Manara RADIO

Manara RADIO Radio channel that sheds light to listeners in Africa,Middle East and across the globe, predominantly "HAUSA" on Islamic tenets and civilization

23/07/2025

LABARUN DUNIYA

PDP TA OSUN TA MARA BAYA GA TAZARCEN TINUBU A 2027

Jam’iyyar PDP reshen jihar Osun ta amince da mara baya ga neman tazarcen shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu a babban zaben da ke tafe a 2027.

PDP ce ke da gwamnati a jihar ta Osun da ke kudu maso yammacin Najeriya karkashin gomna Ademola Adeleke.

A zaben 2023, dan takarar PDP Atiku Abubakar ne ya yi nasara da tazara marar yawa kan shugaba Tinubu na APC.

Kakakin gwamna Adeleke, Adewale Rasheed ne ya karanta matsayar jam’iyyar da nuna duk da haka Adeleke na jam’iyyar PDP don raderadin zai sauya sheka zuwa APC ba daga gare shi ba ne.

Matsayar ta kara da cewa Adeleke zai sake takarar gomna a watan Agustar badi a inuwar PDP.

Masu sharhi na ganin hakan a matsayin wasu dabarun siyasa duk da sanarwar na nuna ai jihar Osun gidan shugaba Tinubu ne.



SANATA NATASHA TA YI YUNKURIN KOMAWA ZAMAN MAJALISAR DOKOKI

Sanata Natasha Akpoti Uduaghan ta yi yunkurin komawa zama majalisar dattawa a Talatar nan.

Natasha da rakiyar magoya baya ciki da ‘yar gwagwarmayar siyasa Aisha Yesufu ta yi kokarin shiga majalisar amma jami’an tsaro ba su ba da dammar hakan ba.

Natasha dai ta na aiki ne da hukuncin babbar kotun taraiya da ta ce umurci dawo da ita majalisar bayan dakatar da ita na tsawon wata 6.

Majalisar dai ta nuna bat a samu umurnin kotun ba kuma matakin Natasha k**ar rashin fassara umurnin kotun ne daidai gabanin kammalar wa’adin dakatarwar.



YUNWA TA YI SANADIYYAR MUTUWAR YARA 21 A GAZA

Tsananin yunwa ya yi sanadiyyar mutuwar yara 21 a Zirin Gaza a cikin sa’a 72 kacal k**ar yanda majiyoyi daga asibitin Annasr su ka baiyana.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin duniya ke kara nuna mawuyacin halin da yaran ke ciki a Gaza.

Kazalika akwai barazanar shigar yunwa don karancin abinci da ke abbadar al’ummar Falasdinawa a yankin da ke fama da hare-haren Isra’ila.

Alkaluma sun tabbatar da kashe fiye da mutum 1000 da ke fafutukar karbar abinci daga wani shirin agaji da majalisar dinkin duniya ke jagoranta a Gaza.

Sojojin Isra’ila kan kai hari da kan hallaka wadanda su ka taru a layin karbar kayan abinci da fakewa da cewa hare-haren na auna ‘yan kungiyar Hamas ne.

Jakadiyar taraiyar turai Kaja Kallas ta yi Allah wadai da kai hare-hare ga wadanda su ka taru don karbar kayan agajin abinci.

Kallas ta nuna ba yanda za a kare wadannan hare-hare don haka ma ta yi magana da ministan wajen Isra’ila Gideon Saar kan bukatar bad a kariya ga masu karbar kayan agaji ko tabbatar da kare rayukan al’umma a yankin.

Babban sakataren majalisar dinkin duniya Antonio Guterres ya yi kira da babbar murya na kare mutane masu taruwa don karbar kayan tallafin.



SAUDIYYA TA MARA BAYA GA SAKE GINA SHAM

Saudiyya ta mara baya ga aikin sake gina kasar Sham bayan shafe shekaru ta na fama day akin basasa.

In za a tuna mayakan tahrir sun yi nasarar kifar da tsohuwar gwamnatin Bashar Al’asad inda Ahmad Al-Sharaa ya zama jagoran gwamnatin kasar.

A zaman majalisar zartarwar Saudiyya karkakashin jagorancin Sarki Salman, Saudiyya ta ce ya na da muhimmaci a kwantar da duk wata fitina a Sham da taimakawa kasar ta sake farfadowa kuma tuni Saudiyya ta ware tallafi ga al’ummar Sham.

Kazalika Saudiyya ta mara baya ga matsayar ministocin wajen kasashe 28 kan kawo karshen yakin Gaza da barin kayan agaji su na shiga Zirin.

Kasar ta Larabawa ta bukaci kasashen duniya su yi tsayin daka wajen ganin lallai Isra’ila ta daina kawo tarnaki ga shigar agaji ga al’ummar Gaza.

18/07/2025

LABARUN DUNIYA

A NA YABAWA SHUGABA TINUBU DON YANDA YA KARRAMA MARIGAYI TSOHON SHUGABA BUHARI

Jama’a na yabawa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu don yanda ya karrama marigayi tsohon shugaba Buhari da Allah ya yiwa rasuwa bayan fama da jinya a wani asibiti a London.

Musamman masu yabon na cewa shugaba Tinubu ya yi duk abun da ya dace tun daga rasuwar Muhammadu Buhari har zuwa jana’iza a mahaifar sa Daura da ke jihar Katsina.

