kuma basu da wata dama tacewa ayi ko a'a a al'amuran Tafiyar da kasarsu , Amma duk da hakan talakawa basa iyayin komai ?
Ko Meyasa kaso mafi yawa na al'ummu sunsan mulkin mallaka ake musu amma basa iya yunkurin kawo Gyara ?

Insha Allahu zamu amsa wadannan tambayoyi a cikin Rubutun mu na gaba , da Zaiyi magana akan yadda 'Yan Mulkin Mallaka suke sarrafa Al'ummar Gari Domin su hanasu kokarin kawo sauyi.

~Ibn Abubakar Alhausawy

KAFIN MU SAMI 'YANCI SAI MUN NEMI 'YANCI (1)Shinfida da Gabatarwa:Kamar yadda na rubuta a taken rubutu kafin mu sami 'ya...
27/02/2024

KAFIN MU SAMI 'YANCI SAI MUN NEMI 'YANCI (1)

Shinfida da Gabatarwa:

Kamar yadda na rubuta a taken rubutu kafin mu sami 'yanci sai mun nemi 'yanci , to haka wanan Magana take daga nan har birnin Sin.

Ba'a taba yin wata al'umma ba da ta sami 'yanci batare da aiki Tukuru domin samun 'yanci ba a Tarihin Duniya, kuma ba za'a fara daga Nigeria ba.

Duk wata Daula ko wata ƙasa da muke kallo ta zama abin kwatance a yau, ta fannin ci gaban tattalin arziki, tsaro da rayuwa mai inganci, to wasune s**ayi aiki domin samar da wanna yanayin, da yanzu wasu suke mora kuma suke Girmamawa tare da sanya Albarka ga gwarazan da s**a samar da wanna yanayin.

Shi 'Yanci Nemansa ake a wajen wanda ya tauye ma al'umma shi, sannan a kwace shi ta yadda daga wanan lokacin to wannan mai tauye 'yanci din ya rabu da ikon da yake dashi na Bautarwa ga al'umma sannan dole ya tabbatar bashi da ta cewa a cikin al'amurran da s**a shafi wannan al'umma, kuma wannan al'umma bata bukatar izninsa wajen yin abinda ya dace ga Al'ummar ta, a takaice de Gudanar da wannnan al'umma ya dawo hannunta Dari Bisa Dari.

Tarkon Masu Bautarwa Ga waɗan da Ake Bautarwa:

Koda mutum kiwo yake to dole ne yasan irin dabbar da yake kiwo, dakuma halayyar ta a maban-bantan yanayi, Ya takeyi ida tana jin yunwa, Yaya takeyi idan tana jin ƙishirwa, wanne irin abinci tafi so, ya takeyi idan bata da Lafiya, ya takeyi idan ta fusata, wanne irin kololuwar mataki take dauka idan tayi Fushi?
Shin Halbi take ? ko Tunkuyi take ? shin Cizo take ? ko kuma kuka takeyi kawai ?

Kuma Dole wannan Mai kiwo yayi tanadin Yadda zai shawo kanta kowanne irin yanayi take ciki, ta hanyar amfani da dabaru, tsoratarwa, Yaudara, Da duk wata hanya mai yiwuwa, Shiyasa Masu kiwon suke samun damar sarrafa abin kiwonsu cikin sauki, koda kuwa sun nufi yanka abin da suke kiwon ne to turjiyar da zasu samu kadance kuma baze hana yanka abin kiwon ba, kuma sauran Dabbobin Bazasu iyayin komai ba. Domin Shi mai kiwon yasan Halayyar abin da yake kiwo ciki da bai a kowanne yanayi.

Dan Adam Kamar Abin kiwo ne Ga Masu Bautar dashi:

Kamar yadda mukayi bayani a sama yadda Masu kiwo Sukeyi na dabba da Allah bai bata Daraja , Ta Hankali kamar dan Adam ba, da yadda Masu kiwon suke ɓata lokaci wajen karantar Halayyar abin kiwonsu, to inaga Masu Sarrafa Dan adam domin su bautar dashi ?

To masu bautar da dan adam da suke kwace masa dukkan 'Yanci na rayuwa da zamantakewa, suma suna karantar Al'ummar da zasu bautar ne tun kafin su mamaye ta, Dole su karanci Dabi'a ta wannnan Al'umma, Shin wannnan Al'umma Tana da tsarin gudanarwa ne , Yayi tsarin shugabancin su yake, Idan akazo musu da bakon abu yaya Sukeyi, Idan sunajin Yunwa yaya Sukeyi, idan an kwace musu Wani abu nasu mai girma a wajensu yaya Sukeyi, Maganar wa sukeji, Idan Sunje Kololuwar yin fushi da tunzura iya me suke iya yi, Shin suna da juriya da Hakurin gwagwarmayar kwato abinda aka kwace musu ko de kawai bari sukeyi ya kwatu?
dade sauransu.
Sannan Masu Mulkin Mallaka suna tanadin ya Zasuyi su samar da maganin waɗan nan yanayi na al'ummar sannan kuma su Bautar da ita, ba tare ma ita Al'ummar tasan bautar da ita ake ba, b***e tayi Yunkurin Neman Hakkinta.

To waɗan da suke bautar da al'ummar Nigeria dama Nahiyar Afirka baki ɗaya, suna Bautar da Al'ummar ne ta hanyar amfani da duk wata hanya ta sarrafawa da suke da ita kuma har gobe A Kangin Bauta Nahiyar Afirka take, Saide bautarwar da ake yiwa wani wajen tafi ta wani wajen rashin Imani.

Zamu ci Gaba Da wannan rubutu Insha Allahu, a fita ta 2.

©️Ibn Abubakar Alhausawy

Sojan Sama na Amurka Aaron Bushnell Kirista  Ɗan Shekaru 24 Ya cillawa kansa wuta a gaban ofishin Jakadanci na Isra'ila ...
26/02/2024

Sojan Sama na Amurka Aaron Bushnell Kirista Ɗan Shekaru 24 Ya cillawa kansa wuta a gaban ofishin Jakadanci na Isra'ila a birnin Washington DC na Amurka.

Sojan yayi Hakane a yunkurin sa na farkar da Duniya irin girman Zalunci da Amurka da Isra'ila suke aikatawa akan Al'ummar Falsɗinawa a Gaza da yamma da kogin Jodan.

Kafin Ya kunna wutar a Jikinsa Saida yayi bayani inda yake cewa

"Ni Bazan kasance mai taimakawa Kisan Kiyashin da Akewa Falsɗinawa ba, dan haka zanyi Wani abu mai tsananin hatsari domin Farkar da duniya dan haka dole Falastinwa su sami 'yanci. "

Bayan ya cillawa kansa wuta a Gaban Ofishin Jakadanci na Isra'ila, yaci Gaba Da maimaita kalmar Free Palestine har Saida wutar taci karfinsa 😭 yazama muryarsa bata fita anajin me yake faɗa, amma yana tsaye yana daga hannu yana kara tabbatar da matsayarsa har Saida ya fadi kasa.

Duk Wannan abun yayi shine yayin da wayarsada ya ajiye ta akan ma'ajiyin waya take daukar video na abinda yake faruwa.

Hoton da yake Kasa Hoton Aaron Bushnell ne.

Menene ra'ayin ku akan irin wannan yunkuri na Aaron domin Farkar da Duniya Halin da Al'ummar Falasɗinawa suke ciki ?

~Ibn Abubakar Alhausawy

Address

Fct Abuja

Telephone

+2348062756904

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nasirul Mahdy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share