White Connect GL

White Connect GL Maraba daku,
Wannan kafar labarai ce Ilimantarwa, Nishadantarwa, fadakarwa gami da tallata hajojinku.

Jiya wani yaron Palestine yana kallon mizail din Iran a sama ya doshi Israel yana kuka cikin raja’i yana ‎ta maimaita ce...
16/06/2025

Jiya wani yaron Palestine yana kallon mizail din Iran a sama ya doshi Israel yana kuka cikin raja’i yana ‎ta maimaita cewa:

“اللهم سدد رميهم”

Allah ka shiryar da jifan su (Iran).

Wallahi ban san sadda hawaye yai ta zubo min ba.

Israel ta dade tana ganawa mutane azaba. Amma Allahu akbar wa lillahil hamdu, jiya sun ga barnar da basu taba gani ba tunda aka kafa kasar a shekarar 1948. Daga karshe ma na’urar kakkabo mizail din kasar komawa tayi tana harbin kanta da kanta.

Fielding by USA around Iran👀🇮🇷
15/06/2025

Fielding by USA around Iran👀🇮🇷

وَلِلَّهِ ٱلْعِزَّةُ وَرَسُولِهِۦ وَٱلْمُؤْمِنِينَ وَلَٰكِنَّ ٱلْمُنَٰفِقِينَ لَا يَعْلَمُونَA yau muna gani da idanunmu...
15/06/2025

وَلِلَّهِ ٱلْعِزَّةُ وَرَسُولِهِۦ وَٱلْمُؤْمِنِينَ وَلَٰكِنَّ ٱلْمُنَٰفِقِينَ لَا يَعْلَمُونَ

A yau muna gani da idanunmu yadda Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke luguden wuta kan haramtacciyar Isra$_ila, wato ƙasar da ta addabi al'ummar Falasɗinu, ta hallaka rayuka, ta ruguje gidaje, kuma ta ci gaba da alfahari da zalunci.

Wannan luguden wutar ba wai yana faruwa bane da karfin soja kawai ba, amma yana faruwa da ƙarfin imani, ƙarfin tawakkali, da ƙarfin gaskiya da aka jingina ga Allah. A lokacin da ƙasashe Musulmi da dama s**a firgita da Isra$_ila da kawayenta, Iran ta tsaya da ƙarfin Allah, ta nuna cewa idan mutum yana kan gaskiya, ba ya buƙatar yawan soja ko makami, sai yardar Allah.

Kamar yadda Alƙur'ani ya faɗa, ɗaukaka da iko ba na makiyan Allah ba ne, Allah ne Mai iko, kuma yana bai wa bayinsa muminai nasara. Iran na nuna mana cewa duk wanda ya dogara da Allah, zai tsaya a gaban zalunci ba tare da girgiza ba. Allah Ya taimaki Jamhoriyar Musulunci.

A ci gaba da hare-haren da Iran ke kai wa haramtacciyar ƙasar Isra$_ila, sabbin rahotanni sun nuna cewa makamai masu ƙet...
15/06/2025

A ci gaba da hare-haren da Iran ke kai wa haramtacciyar ƙasar Isra$_ila, sabbin rahotanni sun nuna cewa makamai masu ƙetare sauti (hypersonic missiles) daga Iran sun faɗa kai tsaye kan cibiyoyin kamfanin Rafael, wanda ke da alhakin ƙera makaman zamani da na kare kai.

Rahotanni sun tabbatar da cewa tashoshin jiragen ruwa na Ashdod da Ashkelon, inda Rafael ke da muhimman masana'antu da rumbunan ajiya, sune s**a fi fuskantar tsananin harin.

Duk da cewa yawancin hotuna da bidiyo sun fi mayar da hankali kan Tel Aviv da Haifa, cikakkun rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa barnar da aka yi a Rafael ta fi muni, sai dai tsauraran matakan toshe bayanai daga gwamnatin Isra’ila sun hana sakin hotuna daga yankunan da abin ya shafa.

Harin yana nuni da cewa Iran na da ƙarfafa leƙen asiri da ƙarfin fasahar soji, har ta iya kai farmaki kai tsaye kan cibiyoyin kera makamai da tsarin tsaron Isra . Wannan wani babban koma baya ne ga tsarin tsaron haramtacciyar ƙasar, kuma yana nuna cewa masu zalunci ba su da mafaka daga hukuncin Allah.

