Arewa Channel 4

Arewa Channel 4 Let's talk North! News, education, and fun - it's all on Arewa Channel 4.

Ba zan goyi bayan Tinubu ba a zaben 2027 muddin ya canza Shettima - Sheikh JingirShugaban Majalisar Malamai na kungiyar ...
26/06/2025

Ba zan goyi bayan Tinubu ba a zaben 2027 muddin ya canza Shettima - Sheikh Jingir

Shugaban Majalisar Malamai na kungiyar Jama’atul Izalatil Bid’a Wa’ik**atis Sunnah (JIBWIS), Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya bayyana matsayansa kan zaben 2027 mai zuwa, inda ya ce, ba zai goyi bayan takarar Bola Tinubu ba a zaben 2027 matukar ya canza Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa.

A cewar Sheikh Jingir, “Ni da wasu na kusa da ni mun goyi bayan Tinubu da Kashim, kuma za mu sake goyon bayan takararku a tare. Duk wani yunkuri sabanin haka ba na tare da shi kuma ba zan goyi baya ba saboda a baya sun amince su yi aiki tare.

Sheikh Jingir ya bayyana hakanne yayin wani taron wa’azi a masallacinsa na ’Yan Taya da ke Jos, babban birnin jihar Filato.

Ya kara da cewa, “Na ji akwai wasu mutane marasa kishin kasa daga ciki da wajen APC da ke kokarin lalata alakar da ke tsakanin Tinubu da Kashim domin cimma mummunar manufarsu. To mu ba ma maraba da wannan Shugaba Tinubu.

Wani mutum a jihar Yobe ya sace ɗan maƙwabcinsa mai shekara 11, ya kashe shi da miyagun kwayoyiRundunar 'yan sandan jiha...
03/05/2024

Wani mutum a jihar Yobe ya sace ɗan maƙwabcinsa mai shekara 11, ya kashe shi da miyagun kwayoyi

Rundunar 'yan sandan jihar Yobe ta k**a wani mai garkuwa da mutane mai shekara 19, Mohammed Abdullahi, kan zargin laifin sace ɗan maƙwabcinsa mai shekara 11 da kuma kashe yaron ta hanyar shayar da shi miyagun kwayoyi.

Kwamishinan 'yan sandan jihar, CP Ahmed Garba, ya ce lamarin ya farune a karamar hukumar Gujba na jahar.

A cewar Kwamishinan, wanda ake zargin ya bukaci iyayen yaron da su biya naira dubu 600 kuɗin fansa kafin daga baya ya kashe yaron da miyagun kwayoyi kana kuma ya bizine gawan yaron.

Harin Tudun Biri: Rundunar Soji Ta Kammala Bincike, Ta Samu Manyan Jami'anta Da LaifiRundunar Sojan Najeriya ta sanar ce...
02/05/2024

Harin Tudun Biri: Rundunar Soji Ta Kammala Bincike, Ta Samu Manyan Jami'anta Da Laifi

Rundunar Sojan Najeriya ta sanar cewa ta kammala binciken da ta dade tana yi game da harin jirgin sama da jami'anta s**a kai kan mutanenda ba sujiba, basu ganiba, a kauyen Tudun Biri na karamar hukumar Igabi, a jihar Kaduna.

Daraktan yada labarai na shelkwatar tsaro, Edward Buba, wanda ya sanar da hakan a yau Alhamis a birnin Abuja, yayin taron manema labarai ya ce manyan jami'an soji biyu da aka samu da laifi za su fuskanci shari'a, kana kuma tun farko bai k**ata akai harin ba.

Idan za a iya tunawa dai harin na ranar Lahadi, 3 ga watan Disambar 2023, yayi sanadiyar ajalin mutane da dama da kuma raunata wasu mazauna garin Tudun Biri, Ugara da kuma Sabon Gida yayinda suke gudanar da bikin Mauludi.

Babbar musibar da ta afka wa kamfanina a bara, ita ce faɗuwar darajar naira daga naira 460 zuwa naira 1,400, a cewar Att...
02/05/2024

Babbar musibar da ta afka wa kamfanina a bara, ita ce faɗuwar darajar naira daga naira 460 zuwa naira 1,400, a cewar Attajiri Alhaji Aliko Dangote.

Kamfanin Dangote ya sanar da tafka asarar naira biliyan 164 sak**akon tabarbarewar tattalin arziki saboda faɗuwar darajar naira a bara.

Ranar Ma'aikata Ta Duniya: Shugaban Jami'ar Jihar Nasarawa Tasha Alwashin Inganta Rayuwar Ma'aikataShugaban jami'ar jiha...
01/05/2024

Ranar Ma'aikata Ta Duniya: Shugaban Jami'ar Jihar Nasarawa Tasha Alwashin Inganta Rayuwar Ma'aikata

Shugaban jami'ar jihar Nasarawa dake Keffi, Farfesa Sa'adatu Hassan Liman, ta lashi takobin samar da yanayi mai kyau da kuma inganta rayuwar ma'aikata domin ci gaba da bunkasa jami'ar.