Duk wasu sun saba da sunan jami’ar Maiduguri wato UNIMAID amma rada ma ta sunan Muhammadu Buhari bai samu wata s**a mai yawa ba don yanda hakan ya zama karramawa ga marigayi Buhari wanda ya zama gwamnan soja a jihar arewa maso gabar da ke da helkwatar mulki a Maiduguri.

Wani abun ma da ya kara kayatar da jama’a shi ne jagorantar taron majalisar zartarwa na musamman don karrama marigayin.

Gaskiyar magana marigayi Buhari ya samu karramawar da za a iya cewa ba wani tsohon shugaba da ya samu irin ta a lokacin rasuwar sa watakila sai tsohon shugaba Nnamdi Azikwe.



AN GUDANAR DA ADDU’O’I NA MUSAMMAN A MASALLATAN JUMMA’A GA MARIGAYI BUHARI

An gudanar da addu’o’I na musamman a masallatan jumma’a da dama a Najeriya don addu’ar neman gafarar Allah ga marigayi tsohon shugaba Buhari.

K**a daga babban birnin taraiya Abuja zuwa jihohi da dama, limamai sun ambaci tsohon shugaban da yi ma sa addu’ar samun rahama.

Gabanin nan an samu malamai da dama na jan hankalin jama’a da muhimmancin yafewa wanda Allah ya yi wa rasuwa bisa laifin da su ke ganin ya yi mu su a lokacin rayuwar sa.

Hatta mukarrabin tsohon shugaban wanda su ka raba gari a siyasa Injiniya Buba Galadima ya ce ya yafewa marigayin duk wani sabani inda ya ce shi ma dama ya nemi yafiyar tsohon shugaban tun ya na raye.



BABBAR KOTUN TARAIYA TA AIYANA 10 GA OKTOBA TA ZAMA RANAR YANKE HUKUNCI KAN BUKATAR KORAR KARAR NNAMDI KANU

Babbar kotun taraiya a Abuja ta aiyana ranar 10 ha watan Oktoba ta zama ranar yanke hukunci kan bukatar korar kira da shugaban kungiyar IPOB ta ‘yan awaren Biyafara Nnamdi Kanu ya shigar na a kori karar sa don ikirarin ba shi da laifi.

Wannan ya biyo bayan rufe ba da shaida daga masu shigar da kara na gwamnatin Najeriya da gabatar da shaidu 5 da ke alakanta Kanu da cin amanar kasa da ta’addanci.

Babban lauyan gwamnati Adegboyega Awomolo ya ce hakika Kanu ya furta kalaman da su ka tada fitina har a ka kasha jami’an tsaro 170.

Kazalika Awomolo ya kara da cewa da sanin Kanu ya rika ambata cewa shi ne shugaban IPOB da a ka haramta.

Lauyan Kanu Mr.Kanu Agabi ya ce ba wata hujja da a ka bayar da ke tabbatar da Kanu na da alaka da tuhumar da a ke yi ma sa don mutum ne mai cika baki da kuri amma ba ya na nufin tada fitina ba ne.

Bayan k**ala sauraron muhawarar manyan lauyoyi sai mai shari’a James Omotosho ya aiyana ranar 10 ga watan Oktoba don yanke hukuncin sake Kanu ko tilasta ma sa ya gabatar da shaidun kare kan sa.



FAFAROMA YA BUKACI KAWO KARSHEN YAKIN GAZA

Fafaroma Leo ya bukaci Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu day a kawo karshen yakin Gaza da ke kawo matsala ga rayuwar mazauna yankin.

A wayar tarho, Fafaroma ya yi magana da Netanyahu ne bayan harin da sojojin Isra’ila su ka kai kan majami’ar katolika ita daya tilo a Gaza inda su ka kasha mutum 3.

Fadar Vatican ta ce Netanyahu ne ya bukaci zantawar ta tarho don nuna juyayin harin kan majami’ar.

A nan Fafaroma ya bukaci kula da wajajen ibada a irin wannan yanayi da kuma kare rayukan al’umma.

An ruwaito Netanyahu na nuna nadamar harin da dora alhakin haka kan batan kai na albarusai.

Akwai shirin Fafaroma Leo da Netanyahu za su gana kan lamarin na Gaza.

13/07/2025

LABARUN DUNIYA

OFISHIN MATAIMAKIN SHUGABAN NAJERIYA YA KOKA KAN ABUN DA YA CE SAUYA KALAMAN MATAIKAMAKIN SHUGABAN

Ofishin mataikamkin shugaban Najeriya ya koka kana bun da ya ce wasu kafafe sun canja manufar kalaman mataimakin shugaban a wani taro a Abuja.

Mataimakin shugaban Kashim Shettima ya dauko tarihi inda ya ce tsohon shugaba Jonathan ya yi nufin kawar da shi daga kujerar gwamna amma wasu jami’ai su ka nuna hakan ya sabawa tsarin mulki.

Shettima na magana ne a taron kaddamar da littafi da tsohon ministan shari’a Bello Adoke ya wallafa kan wani zargi da a ka ta yi na wata rijiyar man fetur mai taken Malabu.

Tuni a ka fassara kalaman na Shettima da cewa ya na hannun ka mai sanda ne ga shugaba Tinubu wanda ya dakatar da gwamnan Ribas Siminalayi Fubara daga kujera na wata 6.

Mai taimakawa mataimakin shugaban kan labaru Stanley Nkowcha ya ce Kashim Shettima na tare da matsayar shugaba Tinubu 100/100 kuma labarin ma akwai bambanci don shugaba Tinubu dakatar da Fubara ya yi ba kawar da shi gaba daya ba.