—Aisha Kazimiyyah

Ranar Arafah!A wannan wuni mai albarka ina roko da barar addu'o'in'ku gare ni, da iyayena, da malamai na, da iyalai na, ...
05/06/2025

Ranar Arafah!
A wannan wuni mai albarka ina roko da barar addu'o'in'ku gare ni, da iyayena, da malamai na, da iyalai na, da aminai na, akan Allah Ya hadamu da dukkan alherin Duniya da Lahira, Ya kare mu daga dukkan sharri, sannan Ya mana baiwa da kyakywawan karshe.
Nima zan muku addu'o'in alheri Duniya da Lahira.
Muna rokon Allah, Al-Hayyu Al-Qayyum, Ya amsa mana addu'o'in'mu, kuma Ya 'yen ta mu zuwa Al-jannah.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJ'UN 😭Mijin ya shiga dakin matarsa a asibiti,ya kalli fuskarta wacce ta canza kala sbd cuta...
02/06/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJ'UN 😭

Mijin ya shiga dakin matarsa a asibiti,
ya kalli fuskarta wacce ta canza kala sbd cutar da take fama da ita
Sai ya tambayeta cikin hargowa:
“Kin karanta rahoton?”

Ta ce: “Eh.”
Sai ya sake tambaya:
“Kin san kina da cutar kanjamau (AIDS)?”

Ta gyada kai kawai,
sannan ta cigaba da kwanciya cikin wahala,
ta janyo bargo ta rufe kanta.

Ya aje wata wasiƙa a ƙarƙashin matashinta,
sannan ya juya zai fita daga ɗakin yana cewa:
“Wata wasiƙa ce a ƙarƙashin matashin ki idan kin ga dama ki duba.”

Bayan ya fita kadan,
ta janyo wasiƙar, ta fara karanta ta.
Sai ta gani a rubuce

“na sakeki saki daya 1.2.3

Ta jefar da wasiƙar, ta lulluɓe kanta da bargo.

Yayin da yakusa barin asibitin,
likitan da ke kula da matarsa ya gan shi,
ya kira shi:
“Alhaji...”

Sai mijin ya juya yana tambaya cikin rashin damuwa:
“Kana da wani magana ne akan matar da ta riga ta zama tsohuwar mata ta,?

Domin na sake ta.
Zuwa yanzu iyayenta za su kula da ita b ni ba.”

Likitan ya kalle shi sosai sannan ya ce:
“Ba haka abin yake ba.
Kai kanka kana bukatar a duba jininka.”

Ransa ya baci, sosai Amma beyi gardama.

Bayan an kammala gwaje-gwajen,
likitan ya dawo da sakamako.

“Alhaji,” ya ce cikin takaici,
“Da bakin ciki nake fada maka cewa kai ma kana ɗauke da cutar da tsohuwar matarka ke da ita…”😳

Sai mijin ya katse shi cikin mamaki:
“Shin ta shigar min da cutar?”

Likitan ya ce:
“A’a, kai ne ka sa mata cutar.
Domin Kwanan cutar a jinin ka ya fi tsawon lokacin da cutar ta fara bayyana a gareta.
Dan haka Kai ne ka shigar mata da cutar.”

“Bayan ’yan kwanakii kai ma zaka fara ganin alamomin cutar.”

Mijin ya yaga rahoton, ya fice da gudu daga asibitin,
ya hau motarsa, ya tafi da gudu har kura tana tashi a bayan sa.

A daren nan mai sanyi gashi ana ruwa,
matar tana kwance a gadon asibiti,
iyayenta da ’yan uwanta suna gefenta.
Ta kalli fuskokinsu da farin jikin mutuwa yana bayyana a jikinta.
Da ƙyar ta iya magana:

Tana cewa “Ya Allah, Ka sani ban taɓa saba maka ba ta wan

02/06/2025
Wata kishiyar yinta annoba ce a gida wata kuma Alkhairi ce. Ance kishiyar Uwah ce tayi wannan aikin wayyo hanjinah innal...
02/06/2025

Wata kishiyar yinta annoba ce a gida wata kuma Alkhairi ce. Ance kishiyar Uwah ce tayi wannan aikin wayyo hanjinah innalillahi wa'annah ilaihin raji'un. Dan Allah a kamota itama a buga mata wannan kusar taji. Saboda ba danta bane shine zata kasheshi. Allah ya wulakanta duk wanda yayi wannan aika aikan😭😭😭

Allah yabaka lafiya 🤲🤲😢😢😢

Wata mata ta je gurin Annabi Dauda (AS) cikin fushi, ta ce masa: "Ya Annabin Allah! Ubangijinka yana da adalci kuwa?Sai ...
29/05/2025

Wata mata ta je gurin Annabi Dauda (AS) cikin fushi, ta ce masa: "Ya Annabin Allah! Ubangijinka yana da adalci kuwa?

Sai ya ce: "Kwarai kuwa, mai adalci ne, ba ya zalunci.

