Kankara Post

Kankara Post Jairdar Kankara Post kafar yada labaru cedata shahara wajen samar maku da shahihai,ingantattun labar.

Dan Majilisar Wakilai Hon. Shehu Dalhatu Tafoki Ya Rabawa Al'ummar Shi Na Yankin Kankara, Faskari Da Sabua N150m.Dan maj...
09/03/2025

Dan Majilisar Wakilai Hon. Shehu Dalhatu Tafoki Ya Rabawa Al'ummar Shi Na Yankin Kankara, Faskari Da Sabua N150m.

Dan majalisar Tarayya na mazabar Ƙanƙara/Faskari/Sabuwa Hon Engr Shehu Dalhatu Tafoki ya raba buhunan shinkafa ƙanana 10kg 2500,25kgs 500 da kuma manya Masu nauyin 50kgs 100.

Dan Majilisar Bai Tsaya nanba yakara da tsabar kuɗi N52m a matsayin tallafin azumi ga al'ummar mazaɓarsa

Taron rabon kayayyakin ya gudana ajiya Asabar 8 ga watan March 2025, daidai da 8 ga watan Ramadan 1446, a Farfajiyar Kasuwar Zamani ta garin Kankara.

Dr.Bishir Usman Ruwangodiya ya bayyana yadda tsarin rabon kayan arziki yake, inda yace kayan da aka sawo sun kai N98m sai kuma tsabar kudi N52m, da in an haɗa gaba ɗaya ƙimar kayan da kudin sun kai N150m

Dr. Ruwangodiya ya cigaba da cewa wadanda zasu amfana da tallafin akwai, Party excos na matakin dukkanin mazaɓun Kankara/Faskari/Sabuwa sun sami jimillar N4m, sai chairman party na mazabu su 31 kowa 20k, excos na LG su 72 kowa 20k each, shuwagabannin APC su uku na ƙananan hukumomin kowa zai sami 50k

Akwai kuma manyan exco na jiha suna da 500k, shuwagabannin jam'iyyar APC a matakin jiha N1m, hakimai kowa 50k, limamai 50k magaddai 20k masu da'awa 3m jami'an tsaro 3m, yan kwamiti 4m, yan Midiya 1.5m

Akwai kuma mutum 1500 da aka zabo daga Kankara/Faskari/Sabuwa, kowa 10k, ƴan amanar ɗan majalisar wato support interest group N5m, masu ruwa da tsaki na jam'iyyar APC N4m, executive stake holders N2m, wadanda iftilain yan bindiga ya shafa 2m, uwar gidan ɗan majalisar ya ware mata N3m don ta rarraba ma mata ƴan uwanta, masu dakko kaya don rarrabuwa N3m, yan jarida N1m, da dai sauransu

Jaridar Rana24 ta kasance yayin gudanar da taron ta kuma ruwaito buhunan shinkafa da za a raba wa shuwagabannin

Waɗanda s**a halarci taron akwai mataimakin gwamnan jihar Katsina Mai girma Faruk Lawal Jobe, sakataren jam'iyyar APC na jiha, zababbun shuwagabanin Kananan hukumomin Sabuwa Engr Sagir Tanimu, zababben shugaban karamar hukumar Kankara Hon. Kasimu Dantsoho, zababben mataimakin shugaban karamar hukumar Faskari Hon Isyaku Wada da sauran mutane da dama.
Dasauran manyan baki da dama

SANARWAR DAURIN AURE:  Amadadin Iyalan Marigayi Malam Idris Maikayan Miya Kankara  Na Farin Cikin Gayyatar Al'umma Zuwa ...
27/07/2024

SANARWAR DAURIN AURE:
Amadadin Iyalan Marigayi Malam Idris Maikayan Miya Kankara Na Farin Cikin Gayyatar Al'umma Zuwa Daurin Auren Shugaban Jaridar Rana24 Wanda Za'ayi Kamar Haka 👇

RANA:9th, August -2024
LOKACI:2:30 Na Rana
WURI:Kofar Fada Kahutu Karamar Hukumar Danja Jihar Katsina

AKaron  Farko Kungiyar FITIYANUL ISLAM Reshen Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina Tayi Taron Fadakarwar Ga 'Ya'yanta.K...
20/06/2024

AKaron Farko Kungiyar FITIYANUL ISLAM Reshen Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina Tayi Taron Fadakarwar Ga 'Ya'yanta.