Nkowcha ya kara da cewa mataimakin shugaban na tare da shugaba Tinubu don matakin na jihar Ribas ceto dimokradiyya ne daga yanda lamura su ka rikice.



‘YAN BINDIGA SUN KAI MUMMUNAN FARMAKI KAN HANYAR FUNTUNA ZUWA GUSAU

‘Yan bindiga sun kai mummunan hari ga matafiya kan hanyar Funtua a jihar Katsina zuwa Gusau a jihar Zamfara.

Harin dai ya yi sanadiyyar kisan gilla ga mutum 7 ciki da mata da kananan yara kazalika kuma miyagun su ka sace wasu fasinjojin.

Akasin ya auku ne yayin da a ke ganin direban motar safa da akasin ya hau kan ta ke kokarin isa Gusau gabanin rufe hanya inda daidai yankin Tsafe ‘yan binmdigar su ka budewa motar wuta.

An yi nazarin inda direban ya dakata a nan Funtua har wayewar gari kafin hawa t**i, ta kan yiwu da an kaucewa mummunan labarin.



WIKE YA SAMU NASARAR KARAR DA A KA SHIGAR DA SHI KOTU KAN MABARATA

Ministan Abuja Nyesom Wike ya samu nasarar karar da a ka shigar da shi a babbar kotun taraiya Abuja kan matakan dirar mikiya kan mabarata.

Wani lauya mai zaman kan sa Abba Hikima ya shigar da ministan kara don a dakatar da shi daga korar mabarata a Abuja da zummar hakan ya zama kare hakkin su na ‘yan kasa.

Alkalin kotun James Omotosho ya yanke hukuncin cewa ministan Abuja da hukumomin Abuja na da hurumin daukar matakai kan mabaratan don barin su zai bude hanyar maida Abuja wajen gangamin mabarata da masu aikata laifuka.

Jostis Omotosho ya nuna daukar bara a matsayin sana’a na nuna yanda zuciyar mabaraci ta mutu ne.



NEMAN SULHUN TSAGAITA WUTA TSAKANIN ISRA’ILA DA HAMAS NA TANGAL-TANGAL

Tattaunawar neman sulhu don dakatar da yaki tsakanin Isra’ila da Hamas na tangal-tangal.

Zaman dai na gudana a birnin Doha na kasar Katar inda a yanzu bangarorin biyu ke zargin juna da kawo tarnaki a sulhun.

Majiya daga Hamas na nuna bukatar Isra’ila ta cigaba da jibge sojojin a Gaza bayan tsagaita wutar na kawo tsaiko a cimma yarjejeniya.

Hakanan ita kuma majiya daga Isra’ila na nuna Hamas ta na kin sassauci a sharuddan tsagaita wutar da hakan ke kawo tsaiko.

Yakin da Isra’ila ke yi kan Gaza ya shiga wata na 21 kuma duk yunkurin tsagaita wuta kan samu cikas don musamman yanda Isra’ila ke hankoron lallai sai ta shafe kungiyar Hamas daga doron kasa.

A yayin da hakan ke gudana, rundunar kare fararen hula a Gaza t ace hare-haren Isra’ila a jiya asabar sun yi sanadiyyar mutuwar fiye da Falasdinawa 20.

Ganau a Gaza ya ce harin ya shafi wata mahaifiya da ‘ya’yan ta maza biyu yarinya daya; inda jefa mu su bom ya daidaita naman jikin su.

10/07/2025

LABARUN DUNIYA

A*O ROCK TA CACCAKI TSOHON SAKATAREN GWAMNATIN NAJERIYA BOSS MUSTAPHA

Fadar A*o Rock ta caccaki tsohon sakataren gwamnatin taraiya Boss Mustapha don kalaman sa na nuna ba wata rawar a zo a gani da shugaba Tinubu ya taka wajen zaman tsohon shugaba Buhari shugaban kasa a 2015.

Mustapha wanda ke magana a taron kaddamar da littafi da kakakin tsohon shugaba Buhari, Garba Shehu ya wallafa ACCORDING TO THE PRESIDENT ya nuna tamkar ba da gudummawar Tinubu ne Buhari ya samu nasarar lashe zaben ba.

Nan take mai taimakawa shugaba Tinubu kan labaru Temitope Ajayi ya ce ai in ba don goyon bayan Tinubu bad a sam Buhari bai samu tikitin takarar APC a 2014 a filin wasa na Teslim Balogun a Lagos ba.

Ajayi ya kara da cewa don haka ai Buhari na bukatar zama dan takara gabanin samun nasarar lashe zabe.

Da alamun Boss Mustapha na nuna fushin magoya bayan shugaba Buhari ne a narkakkiyar jam’iyyar CPC da alamu ke nuna ba a tafiya da su a gwamnatin Tinubu.



NATASHA BA TA DAWO MAJALISA BA A TALATA

‘Yar majalisar dattawa daga jihar Kogi Natasha Akpoti Uduahgan bat a dawo zama a majalisar dattawa ba k**ar yanda ta sanar bayan hukuncin kotu.

An lura a ranar Talata da ya dace ta dawo akwai alamun tsaurara tsaro a gefen majalisa don matakan kauda-barar yiwuwar hatsaniya.

A tsari dai majalisar za ta jira samun takarar hukuncin babbar kotun taraiya karkashin Jostis Binta Nyako da ta yanke hukuncin majalisar ta janye dakatar da Natasha ta dawo da ita majalisar don tsawon dakatarwar na wata 6 ya sabawa tsarin mulki.

