White Connect GL

White Connect GL Maraba daku,
Wannan kafar labarai ce Ilimantarwa, Nishadantarwa, fadakarwa gami da tallata hajojinku.

Rahoto:Jami’an tsaro sun k**a wasu mutane da ake zargi da yunkurin aikata laifi a guraren zaɓen cike gurbi da aka gudana...
16/08/2025

Rahoto:
Jami’an tsaro sun k**a wasu mutane da ake zargi da yunkurin aikata laifi a guraren zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Kananan Hukumomin Shanono da Bagwai.

Lamarin ya haifar da fargaba a tsakanin jama’a, inda ake ganin irin wannan abu na iya barazana ga tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma sahihancin zaɓe.

Sai dai ana fatan matakan da jami’an tsaro s**a ɗauka za su zama izina, tare da kawo tsafta a harkar siyasa.

Allah Ya sa mu dace, Ya kuma sa mu san darajar kanmu domin mu guji aikata abubuwan da za su zubar mana da mutunci da amana a idon duniya.

16/08/2025

🥰🤣

🙈🙈🙈
16/08/2025

🙈🙈🙈

NASIHAR WATA UWA MAI HANKALI GA 'YARTA YAYIN AURENTAKu duba comments section,👇Don Allah idan kun anfana ku yaɗa mana
28/07/2025

NASIHAR WATA UWA MAI HANKALI GA 'YARTA YAYIN AURENTA

Ku duba comments section,👇

Don Allah idan kun anfana ku yaɗa mana

Kar fa ku ce tsafi ne!😅👇Ka sa yatsunka a nan sannan ka tauna haƙoranka, sai ka gaya mana me ka ji a comment?Nan gaba za ...
27/07/2025

Kar fa ku ce tsafi ne!😅👇Ka sa yatsunka a nan sannan ka tauna haƙoranka, sai ka gaya mana me ka ji a comment?

Nan gaba za mu yi bayanin me yake faruwa.

INDA RANKA!Yawaitar Yiwa Dabbobi Fyade! Na Kara Ta'azzara A Kudancin Najeriya' Inda Ko A Safiyar Lahadinnan ma' Aka Sake...
27/07/2025

INDA RANKA!

Yawaitar Yiwa Dabbobi Fyade! Na Kara Ta'azzara A Kudancin Najeriya' Inda Ko A Safiyar Lahadinnan ma' Aka Sake Samun Wani Magidanci A Jihar Anambra Da Laifin Afkawa Wata Saniya Ta Karfin Tuwo' Inda Yayi Mata Jina-jina Ta Hanyar Fyade!

Ana yawan Samun Matasa Da Laifin Haikewa Dabbobi' Dangin Kaji' Akuyoyi' Tumakai' Da Shanu A Kudancin Najeriya!

Allah Kasa Mufi Karfin Zukatan mu' Amin 🙏

Ba zaki fahimci illar da kikayi wa rayuwar ki ba sai nan gaba matukar zaki yi sabon Allah.Duk lokacin da kika biyewa rud...
27/07/2025

Ba zaki fahimci illar da kikayi wa rayuwar ki ba sai nan gaba matukar zaki yi sabon Allah.

Duk lokacin da kika biyewa rudin duniya da bin kyalkyalin zamani,kika watsar da tarbiyyar ki daga baya zaki fahimci kinyi kuskure.

Su wadannan mazan da kika biye masu,su bazasu aure ki ba,KO kin masau maganar aure bazasu yi ba domin sun san ke ba mutuniyar kirki ba ce.

Kina kallon irin wadannan matan da s**a bi rudin zamani, daga karshe yadda rayuwar su ya zama abin tausayi.

Don haka ki rufawa kanki asiri kiyi tuban gaskiya,ki zama mutuniyar kirki,ki zama uwa ta gari ga zuri'ar da zaki haifa.

25/07/2025

Na yi aure shekaru biyu da s**a wuce. Ina aiki a wata makarantar sakandare a matsayin mai lissafi (accountant), ina samun albashi ₦110,000 a kowane wata.

Kwana biyu kacal bayan aure, mijina ya karɓi katin ATM ɗina. Duk lokacin da albashi ya shigo, shi ne ke cire duk kuɗin, ya ɗauki ₦70,000, ya bani ₦40,000 in yi komai da shi – abinci, sufuri, da duk wasu buƙatun gidan.