Kungiyar Addinin ta FITIYANUL ISLAM ta gudanar da taron ne a ranar 19 ga watan Yuni Shekarar 2024 a Makarantar firamare Nuhu Model a garin Kankara jihar katsina.

Ayayin Taron Shugaban ta na wannan yanki Malam Tasiu Yusuf yayiwa Al'ummar malarta Wannan taron marhabin da kuma fatan Allah ya baiwa dukkanin wanda ya samu ikon Halarta da wadanda ma basu samu damaba sabili da wasu uzurirrikan rayuwa ladar sada Zumunci.

Shugaban ya kuma nuna farin ciki da godewa Manyan shehunnan Malumma da s**a halarci taron.

Kamar yadda Rana24 ta ruwaito Shugaban ya Kara da bayyana cewa Kungiyar FITIYANUL ISLAM dai na daya daga Kungiyoyin da suke was Addinin musulumci Hidindimu ayayin gudanar da wani Taron Al'umma ko ako'inama aduk lokacina da bawa Ke bukatar taimkon gaggawa.

Malam Abdullahi Na-Daura na daya daga cikin Malama da s**ayi jawabi ayayin taron inda yayi jawabi akan muhimmancin hadinkai ga dukkanin al'ummar da kuma matsalolin da rashin hadinkan Ke samarwa ga Al'umma da Kungiyoyi.

Mataimakin Babban Limamin Mabiya Darikar Tijjaniya reshen karamar hukumar Kankara Malam Ghali Abdullahi Ratibi ya fadakar da 'ya'yan Kungiyar FITIYANUL ISLAM din muhimman aikace aikacen s**a Rataya a wuyan Dan Agaji ga Addinin musulumci akoyaushe.

Hakazalika Babban Limamin Mabiya Darikar Tijjaniya Reshen Karamar Hukumar Kankara Malam Surajo Abdullahi Kankara yayi bayanai masu matukar mahimancin gaske da Kuma shwarwari ga dukkanin wanda yake gudanar da wannnan aiki.

Shehun Malamin yakumayi kira da Al'umma mu tashi TSAYE wajen ganin MUN nemi ilmi domin samun cigaba Adukkanin al'amurorin damuka sa agaba.

Limamin ya kuma kirayi mutane da musakasance masu hadin kai da rikon Amana da hakuri da fidda son zuciya Adukkanin al'amurori.

Malam Nasiru Mai-unguwa ya Gudanar Da Bayani akan waye Dan Agaji inda yakuma bayyana Wasu daga cikin Aikace aikacen da Halayen dukkanin Dan Agaji kamar haka

Yafara da bayyana Dan Agaji amatsayin Sojan Addinin musulumci,Mai juriya,Rikon Amana,Mai Gaskiya,Mai Hankali,Mai Tsafta,Mai Aikin Addini,Mai hakuri da nemana Ilmi akodayaushe.

Babban Kwamandan Dakarun matasan Agajin Na Fitiyanul Islam Reshen Karamar Hukumar Malam Auwal Salisu yayi godewa shugaban kungiyar Malam Tasiu Yusuf da dukkanin sauran Yan Kwamitin tafiyar da wannan Kungiyar duba da yadda s**a kokarta wurin shirya masu wannna taron Fadakarwa na Farko a karamar hukumar Kankara.

Wadanda s**a samu halartar Taron sun hada da Malam Magaji,Alhaji Masa'udu maikatako da sauran Al'umma da da dama.