Hatta a gefen Natasha ba a ga umurnin neman ahuwar kotu kan wallafa shagube da ta yi ga shugaban majalisar Godwill Akpabio da su ke matukar tsama da shi.

Ra’ayoyi na tunanin ba mamaki lauyoyi sun ba wa Natasha shawarar tad an jinkirta komawar ta majalisar har sai an share dukkan tarnaki.



JAMI’AN TSARO 5 SUN RASA RAI A FAFATAWA DA ‘YAN BINDIGA A KATSINA

Jami’an tsaro 5 da farar hula daya sun rasa rai a arangama da ‘yan bindiga a yankin karamar hukumar Faskari a jihar Katsina.

Akasin ya auku ne lokacin da jami’an su ka kai dauki ga harin ‘yan bindigar da ya hada da kauyen Kadisau.

Ma’aikatar tsaron cikin gida ta jihar Katsina ta baiyana cewa wadanda su ka mutu sun hada da ‘yan sanda 3 da sojoji 2.

Jihar Katsina da ke cikin jihohin da ke fama da barayin daji ta kafa rundunar tsaron ‘yan sa kai don kalubalantar ‘yan bindigar.



KIMANIN MUTUM 40 SU KA RASA RAN SU A HARIN ISRA’ILA KAN GAZA

Wani sabon harin Isra’ila kan sassa daban-daban na Gaza ya yi sanadiyyar kisa ga kimanin Falasdinawa 40.

Asibitin Al-Nasr da ke yankin Khan Younis a kudancin Gaza ya baiyana cewa cikin wadanda hare-haren su ka kashe akwai mata 17 da yara 10.

Wani abun tausayi ma a wannan sabon harin akwai mutum 10 rus da su ka rasa ran su daga iyali daya.

Sojan Isra’ila ba su ce komai ba kan wannan mummunan harin in ka debe baiyana cewa sun kai hari hari kan fiye da bigirori 100 da su ka auna wadanda zaiyana da ‘yan bindiga, rumbunan mak**an Hamas da hanyoyin hada-hada na karkashin kasa.

Firaministan Isra’ila duk da wannan kashe-kashe ya sake ganawa da shugaban Amurka Donald Trump kan batun tsagaita wuta da hakan zai iya kai wa ga dakatar da yakin da ya kai wata 21.

Masu shiga tsakani na cigaba da tattaunawa yayin da mazauna Gaza ke fatar dakatar day akin da ke daukar rayukan jama’a kusan kullum.

Da alamun Isra’ila na son yin iyakacin kisan da za ta iya yi don ko an tsagaita wuta ta riga ta murkushe al’ummar yankin da sunan gamawa da Hamas.

Trump da Nrtanyahu sun zauna a ginin Capitol su ka shaidawa manema labaru burin su na murkushe Hamas da kuma kasancewar zumuncin Amurka da Isra’ila ya fi kowane lokaci karfi wajen fahinmtar juna a shekaru 77.

Hakanan Netanyahu ya kawo batun nan na inganta huldar kasashen Larabawa da Isra’ila ABRAHAM ACCORD da Trump ya kirkiro a mulkin sa na farko hard a burin karfafa diflomasiyya tsakanin Isra’ila da Saudiyya.

Turkiyya da ta ke kasar Turawa a lokacin ta soki kasashen Larabawa da su ka shiga wannan diflomasiyya da su ka hada da Daular Larabawa da Katar da zaiyana hakan da abun takaici.

Hakanan shi ma shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas ya nuna matukar fusata da abun da Larabawa su ka yi, ya na daukar hakan da tamkar ‘yan uwan su sun yi biris da su.

Wani lokaci cikin mako jaladan Trump na gabar ta tsakiya Steve Witkoff zai sauka a Doha na Katar don cigaba da zantawar bayan fage tsakanin Isra’ila da Hamas.

08/07/2025

LABARUN DUNIYA

SHIGA TA HADAKAR ADC BA CIN AMANAR LEBA BA NE-OBI

Dan takarar jam’iyyar Leba a zaben shugabancin Najeriya na 2023 Peter Obi ya ce shigar sa hadakar ‘yan adawa da ke da zummar kalubalantar APC a 2027 ba cin amanar jam’iyyar sa ta Leba ba ne.

Peter Obi da dan takarar PDP a 2023 Atiku Abubakar da wasu ‘yan hamaiya sun shiga jam’iyyar ADC don samun fagen yin takara a zabe mai zuwa.

Obi wanda har yanzu ya na jam’iyyar Leba ya nuna ya shiga gamaiyar ce don zaben 2027 kuma har yanzu a na 2025 don haka kenan bai ga abun tada jijiyar wuya ba.

Shugabancin jam’iyyar Leba da ke karkashin Julius Abure na nuna rashin amincewa da matakin na Obi har ma da bukatar sa da ya fice daga jam’iyyar.

Daya bangaren karkashin Mrs.Nenadi Usman ya mara baya ga matsayar Obi ta taka rawa a ADC.

Hakika hadakar na fama da kalubale na wasu ‘yan jam’iyyar ADC da ke ganin wasu na neman kwace mu su jam’iyya don haka su ke kalubalantar hakan a kotu.

Gamaiyar dai ta nada tsohon shugaban majalisar dattawa David Mark ya zama shugaban jam’iyyar.