Menene labarin ki? Sai ta ce: "Ni bazawara ce, ba ni da mai taimaka min, ga 'ya'ya mata guda 3 marayu. Ina ciyar da su ne da sana'anar saƙa da nake yi.
Jiya na yi sakata mai yawa, na daure a wani jan tsumma, zan tafi kasuwa na sayar, na sami abin da zanciyar da kaina da 'ya'yana, sai wani tsuntsu ya zo ya wafce daga hannuna. Kuma ba ni da komai, ga marayu.😭

Kafin Annabi Dauda (AS) ya ce komai ga wannan mata, sai ga wasu mutane su 10 sun shigo, kowannen su da Dinare 100 a hannunsa, s**a ce:

"Ya Annabin Allah! Muna son za mu yi sadaka da wannan kudi... Sai Annabi Dauda (AS) ya ce da su: "Me ya faru?" Sai s**a ce:
"Muna cikin jirgin ruwa, sai iska mai karfi ta taso, jirgin namu ya bule, sai muka dinga ambaton Allah, kuma muka yi bakancen idan Allah Ya tseratar da mu, za mu yi sadaka da Dinare dari-dari.

Muna cikin wannan hali, sai wani tsuntsu ya jeho mana wani jan tsumma, a cikin tsumman akwai wata saƙa.
Sai muka toshe bular da wannan saƙar, Allah Ya tseratar da mu.

Sai Annabi Dauda (AS) ya yi godiya ga Allah, ya fuskanci wannan mata ya ce mata: "Ubangijinki mai adalci ne... Idan kin yi saƙar nawa k**e siyarwa?"

Sai ta ce: "Dirhami daya".
Sai ya ce: "Ga Dinare 1000, Allah Ya sayi saƙarki, karbi ki je ki ciyar da 'ya'yanki".

ALLAH YA WARWARE MANA MATSALOLINMU, YA KYAUTATA MANA TATTALIN ARZIKINMU.

AKWAI BUKATAN A YAYATA WANNAN KISSAR, KO WASUN MU ZA SUJI KARFIN GUIWA.
*
*Sanna muna rokon ku arzuki kuyi following 💫 wannan account Don Allah ✍️.......

24/05/2025

Shine Maganar Gaskiya

18/05/2025

🫡🧏

Wani mutum ya ce:Na gayyaci ɗaya daga cikin makwabtana zuwa gidana domin mu ci abincin buda-baki tare. A farko ya ƙi zuw...
16/05/2025

Wani mutum ya ce:
Na gayyaci ɗaya daga cikin makwabtana zuwa gidana domin mu ci abincin buda-baki tare. A farko ya ƙi zuwa, amma na dage har ya yarda ya zo.

Da muka isa gidana, na kai shi ɗakin baƙi, na ce masa:
"Ji daɗin kanka, ka ɗauka gidan kamar naka ne."

Bayan ɗan lokaci kaɗan, lokacin azumin Magariba ya matso. Na fara shirya teburin cin abinci, na jera faranti da abinci iri-iri masu daɗi waɗanda matata ta dafa — abinci masu ƙamshi da ban sha’awa.

Bayan ƴan mintuna, aka yi kiran sallar magariba. Sai muka zauna kan teburin, muka fara buda baki.
Amma na lura makwabcin nan yana cin abinci cikin baƙin ciki, yana ɗan ɗanɗanawa cikin jinkiri sosai.

Sai na kalle shi nace:
"Lafiya dai, ya Abu Abdallah? Me yasa kake cin abinci haka? Kana jin kunya ne? Ko kuwa ba ka jin yunwa?"
Sai ya yi min murmushi kawai, ya ci gaba da cin abincinsa.

Ni kuma na ci har na ƙoshi, cikina ya cika. Kuma abinci da yawa ya rage a tebur. Sai na ce masa:
"Ka ƙara ci, ya Abu Abdallah. Ni zan shiga cikin gida in shirya, mu tafi masallaci tare."

Na shiga ciki don shirya kaina. Amma kafin in fito, na leƙa ta taga mai madubin ɓoye (wanda daga ciki ba za a gan ni ba, amma ni zan iya ganin waje).

Abin da na gani ya karyar min da zuciya, idanuna s**a cika da hawaye ba da niyya ba.
Na gan shi yana tarawa ragowar abinci a cikin wani roba.

Na fito cikin gaggawa nace:
"Me kake yi haka, ya Abu Abdallah? Me yasa kake tara abinci haka?"

Karshen labarin ya na a comments section ko kubi profile Dina don fallow da zaran an ɗaura.....👎

Address

Fct Abuja

Telephone

+2348032801782

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when White Connect GL posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to White Connect GL:

Share