A yau ne Babbar kotun Tarayya dake Kano zata yanke hukunci kan shari'ar da Babba Ɗanagundi ya shigar da gwamnatin jihar Kano, kan hana rushe masarautu 5

Mai shari'a Abdullahi Muhammad liman ne zai yanke hukunci a babban kotun Tarayya dake jihar Kano zata yanke hukunci kan karar da Babba Ɗanagundi ya shigar da gwamnatin jihar Kano kan hana rushe masarautun jihar.

Ko wa kuke fatan yayi nasara a wannan shari'ar?

Ku biyo mu domin jin yadda za'a toya wainar a yau.

KATSINA COLLEGE KATSINA OLD BOYS ASSOCIATION 2001/2006 GRADUATE'SƘungiyar tsofaffin ɗalibai na kwalejin Katsina watau Ka...
17/06/2024

KATSINA COLLEGE KATSINA OLD BOYS ASSOCIATION 2001/2006 GRADUATE'S

Ƙungiyar tsofaffin ɗalibai na kwalejin Katsina watau Katsina College Katsina ƴan shekarar 2006 (KCK 2006), a ƙarƙashin jagorancin shugaban kungiyar Nura Saulawa

Ana sanarwa tare da gayyatar dukkan mambobinta cewa, akwai taron sada zumunci (kamar yadda aka saba), a gobe sallah 18/06/2024.

Taron zai guda ne a harabar makarantar ta KCK, da misalin ƙarfe 4 na yamma, In shaa Allahu.

Allah Ya Bada Ikon Halarta, Amin.

Sanarwa daga jami'in huda da jama'a na kungiyar Mannir Idris Kankara

Katsina State Government Scores high marks in addressing Water Supply Challenges as CFM of Netherlands Pays Visit to the...
24/04/2024

Katsina State Government Scores high marks in addressing Water Supply Challenges as CFM of Netherlands Pays Visit to the Deputy Governor Mal. Faruk Lawal Jobe_

A team of Climate Fund Managers from Netherlands and InfraCo Nigeria have commended the Dikko Radda led administration in Katsina State for its unwavering commitment to addressing water Supply Challenges in the State.

The team gave out this commendation when its members paid a courtesy visit on the deputy Governor of Katsina State Mal Faruk Lawal Jobe in Katsina State Government House.

The Climate Fund Managers took the advantage of the visit and inspected water works, water treatment plants as well as the booster stations of Ajiwa and Zobe Dams situated in Batagarawa and Dutsinma respectively.

Earlier, the deputy Governor of the State Mal. Faruk Lawal Jobe spoke at length on the giant strides so far put in place in the area of water supply by the present APC administration in the State.

Kungiyar Tafoki Support Organisation Ta  Rabawa 'Yan Gudun Hijira Kayan Tallafi A Garin Kankara Jihar Katsina.✍️Mannir I...
30/03/2024

Kungiyar Tafoki Support Organisation Ta Rabawa 'Yan Gudun Hijira Kayan Tallafi A Garin Kankara Jihar Katsina.

✍️Mannir Idris Kankara

A ranar 28/3/2024 Kungiyar dake goyowa Dan majilisar wakilan mai wakiltar Kananan hukunomin Kankara, Faskari da Sabuwa a tarayya Hon. Shehu Dalhatu Tafoki ta bayar da tallafi ga masu gudun hijira da Kuma gajiyayyu dake shiyyar Unguwar Nasarawa cikin garin kankara.

Kayan tallafin sun hada da Buhunnan shinkafa 2 kwalayen kilin da Kuma na sabulun wanka guda goma sha biyu.

Anashi jawabin shugaban kungiyar baki daya Malam Musbahu Tukur Kogunan sarkin Pauwa,yace wannan sun yini ne amatsayin somin dabine.
Hasalima sunyi hakane maimakon suje hannu , Amma akwai abubuwan da dama dake kan hanyar zuwa.

Shugaban kungiyar TSKmatakin karamar hukumar kankara Nasir Wada Zango ya yaba da gudumuwar tallafin yakuma gargadi ga shuwagaban rabon kayan.