OLUBADAN YA RIGA MU GIDAN GASKIYA

Basarake a jihar Oyo Olubadan Oba Owolabi Olakulehin ya riga mu gidan gaskiya ya na mai shekaru 90 a duniya.

Oba Olakulehin dai ya samu hawa kargar sarautar ne ma a bara inda ko a wannan lokacin ba shi da koshin lafiya.

Tuni shugaba Tinubu ya mika sakon ta’aziyyar sa ga masarautar Badun da al’ummar jihar Oyo kan mutuwar basaraken.

Shugaba Tinubu ya kara da cewa a makon jiya basaraken ya turo ma sa gaiyatar bukin cikar sa shekara 90 a duniya da kuma shekara daya kan karaga; amma ‘yan kwanaki gabanin bukin sai ta Allah ta kasance.



AN KORI MASU BIYAIYA GA SARKI AMINU ADO BAYERO DAGA BABBAN GIDAN FADAR KANO

An kori masu cigaba da biyayiya ga Sarki Aminu Ado Bayero daga babban gidan fadar sarkin Kano.

In za a tuna tun bara gwamnan Kano ya kwabe Sarki Aminu Ado daga sarauta ya dawo da Sarki Sunusi Lamido kan karaga.

Sarki Aminu Ado ya shigar da karar kalubalantar kwabe shi inda bisa ya cigaba da sarautar sa daga fadar sarki ta Nasarawa a nan Kano.

Wato yayin da Sarki Sunusi ke sarauta a babbar fada da ke kofar kudu, shi kuma Sarki Aminu na sarauta daga gidan Nasarawa.

An samu hatsaniya yayin da ‘yan ayi-ta-ta-kare su ka nemi fitar da magoya bayan Sarki Aminu da karfin tsiya daga fadar.



TRUMP YA GANA DA NETANYAHU A WHITE HOUSE

Shugaban Amurka Donald Trump ya gana da Firaministan Isra’ila a fadar White House kan shirin neman tabbatar da tsagaita a yakin Gaza.

Trump ya zauna kan dogon teburi daura da Netanyahu ya na mai nuna lokaci ya yi na dakatar da yakin Gaza da nuna Hamas na shirye don kulla yarjejeniya.

Donald Trump wanda a baya ya nemi al’ummar Gaza su tattara komatsen su, su fice daga Zirin, yanzu ya nuna za a iya samun tsagaita wuta zuwa mako mai shigowa.

A nan Netanyahu ya ce Isra’ila ba za ta kyale Gaza ba tare da zuba ido na tsaro ba kuma sam ba su damu da tunanin mutane da za su iya cewa ai hakan ya tauye matsayar zaman Falasdinu a matsayin cikakkiyar kasa mai ‘yanci.

Wani abun dubawa ma shi ne Netanyahu ya zabi da a ba wa Trump lambar yabon nan mai daraja ta duniya NOBEL kana bun da ya ce aikin sulhun zaman lafiya da ya ke jagoranta a kasashe.

Netanyahu ya mikawa Trump kofin wasikar da ya turawa kwamitin NOBEL kuma dama Trump na da burin samun wannan lambar.

Wannan na zuwa daidai lokacin da Hamas da Isra’ila ke ganawa ta bayan gida kan neman sulhun a birnin Doha na Katar.

Mutane sun taru daf da fadar White House a lokacin ganawar su na caccakar Netanyahu da zama mai kisan kare dangi a Gaza.



AMURKA TA FIDDA KUNGIYAR TAHRIR HAYAT SHAM DAGA JERIN ‘YAN TA’ADDA

Amurka ta zare sunan kungiyar Al-nusra ko Hayar Tahrir Al-Sham daga jerin kungiyoyin da ta zaiyana a matsayin na ‘yan ta’adda.

Kungiyar dai ta yi kundunbala ta mamaye birnin Damaskas din Sham da hakan ya kawo karshen mulkin Bashar Al’Asad.

Shugaba Trump ne ya tabbatar da matakin bayan dage takunkumin aware ga kasar Sham don ta farfado daga tsawon shekarun da ta auka yakin basasa.

Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ne ya rantaba hannu kan takardar janye kungiyar Nusra daga jerin ‘yan ta’adda a littafin Amurka.

In za a tuna jagoran Al-nusra kuma sabon shugaban Sham Ahmad Al-Sharaa ya gana da shugaba Trump a ziyarar da ya kai birnin Riyadh a kwanakin baya.

08/07/2025

Masjid Ghamama a Madinatul Munawwara na daga muhimman wajajen tarihi a Madina. Nan ne Manzon Allah mai tsira da aminci ya yi sallar rokon ruwa da sallolin idin sa biyu na karahe.Lokacin filin na karshen birnin Madina na asali.
Faifan daya ne daga tsaraba 7-10 na hajjin 1446Ah da zan kawo. Allah ya biya ma na bukatun alheri 👇

06/07/2025

LABARUN DUNIYA

ZA MU KAUDA DUK WANI DOGON TARNAKIN HULDAR NOMA DA KASAR BURAZIL-SHUGABA TINUBU

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya baiyana cewa Najeriya za ta kawar da duk wani tarnaki da ke kawo tsaiko wajen bunkasa aikin noma tsakanin Najeriya da kasar Burazil.

Shugaban wanda ya jagoranci tawagar gwamnatin sa zuwa Burazil a yankin Amurka ta kudu, na ganawa ne da shugaban Burazil Luiz Incio Lula Da Silva.