Na tambaye shi sau ɗaya, me yake yi da sauran kuɗin? Sai ya ce yana amfani da shi ne wajen taimaka wa harkar kasuwancinsa na dinki. Na kai ƙorafi wajen mahaifiyata, amma ta ce na yi haƙuri, ai shi mijina ne.

Wata rana, bayan watanni na yin shiru, na ce masa ya bar ni in yi amfani da cikakken albashina wata guda kacal don na sayi takalma da kayan zuwa aiki. Abin da ya ce kawai shi ne: “Ke wawiya ce.” Ya ce in ci gaba da amfani da abin da nake da shi. Da na dage, sai ya buge ni da bel.

Na kasa jurewa, sai na je wurin shugabarmu a makaranta, na gaya mata halin da nake ciki. Ta bani shawara na bude sabon asusun ajiya, kuma ta shirya yadda albashina zai rika zuwa rabin-rabi — ₦60,000 zuwa tsohon asusun, ₦50,000 zuwa sabon na sirri.

Na yaudare shi cewa makaranta ta rage albashi zuwa ₦60,000 saboda rage ma’aikata. Da albashi ya shigo, sai ya cire ₦40,000, ya bani ₦20,000. Na tambaye shi ta yaya zan iya kai kaina aiki da waɗannan kuɗin? Ina tambayar kuɗin da ya ke ajiyewa ma? Cikin dare sai ya buge ni da ƙarfi, ya dukar min cikin da nake da ciki — har na zubar da juna biyu.

Bayan na fita daga asibiti, sai ya sake yi min barazana: idan na sake tambayar wani abu, zai lahanta ni. Shi ne mutum da muka yi soyayya shekara da watanni, amma ban taɓa ganin wannan halin nasa ba. Amma saboda dokar cocinmu, ba a yarda muyi zaman mu kadai kafin aure, don haka ban samu damar gane shi sosai ba kafin auren.

Bayan wani lokaci, mahaifiyata ta kamu da ciwo. Na roƙi mijina in aika mata ₦15,000 don kula da kanta. Sai ya ce a’a, mahaifiyarsa na buƙatar injin daskare kifi (freezer) domin kasuwancinta. Ban ce komai ba. A sirrance, na aika wa mahaifiyata kuɗi daga ƙaramin ajiyar da nake yi a sabon asusun.

Mako guda kacal sai mahaifiyarsa ta yi haɗari da Keke Napep. Sai ya zo yana cewa in ɗauki bashi daga ofishina don ya haɗa da na shi a biya kudin jinya. Na tuna masa da lokacin da ya hana ni taimaka wa mahaifiyata. Na ce masa a’a, ba zan ɗauki bashi ba.

Watanni biyu bayan haka, sai ya mayar min da katin ATM — saboda ya gane albashin baya zuwa can ba. Na ce masa ya ajiye katin kawai, ba na buƙatarsa. Cikin fushi ya ɗauki bel yana kokarin bugeni. Amma wannan karon, na ce ya isa. Na ɗauki bututun labule, na buge shi a wuya.

Sai ya rika ihu yana cewa wai na yi ƙoƙarin kashe shi. Iyalan sa s**a ce in je in ba shi hakuri. Na ce a gawata ma ba zan roƙe shi ba.

Washegari, na tattara kayana, na bar gidan. Wata mata da na taɓa yi mata aikin nanny tun bayan sakandare ta taimake ni. Na gaya mata halin da nake ciki. Sai ta bani ₦450,000 don in k**a gida. Na koma sabuwar rayuwa – na samu salama da natsuwa.

Daga baya malamaina s**a ce in koma, a gyara zaman aure. Na ce a'a, ni dai na fi so in zauna lafiya fiye da mutuwa a cikin aure. Duk da haka na je na nemi gafara, amma na gaya musu gaskiya: “Rayuwata ta fi komai muhimmanci.”

Yanzu kuma mahaifiyata – wacce ke da ciwon suga da hawan jini, har yanzu tana cikin jimamin rasuwar mahaifina – tana ce min idan ban koma ba, zan karya mata zuciya, har ta mutu.

Wannan ne kadai ke damuna yanzu.