Malam Nazir Abdullah wanda shine jogaran wadanda kayan yayi Godiva duba da yanda aka zabi makarantar shi amatsayin inda, za'a kaddamar dactallafin.

Angudanar Da Rabon Shinkafar Da Dan Majilisar Tarayya Hon. Engr. Shehu  Dalhatu Tafoki Ya Tallafawa Al'ummar Kankara Jih...
24/03/2024

Angudanar Da Rabon Shinkafar Da Dan Majilisar Tarayya Hon. Engr. Shehu Dalhatu Tafoki Ya Tallafawa Al'ummar Kankara Jihar Katsina.

✍️Mannir Idris Kankara.

A ranar Lahadi 24/3/2024 kwamitin rabon tallafin kayan da Danmajilisar Tarayya Mai wakiltar kananan hukumomin Kankara, Faskari Da Sanuwa Hon. Shehu Dalhatu Tafoki ya bayar ga dukkanin jama'ar dayake wakilta.

Rabon Tallafin Wanda ya gudana karkashin Masu taimaka mashi na musan man afannin ayyukan majilisa Engr. Abdulbasir Gambo Kankara Da Hon. Nasir Wada Zango ya gudana kamar yadda aka tsara.

Abayanin da muke samu daga daya daga viking masu rabon Hon. Nasir Wada Zango ya bayyana wannan shinkafa da kudine da aka bayar domin tallafawa al'umma su gudanar da azumi lafiya.

Haka zalika Engr. Abdulbasir Yayi kira ga wakilan da aka baiwa sakon shinkafar da kudin suji tsoron Allah su kamanta gaskiya da sanin yakamata yayin da zasu rabawa al'ummomin su.

Bayan tabbatuwar wakilan kowace mazabun ne aka fara Kiran sunayen mazaba-mazaba ana damka wa wakilan buhunnan shikafa 20-20 tareda da mika masu N100,000 ga kowace mazaba.

Wakilin Rana24 ya tambayi wasu daga cikin wadanda s**a amfana da yanayin basu kayan inda s**a ce ba'abinda zasu ce tun daga Hon. Tafoki hat zuwa mask rabo illa s**e Allah ya Basu abinda suke nema.

Hon. Aminu Suleiman Wanda dayane daga cikin yan kwamitin rabon wadannan kayan Alheri yazo lokacin da ake bukatar shi, Yakima shedamana ba"ataba samun Danmajilisar dayayi masu makamanci irin wannan tallafi ba.

Hajiya Abule Hamza Mai baiwa shugaban karamar hukumar shawara ta fannin mata tace gaskiya irin wannan abune dake karawa shuwaganin farin jini da kwarjini a idanun al' umma da ake shugabanta.

Mazbu 7 ne wadanda aka s**ai saura Wanda aka mikawa 4 ayayin kaddamarwa.

Mazabun Da S**a karbi kayan tallafin sun hada :
Ketere, kukasheka, Zango Zabaro, Wawarkaza, Kankara A&B, da sauran su.

Bayan kammala rabawa mazabune kwamitin ya cigaba da Kungiyoyi al'umma matasa Dana sna'o'i na karamar hukumar inda wa

Dan-majilisar Dattawa Sen. Muntari Mohammed Dandutse Ya Gwagwaje Al'ummar Karamar Hukumar Kankara Da Kudade.Daga: Mannir...
21/03/2024

Dan-majilisar Dattawa Sen. Muntari Mohammed Dandutse Ya Gwagwaje Al'ummar Karamar Hukumar Kankara Da Kudade.

Daga: Mannir Idris Kankara

A yau Laraba Dan-majalisar Dattawa yankin Katsina ta kudu Sen. Muntari Mohammed Dandutse ya rabawa mutane 400 N10,000 a karamar hukumar kankara.