A yayin taron a cibiyar soja ta Copacabana da ke Rio Da Janeiro, Shugaba Tinubu ya ce tuni Najeriya na cikin tserereniyar bunkasar noma da hakan ya hada da kiwo har ma da na kaji.

A nan shugaban ya shaidawa shugaba Inacio Lula cewa Najeriya za ta kawar da duk wata kangiya don bunakasa hulda da Burazil ta bangaren kasuwanci, sufurin jirgin sama da noma.

Baya ga arzikin man fetur, Najeriya na da kasar noma da kiwo mai fadi ga kuma arzikin ma’adinai da ke bukatar kyakkyawar huldar zuba jari daga ketare.

A jawabin sa shugaba Da Silva ya ba da tabbatar Burazil za ta amince da duk wata yarjejeniya tsakanin ta da Najeriya ba da bata lokaci ba zuwa ziyarar nan gaba da shugaba Tinubu zai kawo.



BABBAR KOTUN TARAIYA TA YANKE HUKUNCIN MAJALISA TA DAWO DA SANATA NATASHA

Babbar kotun taraiya a Abuja ta yanke hukuncin majalisar dattawa ta dawo da Sanata Natasha Akpoti Uduaghan daga dakatarwar da ta kai wata 6.

Wannan hukuncin ya biyo bayan karar da Natasha ta shigar kotun don bukatar bi ma ta kadun ta a hatsaniyar da ta fara daga sauya ma ta kujera da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ya yi da Natasha ke ganin hakan shiga hakkin ta ne.

Mai shari’a Binta Nyako c eta jagoranci yanke hukuncin duk da ta azawa Natasha tarar Naira miliyan 5 don yanda ta keta hurumin kotu wajen yin shagube ta yanar gizo ga shugaban majalisar Akpabio alhali kotu ta haramta irin wadannan kalaman.

Jostis Nyako ta ce majalisa na da huruminm ladabtar da ‘ya’yan ta da su ka zarme amma dakatarwar da ta kai wata 6 ta yi tsanani don haka ta keta hurumin tsarin mulki.

Kotun ta umurci Natasha ta nemi ahuwar keta hurumin kotu da ta yi a jaridu biyu da yanar gizo.





BA WATA HAMAIYA TSAKANI NA DA ABDULJABBAR AMMA BA MA TARE A MATSAYAR SA-SHEIKH MADATAI

Shaharerren malamin Sufiyya a Kano Sheikh Abubakar Madatai ya ce sam ba wata jikakka tsakanin sa da Sheikh Abduljabbar Kabara sai dai sun yi hannun riga kan kalaman sad a su ka kai ga mukabala.

Sheikh Madatai na Karin bayani ne bayan mabiya Abduljabbar sun soki lamirin sa na matsayar da ya tsaya a kai kan hukuncin da kotu a Kano ta yankewa Abduljabbar din inda yanzu haka ya ke gidan yari.

Abubakar Madatai ya kara da cewa shi aboki ne ga Abduljabbar kuma ya ba shi shawara da ya rika tauna kalamai kafin furta su amma shawarar ba ta samu karbuwa ba.

Malamin na sufiyya ya bukaci almajiran Abduljabbar su rika karatu da fahimtar karatun da kuma tsayawa kan gaskiya ba kauda da kai daga gaskiyar lamura ba.

An samu sake bullowar batun Abduljabbar wanda kotu ta yankewa hukunci mai tsanani na kisa; inda wasu ke ganin ba a yi ma sa adalci ba yayin da wasu su ka ce shari’ar ta tafi bisa ka’ida.



SHUGABAN ADDINI NA IRAN AYATOLLAH KHAMENEI YA BAIYANA KARO NA FARKO TUN FARA ARANGAMA DA ISRA’ILA

Shugaban addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya yi baiyana ta farko tun fara arangama da kasar Isra’ila da ya gudana tsawon kwana 12.

Masu sharhi na cewa ta kan yiwu Ayatollah Khamenei wanda shi ne mai yanke matsayar karshe ga lamuran Iran ya fake a maboyar karkashin kasa don kaucewa farmakin Isra’ila ko Amurka.

An ga Khamenei a ranar Ashura ya fito ya zauna a masallaci da ke gefen gida da ofishin sa yayin da jama’a su ka mike su na yi ma sa sambarka da jinjina.

Khamenei a kalaman sa na dakatar da yakin ya aiyana nasara kan Amurka da Isra’ila musamman da nuna nasarar hari kan cibiyar sojan Amurka a Katar.

In za a tuna shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Khamenei barazanar cewa sun san inda ya ke amma ba su da niyyar kisa gare shi a yanzu.

Iran ta tabbatar da mutuwar fiye da mutum 900 a hare-haren na Isra’ila da Amurka da samun rauni ga dubban mutane amma ta ce sam hakan bai wargaza shirin ta na kera mak**an nukiliya ba da ta ke cewa na muradun zaman lafiya ne.



HAMAS TA NUNA KARSASHIN SHIGA YARJEJENIYAR TSAGAITA WUTA

Hamas mai mulkin Gaza ta baiyana karsashin neman tsagaita wuta tsakanin ta da Isra’ila a yakin da ya shiga wata na 21.

Wannan na zuwa biyo bayan zagin da Amurka ta yi kan shirin tsagaita wuta da masu shiga tsakani su ka gabatar.

