29/05/2025
Wata mata ta je gurin Annabi Dauda (AS) cikin fushi, ta ce masa: "Ya Annabin Allah! Ubangijinka yana da adalci kuwa?
Sai ya ce: "Kwarai kuwa, mai adalci ne, ba ya zalunci.
Menene labarin ki? Sai ta ce: "Ni bazawara ce, ba ni da mai taimaka min, ga 'ya'ya mata guda 3 marayu. Ina ciyar da su ne da sana'anar saƙa da nake yi.
Jiya na yi sakata mai yawa, na daure a wani jan tsumma, zan tafi kasuwa na sayar, na sami abin da zanciyar da kaina da 'ya'yana, sai wani tsuntsu ya zo ya wafce daga hannuna. Kuma ba ni da komai, ga marayu.😭
Kafin Annabi Dauda (AS) ya ce komai ga wannan mata, sai ga wasu mutane su 10 sun shigo, kowannen su da Dinare 100 a hannunsa, s**a ce:
"Ya Annabin Allah! Muna son za mu yi sadaka da wannan kudi... Sai Annabi Dauda (AS) ya ce da su: "Me ya faru?" Sai s**a ce:
"Muna cikin jirgin ruwa, sai iska mai karfi ta taso, jirgin namu ya bule, sai muka dinga ambaton Allah, kuma muka yi bakancen idan Allah Ya tseratar da mu, za mu yi sadaka da Dinare dari-dari.
Muna cikin wannan hali, sai wani tsuntsu ya jeho mana wani jan tsumma, a cikin tsumman akwai wata saƙa.
Sai muka toshe bular da wannan saƙar, Allah Ya tseratar da mu.
Sai Annabi Dauda (AS) ya yi godiya ga Allah, ya fuskanci wannan mata ya ce mata: "Ubangijinki mai adalci ne... Idan kin yi saƙar nawa k**e siyarwa?"
Sai ta ce: "Dirhami daya".
Sai ya ce: "Ga Dinare 1000, Allah Ya sayi saƙarki, karbi ki je ki ciyar da 'ya'yanki".
ALLAH YA WARWARE MANA MATSALOLINMU, YA KYAUTATA MANA TATTALIN ARZIKINMU.
AKWAI BUKATAN A YAYATA WANNAN KISSAR, KO WASUN MU ZA SUJI KARFIN GUIWA.
*
*Sanna muna rokon ku arzuki kuyi following 💫 wannan account Don Allah ✍️.......