Hon. Abubakar Nuhu wanda shine jagoran wakilan da s**a gudanar da rabon kudaden wadanda s**a zo daga garin Funtua ya fara da bayyanawa Mutanen das**a amfana da sakon godiya daga Danmsjilisar ga Al'immar karamar hukumar ta kankara bisa nuna kauna da goyon bayan da suke nuna mashii.

Sannnan ya kuma tabbatar da akwai wasu ayyukan alheri dake tafe zuwa garin na kankara Wanda Sanatan yasamo daga tarayya daga bisani ya lissafawa al'umma yadda tsarin rabon kudin yake zuwa kaso 4.

Kason farko akwai Malamai 100, 50,50 daga Darika da Izala, Mata 100,Dattawa 100 sainkuma matasa 100 Wanda jimillar s**a kai 400 Inda kowa yasamu kunshin N10, 000 hannu da hannu.

Malam Hamisu Donawa na daya daga cikin kwamitin rabon ya bayyana sun kasa rabon shiyyoyi 11 na mazabun da karamar hukumar ta kunsa, wanda Hakan yasa mutanen wajen gari sun amfana matuka.

Daya daga cikin Malaman da s**a amfana Malam Abdulrashid ya yaba sosai da wannan tsari domin zai ragewa mutane radadin halin da ake ciki, shima Malam Isah ya godewa Danmajilisar gamida yin addu'a ta Kara samun cigaba.

Mata da Maza dama ne s**a kasance cikin farin ciki.

Nazir Isiya wanda shine mai taimakawa wajen biyan Malamai Addini ya yaba da halin dattakon da aka nuna.

Haka zalika shima Aliyu shehu dake bangaren biyan mata ya nuna godiya da yadda matan s**a nuna yayin tantacewa.

Sauran Yan kwamitin tafiyar da rabon kudin sun hada da Bature Omo, Shamsuddeen Magaji, Abdulbasir Maihoto, Danjuma Direba da Kuma Sadiq Pauwa.

Anyi rabon batare da samun Wani tarnakiba.

MACE MAI KAMAR MAZA : Mai Baiwa Gwamnan Jihar Katsina Shawarma Akan Huddatayyar Gwamnatoci Hon. Hadiza Hassan Maikudi Ta...
18/03/2024

MACE MAI KAMAR MAZA : Mai Baiwa Gwamnan Jihar Katsina Shawarma Akan Huddatayyar Gwamnatoci Hon. Hadiza Hassan Maikudi Ta Rabawa Al'umma Buhunnan Shinkafa 40.

Hon. Hadiza Hassan Maikudi wadda itace maibaiwa Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ta bayar da manyan Buhunnan shikafa masu nauyin 50 ga al'umma.

Kamar yadda wakilin mu ya tabbatas anyi rabon shinkafar ne Farfajiyar sabuwar Kasuwar Kankara wadda akafi sani da Modern Market dake kan titin Zuwa garin Dutsinma cikin garin Kankara. Shinkafar buhunna 40 masu nauyin 50 kowannanen su.

Ayayin jawabin shi Wakilin Rabon Shinkafar Engr. Abdulbasir Gambo Kankara ya bayyana "Wannan rabon shinkafa Hajiya Hadiza tayine domin tallafawa al'umma domin Allah da zummar ragewa jama'a wahalhalin alfarmar wannan wata na Ramadan.

Al'umma sun Yaba da yadda Engr. Abdulbasir ya tsaya Kai da fata tun daga farko rabo har karshen rabon wannan shinkafa .

Maitaimakawa gwamnan jihar Katsina ta fannin samar da labarai daga karamar hukumar kankara Muhammad Sale OC (Manga) wanda shima dayane daga masu rabon wannnan shinkafa Kuma daga cikin matasan da suke goyawa Hon. Hadiza Baya ya tabbatar cewa wannan kadan ne daga cikin alkairan da Hajiyar keda zummar samawa al'umma.