Kungiyar dai ta Hamas da ke mulkin Gaza ta baiyana matsayar bayan ganawa da takwarorin ta a gwagwarmaya da su ka hada da ISLAMIC JIHAD wacce ke son tabbacin yarjejeniyar za ta dakatar da yakin gaba daya kar ya zama daga bisani Isra’ila ta cigaba da farmaki bayan mika ma ta k**ammun mutanen ta.

Rahotanni sun baiyana kashe Karin mutum 20 a Gaza a sabbin hare-haren Isra’ila ranar asabar kuma Isra’ila ba ta yanke matsaya ta karshe kan yarjejeniyar ba.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu zai ziyarci fadar White House a Litinin din nan don tattaunawa da shugaba Trump kan yarjejeniyar.

Donald Trump a amsa tambaya kan matsayar ta Hamas ya nuna akwai bukatar yin wani abu kan Gaza.

04/07/2025

LABARUN DUNIYA

TSOHON SHUGABA BUHARI NA LONDON DON KARBAR MAGANI



Tsohon shugaban Najeriya Manjo Janar Muhammad Buhari mai ritaya na London don samun jinya bisa rashin lafiya da ta same shi.

Majiyoyi sun baiyana cewa tsohon shugaban dai ya tafi London ne inda ya saba zuwa don duba lafiyar sa ko binciken koshin lafiyar sa inda a can ne ya ganu da jinyar da ta zaunar da shi a can.

An ga ko an ji jami’an labarum tsohon shugaban na tabbatar da wannan jinyar amma ba k**ar yanda a ke yayata tsanantar jinyar ba; su na masu cewa ya samun sauki kwarai.

In za a tuna tsohon shugaban da ya sauka daga mulki bayan wa\adi biyu na shekaru 8, kan je London da zarar ya samu jinya kuma cikin jinyar akwai ciwon kunne.

Muhammadu Buhari dai da ya dawo zama a Kaduna bayan gyara ma sa gidan sa, na da shekaru 82 a bana.



FADAR A*O ROCK TA CACCAKI TSOFFIN MINISTOCIN BUHARI DON SHIGA GAMAIYAR KALUBALANTAR TINUBU A 2027

Fadar gwamnatin Najeriya A*o Rock ta caccaki wasu tsoffin ministocin gwamnatin Buhari don shiga gamaiyar da ke da zummar kalubalantar shugaba Tinubu a zaben da ke tafe a 2027.

Kakakin shugaba Tinubu, Bayo Onanuga ya zaiyana tsoffin ministocin da marar sa godiyar Allah.

Gamaiyar dai ta hada da kusan dukkan masu hamaiya da ashugaba Tinubu don neman madafun ikon taraiya.

Cikin wadanda Onanuga ya ambata akwai tsohon ministaan sufuri Rotimi Amaechi wanda Onanuga ya ce ya tsani APC bayan faduwa zaben fidda gwani takarar shugaban kasa a 2023.

Sai Rauf Aregbesola wanda Onanuga ya ce an kore shi ne daga APC don angulu da kan zabo da ya yi a zaben gwamnan jihar Osun.

Sai Hadi Sirika wanda Onanuga ya ce ya samu matsala a kwangiloli da hakan ya kawo ma sa matsalar tantance amanar sa.

Onanuga ya yankewa mutanen hukunci da cewa masu maitar neman samun shugabanci ne kawai.



SHARERREN MAI TSARON GIDA NA KUNGIYAR KWALLON NAJERIYA PETER RUFAI YA RIGA MU GIDAN GASKIYA



Shahrerren mai tsaron gida na kungiyar kwallon kafa ta Najeriya Peter Rufai ya riga mu gaskiya.

Hukumar kula da harkokin kwallon kafa ta Najeriya NFF ta nuna juyayin mutuwar Rufai da nuna ba ta da labarin jinyar da ya yi.

Peter Rufai ya yi suna a bangaren tsaron gida na kungiyar kwallon kafa ta Najeriya tun sunan ta GREEN EAGLES hart a koma SUPER EAGLES.

Ba shakka ba za a kawo labarin lamuran kwallon kafa a Najeriya ba tare da ambatar sunan Peter Rufai ba.

An haifi Peter Rufai a jihar Lagos a 1963 inda bai dau hanyar gadon gidan su na sarauta ba a Idimu; ya tsaya kan kwallon kafa.





HAMAS NA BUKATAR TABBACIN DAKATAWAR YAKI GABA DAYA A SABUWAR YARJEJENIYA

Kungiyar Hamas mai mulkin Zirin Gaza na bukatar tabbacin sabuwar yarjejeniyar da a ke sa ran kullawa don tsagaita wuta ta hada da dakatar da yaki gaba daya.

Wannan kazalika na zuwa ne a lokacin da Isra’ila ta sake kai hare-hare a sassan Gaza da mutane da dama su ka rasa ran su.

Ma’iakatar lafiya a Gaza ta fidda adadin alkaluman da ke nuna kimanin mutum 59 ne su ka rasa ran su a alhamis din nan sanadiyyar hare-haren sojojin Isra’ila.

Isra’ila na cewa akwai alama mai karfi ta cimma tsagaita wuta da batun mika Isra’ila da Hamas ke garkuwa da su a yakin da ya kai wata 21.

Yunkurin samar da tsagaita wuta a Gaza ya kara karfi biyo bayan shigewa gaba da Amurka ta yi wajen samar da tsagaita wuta a hare-haren da Isra’ila ta kai wa Iran da ya haddasa yaki na tsawon kwana 12.

Dama batun kawo karshen yakin gaba daya ne kan zama abun da ba a cimmawa a yerjeniyoyin baya.