Amma gaskiya, ba zan iya komawa rayuwar azaba ba. Rayuwa guda ce. Ban shirya barin kaina cikin hannun wanda ke bugeni, ke ɗaukar ni k**ar baiwar sa, kuma ke barazana ga lafiyata ba.

---

Ina roƙon shawarar ku.

Me ya k**ata nayi?
Shin jin daɗin zuciyata ba ya da daraja idan mahaifiyata na cikin damuwa?
Ina jin laifi, amma ban ji kuskure ba.

Daga Shafin Naomi David

Akwai nau'in mutanen da ba sa son fita daga gida, ba sa son shiga cikin mutane, suna jin daɗin zama a ɗakinsu su kaɗai. ...
25/07/2025

Akwai nau'in mutanen da ba sa son fita daga gida, ba sa son shiga cikin mutane, suna jin daɗin zama a ɗakinsu su kaɗai. Idan sun fita, da zarar sun kammala abin da ya kai su, sai su koma gida ba tare da tsayawa a ko'ina ba.

Su ne mutanen da ke da aboki ɗaya ko biyu kacal, ba sa yawan kira ko chat ko mu’amala da mutane. Wayoyinsu yawanci a kan “silent” suke, kuma ba sa jiran kiran kowa, ko wani ya yi tambaya game da su.

Su ne waɗanda ke buɗe Facebook ko WhatsApp a kowane lokaci, amma ba sa posting, ba sa chatting, ba sa comment.
Ba su damu da kowa ba, ba su damu da a damu da su ba.

Su ne waɗanda kullum fuskarsu na da murmushi, hankalinsu cikin duniyar tunani da hangen nesa. Ba sa cutar da kowa, suna da hankali da ɗabi’a mai tsari da natsuwa.

Isa Sadi

Ya Allah!Kai ne wanda Ka halicce ni, kuma Kai ne Kake shiryar da ni.  Kai ne Kake ciyar da ni kuma Kake shayar da ni.  I...
23/07/2025

Ya Allah!
Kai ne wanda Ka halicce ni, kuma Kai ne Kake shiryar da ni.
Kai ne Kake ciyar da ni kuma Kake shayar da ni.
Idan na kamu da rashin lafiya, Kai ne Kake warkar da ni.
Kai ne Kake kashe ni, sa'an nan Kai ne Kake rayar da ni.
Kai ne nake fatan zai gafarta min kurakuraina a ranar sak**ako.
Ya Allah! Ka ba ni hikima, kuma Ka hada ni da mutanen kirki salihai.
Ka ba ni harshe mai gaskiya a cikin zance.
Ka sanya ni cikin ƴan Aljanna.
Ka gafarta mana da iyayenmu, da dukan muminai a ranar da za a tayar da mutane.
Kada Ka kunyatar da ni a ranar da za ka tashi mutane domin hisabi,
Ranar da dukiya da ƴaƴa ba za su amfana ba,
Sai wanda ya zo da zuciya mai tsarki.
Ameen.
© White connect

Wata mata suna cikin karin kumallo tare da mijinta, sai ta kalli tagar da ke kallon waje, ta ga makwabciyarta tana shany...
23/07/2025

Wata mata suna cikin karin kumallo tare da mijinta, sai ta kalli tagar da ke kallon waje, ta ga makwabciyarta tana shanyar kayan wanki. Sai ta ce wa mijinta:
"Ka duba wani irin wanki, sam sam bai fita ba. Wannan matar ba ta iya wanki sosai ba."
Mijinta ya kalli tagar amma bai ce komai ba, ya yi shiru.

Kullum idan makwabciyarsu ta shanyar wanki, sai matar nan ta maimaita wannan maganar ga mijinta.

Wata rana, sai ta duba tagani sai ta ce wa mijinta:
"Subhanallah! Kalli wankin ta na yau ya fita sosai kuma yayi kyau."
Sai mijinta ya ce mata:
"Abunda ya faru shi ne yau na farka da wuri sai na goge tagar gidanmu da kura da datti s**a taru s**a yi yawa a kai."

KU FITO MANA DA DARUSSAN DA KUKA DAUKA DAGA CIKIN WANNAN LABARIN.

Address

Fct Abuja

Telephone

+2348032801782

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when White Connect GL posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to White Connect GL:

Share