Wasu daga cikin wadanda s**a amfana da wannan shinkafa sun yaba da wannan taimako datayi musanman acikin irin wanna yanayi da ake ciki na rayuwa. Sun Kuma Yi addua'ar Allah ya jikan iyayenta yasa agama da duniya Lafiya.

Daga cikin wadanda s**ai aikin rabon sun hada da Malam Ibrahim Manager, Hon. Aminu Suleiman da sauransu

📷 Rana24

Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Faruk Lawal Jobe Ya Kai Ziyarar Ta'azziyar Ga Iyalan Shugaban Hukumar Tsaron C-Watch Na...
23/02/2024

Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Faruk Lawal Jobe Ya Kai Ziyarar Ta'azziyar Ga Iyalan Shugaban Hukumar Tsaron C-Watch Na Karamar Hukumar Kankara.

✍️Mannir Idris Kankara

A ranar Alhamis 22/2/2024 Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Maigirma Malam Faruk Lawal Jobe yakai Ziyarar ta'aziyya ga iyalan marigayi Malam Sanusi Hassan Kankara Shugaban hukumar Tsaro ta jihar Katsina.

Malam Sanusi ya yagamu da ajalin shi tahanyar harbin bindiga awata musayar wuta da aka gwabza da Yan ta'addar daji ajiya Laraba.

Ayayin ziyarar ta'aziyyar maigirma mataimakin Gwamnan Faruk Lawal Jobe ya jajantawa Iyalan Marigayin haka zalika yayi Addu'ar naman gafara ga mamacin da fatan Aljanna ce makomar shi.

Waɗanda s**a rufa mashi baya sun hada Kwaminshinan Ayyuka na musanman Alhaji Isah Mohammed, Shugaban gudanarwar na Babban Asibitin Garin Katsina Dr. Mohammed Umar Zango da sauran Al'umma.

Yakumayi Addu'ar Allah ya kawo tabbatacen zaman lafiya a karamar hukumar Kankara, Jihar Katsina da Najeriya baki daya.

📷 Rana24

Dan Majilasar Tarayya Mai Wakiltar Kananan Hukumomin Kankara, Faskari Da Sabuwa Ya Samawa Al'ummar Motocin Dauka Marasa ...
26/01/2024

Dan Majilasar Tarayya Mai Wakiltar Kananan
Hukumomin Kankara, Faskari Da Sabuwa Ya Samawa Al'ummar Motocin Dauka Marasa Lafiya

A ranar Alhamis 25/1/2024 Dan Majilasar , ,, mai Kananan hukumomin Kankara, Faskari Da Sabu,,wa ac tarayya Hon. Jamilu Mohammed Lion ya samar da motocin Asibiti a Kananan hukumomin dayake wakilta.

Hon. Jamilu Mohammed Lion Yana daya daga Cikin Yan Majilasar Wakilai da s**a ionsamu nasarar akarkashin Jam'iyyar PDP ga Jihar Katsina azaben gama gari daya gudana a Shekarar 2023.

Dan Majilasar Wakilan ya fara Ƙaddamar da mika motar Asibitin ne da karamar Karamar Hukumar Kankara ayau m alokacin Gudanar bikin Hon. Lion ya kuma samar da motar daukar Marasa Lafiya kirar Golf sabuwa gadagal ga Al'ummar Mazabar Garagi ta Kankara.

Haka zalika ya samar da Fayib Fayib na rijiyar tuka tuka kimanin guda 250 domin gyaran wasu rijiyoyin burtsatsen da s**a Samu matsala gamida hannuwan buga rijiyoyin burtsatsen Guda Biyu.

Hon. Jamilu lion Baitsayana Nan ba ya Samar da Buhunnan Shinkafa guda 80 dukka ga al'umma Mazabar Garagin ta Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina.

Shugaban Jam'iyyar PDP a karamar hukumar Kankara Hon. Amadu Mai kanananzir yayiwa mahalarta taro barka da zuwa sannan yayi kira ga al'ummar Mazabar Garagi da kada su biye wani ya rudesu ayayin gudanar da Zaɓen Cika gurbin da za'a ayi nan GABA.