Farfesa Liman ta bayyana hakanne cikin sakonta na taya ma'aikata murnar zagayowar bikin ranar ma'aikata ta duniya.

A watan Afrilun da ya gabata ne aka nada Farfesa Sa'adatu Hassan Liman a matsayin sabuwar Shugaban Jami'ar ta jihar Nasarawa kuma mace ta farko da ta taba rike wannan mukamin.

Muhimman Abubuwa Da S**a Ja Hankali Game Da Bikin Ranar Ma'aikata ta Duniya ta 2024 a Najeriya - Ma'aikatan Najeriya sun...
01/05/2024

Muhimman Abubuwa Da S**a Ja Hankali Game Da Bikin Ranar Ma'aikata ta Duniya ta 2024 a Najeriya

- Ma'aikatan Najeriya sun koka kan 'ƙuncin rayuwa.

- Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta sanar da cewa ta yi ƙarin albashi ga ma'aikatan gwamnati tsakanin kaso 25 cikin 100 zuwa 35.

- Ƙungiyoyin ƙwadago sun yi fatali da ƙarin albashin ma'aikata a Najeriya.

WATA SABUWA: ƴan sanda a Bauchi sun k**a wani matashi dake shigar mata da sunan Fatima mai ZogaleRundunar ƴan sandan jih...
01/05/2024

WATA SABUWA: ƴan sanda a Bauchi sun k**a wani matashi dake shigar mata da sunan Fatima mai Zogale

Rundunar ƴan sandan jihar Bauchi ta k**a wani matashi mai suna Kabiru Ibrahim Dake shigar mata da sunan Fatima mai Zogale.

An k**a matashin ne a lokacin da yake ƙoƙarin cutar wani matashi akan cewa shi mace ce. Bayan saurayin ya ɗaukeshi kwanan gida, saida s**aje gidan sai yaga na mijine ɗan uwansa.

Filato: An kashe mutum 13, an raunata 10 a Mangu da BokkosA ranar Jumma'ah, rundunar 'yan sandan jihar Filato tace 'yan ...
20/04/2024

Filato: An kashe mutum 13, an raunata 10 a Mangu da Bokkos

A ranar Jumma'ah, rundunar 'yan sandan jihar Filato tace 'yan bindiga sun kashe mutum 11 da kuma raunata wasu 7 a kauyen Tilimpat, na gundumar Push*t, a karamar hukumar Mangu na jihar Filato.

Kazalika, rundunar ta ce an kashe mutum 2 da kuma raunata wasu 3 a karamar hukumar Bokkos na jahar a ranar Alhamis.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, DSP Alfred Alabo, wanda ya sanar da hakan cikin wata sanarwa ya ce Kwamishinan 'yan sanda na jahar, CP Emmanuel Olugbemiga Adesina, ya ziyarci wuraren da lamarin ya faru domin shaida irin barnar da aka yi.

Kakakin ya kara da cewa Kwamishinan 'yan sandan ya tura da karin jami'ai wuraren da lamarin ya faru, kana kuma ya zanta da masu ruwa da tsaki na yankin da nufin samar da hanyoyin dawo da zaman lafiya a yankunan.

Kotu ta daure wani dalibi wata shida kan laifin satar tukunyar gas a JosA ranar Talata, kotun Majistre dake Jos, ta daur...
16/04/2024

Kotu ta daure wani dalibi wata shida kan laifin satar tukunyar gas a Jos

A ranar Talata, kotun Majistre dake Jos, ta daure wani dalibi dan shekara 24, mai suna Ayobami Analowo, kan laifin satar tukunyar gas.

Sai dai Alkalin kotun, Shawomi Bokkos, ya baiwa Analowo zabin biyan taran kuɗi naira dubu 20.

Da farko, mai kara, Spekta Ibrahim Gokwat, ya shaidawa kotun cewa wanda aka yankewa hukuncin ya aikata laifinne tun ranar 2 ga watan Maris.

02/04/2024

ALLAHU AKBAR: Yadda Sheikh Sudais ya zazzaga addu'o'i a masallacin Harami na Makkah a daren 23 na RAMADAN!

ABUN SHA'AWA: Irin abincin da ake rabawa talakawa mabukata a Saudiya.Wani ɗan Najeriya mazaunin kasar wanda ya turo da h...
02/04/2024

ABUN SHA'AWA: Irin abincin da ake rabawa talakawa mabukata a Saudiya.

Wani ɗan Najeriya mazaunin kasar wanda ya turo da hotunan ya ce a Saudiya ba a rabon abinci ba naman kaza.

15/03/2024

Wasun mu suna aikata wannan kuskure, daure ka kalla zai amfane ka.

Address

Fct Abuja

Telephone

+2349043462369

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Channel 4 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Channel 4:

Share