A na tsammanin cikin mutum 50 da Hamas ke garkuwa da su, 20 na raye kuma yarjejeniyar na bukatar mika masu ran da matattun da hakan zai kai ga sako wasu Falasdinawa da ke garkame a gidajen yarin Isra’ila.

30/06/2025

LABARUN DUNIYA

BA SADAUKARWAR DA ZA TA YI YAWA GA MASLAHA-FUBARA

Gwamnan jihar Ribas Siminalayi Fubara ya ce ba wata sadaukarwa da za ta yi yawa ga bukatar zaman lafiya ko samun maslaha.

An ruwaito Fubara na wannan magana lokacin da magoya bayan sa ke ganawa da shi a Fatakwal babban birnin jihar ta Ribas.

Gwamnan da ke zaman dakatarwa biyo bayan aiyana dokar t abaci a jihar , na nuni ne da yanda a ka ga ya yi zaman sulhu da ministan Abuja Nyesom Wike duk da ya na da hannu dumu-dumu wajen dalilan aiyana dokar ta bacin.

Fubara wanda nan ba ba dadewa ba zai koma kan karagar sa ya lura ainihin magoya bayan sa sun shiga damuwa da nuna takaicin ganawar sulhun, amma ya ce babban abu jihar Ribas ta samu zaman lafiya.

Gaskiyar magana da alamun Fubara na hikimar dawowa kan kujerar sa ne don in ya cigaba da cijewa, to Wike zai kara bullo da wata manakisar da za ta iya kifar da kujerar ma gaba daya musamman yanda ya ke da tagomashi a gwamnatin Tinubu.



JADAWALIN SHIRIN AIKIN HAJJIN BADI NA NAHCON YA BAIYANA

Jadawalin shirin gudanar da aikin hajjin badi shekara ta 2026 na hukumar alhazan Najeriya NAHCON ya baiyana.

Shirin dai na kan lokaci na tsakanin hukumomin Najeriya ne da masu masaukin baki wato Saudiyya.

Dama tun ranar 12 ga watan Zhulhijjah 1446 hijiriyya a ka fara tsara sabon shirin aikin hajji wato lokacin da a ka k**ala aikin hajjin bana da ya gabata.

Cikin jadawalin akwai daukar jami’an da za su yi kwangilar hidimar alhazai, batun k**a masaukai, yin rejista har zuwa k**ala biyan kudin kujera.

Jadawalin ya nuna za a k**ala shirin karshe zuwa 16 ga watan Afrilu na 2026 inda a ke fatan alhazai za su fara isa kasa mai tsarki.



NETANYAHU YA CE YA GA KAFAR KWATO KAMAMMUN ISRA’ILAWA A GAZA

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce ya ga kafar kwato k**ammun Isra’ilawa da ke hannun Hamas a Gaza.

Netanyahu wanda ya aiyana cewa kasar sat a samu nasarar yakin da ta yi na tsawon kwana 12 da Iran, hakan a gare shi hanya ce ta bude ta ceto k**ammun da Hamas ke garkuwa da su.

Tun 7 ga Oktobar 2023 Hamas ta kutsa yankin Isra’ila ta k**a mutum 251 inda daga nan a ka shiga yaki ko kuma a ce Isra’ila ta yi ta kai miyagun hare-hare da jiragen yaki kan Gaza ta kasha fiye da Falasdinawa dubu 50.

Hamas dai a yarjejeniya a baya ta sako wasu daga k**ammun inda yanzu a ke tsammanin akwai saura mutum 50 ciki da 27 da Isra’ila ta ce sun mutu.

Kungiyar masu bin diddigin kwato k**ammun a Isra’ila ta nuna farin ciki cewa akalla yanzu Netanyahu zai maida hankali wajen karbo wadanda su ka saura a hannun Hamas.

Kazalika akwai gawar wani soja da Hamas ta ke ajiye da shi tun 2014 da ya mutu kuma shi ma Isra’ila na son a mika ma ta shi.

Amfani da karfin soja kadai ba zai zama hanyar ceto mutanen da rai ba inda amfani da kofar yarjejeniyar tsagaita wuta ya zama mafi a’ala amma Isra’ila da ta kware wajen leken asiri da amfani da karfin marar kima na iya aikata komai.



HARIN ISRA’ILA YA KARA KASHE KIMANIN MUTUM 17 A GAZA

Wani sabon harin sojojin Isra’ila kan Gaza ya yi sanadiyyar kasha Falasdinawa 17.

Kakakin rundunar kiyaye lafiyar farar hula na Gaza Mahmud Bassal ya baiyana cewa 16 daga wadanda a ka kasha ta sanadiyyar boma-bomai ne daga jiragen yaki a wajaje 5.

Bassal ya ce akwai yara biyu ma da a ka kasha a gidan su ta hanyar jefa mu su bom a Zeitun da ke Gaza kuma gaba daya an daidaita gidan.

Isra’ila ba ta yi Karin haske nan take kan wannan kisan ba amma ta ce ta na dagewa ne don karya karfin sojan mayakan Hamas.

Ma’aikatar lafiyar Gaza fitar da alkaluman yawan mutanen da Isra’ila ta kasha zuwa yanzu a a yakin da sun kai 56, 412 kuma akasarin su mata ne da kananan yara. Majalisar dinkin duniya na da kwarin guiwa kan sahihancin alkaluman.

Address

Fct Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Manara RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Manara RADIO:

Share

Category