Comr. Nuraddeen Adam Tina Yayi kira da jan kunne ga al'umma yankin Garagi dasu tsaya tsaf su zabi Jam'iyyar PDP a Zaɓen mazabar domin cigaba da sharbar romon demokariya.

Shugaban Matasan Jam'iyyar PDP a Mazabar Garagi Alhaji Nura ya Tabbatarwa Dan Majilasar Wakilai da yardar Allah zasu Tabbatarwa duniya Mazabar Garagi ta PDP ce, yakuma godewa Waɗannan abubuwan Alheri da Hon. lion yasamar ayankin su.

Danmajilisar inda Zaku Iya tunawa bayan Zaɓen da ya gudana abonkin takararshi na Jam'iyyar APC Hon. Dalhatu Tafoki ya garzaya kutun sauraran kararraki zabe domin kalubalantar yanda aka gudanar da Zaɓen Saboda rashin yin zabw awasu rumfunan Zaɓe daga

Gidauniyar Kankara Ke Gabanmu (KKG)Ta Daukewa Mutane 118 Nauyin Sayen Katin Ganin Likita Hadida Yimasu Awon Cututtuka A ...
17/01/2024

Gidauniyar Kankara Ke Gabanmu (KKG)Ta Daukewa Mutane 118 Nauyin Sayen Katin Ganin Likita Hadida Yimasu Awon Cututtuka A Garin Kankara Jihar Katsina.

Daga : Mannir Idris Kankara

A ranar Talata 16/1/2024 Gidauniyar Kankara Ke Gabanmu ta gudanar da aikin rabon katin ganin Likita Kyauta ga dukkan mara lafiyar da yaje da zummar ganin Likitan Asibitin kiwon lafiya matakin farko a Garin Kankara Jihar Katsina baki daya.

Rabon katin ganin Likitan daya gudana a Asibitin cikin garin Kankara ayau Talata majiyar Rana24 data ruwaito Waɗanda s**a amfana da rabon kati sun Kai kimanin su 118 ne.

Waɗanda S**a Amfana da wannan Shirin sun hada da mata da Maza wadanda s**a fito da daga sassan kauyuka da cikin garin karamar hukumar Kankara.

Haka zalika wannan gidauniyar ta dauki nauyin biyan Kuɗaɗen awon Cututtuka da s**a shafi kowace irin rashin lafiya awannan Ranar, irinsu awon matan masu dauke da juna Biyu, awon masassarar cizon sauro,tayfod,da sauran awon matsalolin da al'umma ke fuskanta.

Azantawar wakilin mu da wasu daga cikin matan da s**a samu amfana da wannan shirin fannin Mata masu ciki Sun Mai suna Murja Hashimu wadda tafito daga wajen garin Kankara ta bayyana matukar jin dadin dataji na daukar nauyin saymi mata katin Awo da biya mata Kuɗin Awon cikin da wannan gidauniyar tayi takumayi Addu'ar Allah ya bada abinda ake nema na Alheri ya kuma kara awo irin Waɗannan Kungiyoyin dake tsllafawa al'umma akaramar Hukumar Kankara.

Isma'il Alhassan na cikin Waɗanda s**a amfana daga bangaren Maza wanda shima ya fito ne daga garuruwan Wajen garin Kankara ya yaba da Matuka da samun wannan tallafin dauke mashi biyan Kuɗaɗen awon matsalar data sashi yazo Asibitin.

Hon. Tajjuddeen Modoji Kankara wanda shima yasamu wannan taimakon gidauniyar afannin yaron wajenshi dake fama da rashin lafiya ya godewa Shugaban wannan gidauniyar da Kuma Ma'aikatan das**a gudanar da aikin bisa tsari das**a shirya.

Shuagaban Hukumar Kiwon Lafiya Amatakin Farko na Karamar hukumar Kankara Alhaji Abdulsalam Jikamshi ya yaba Matuka da Kuma yin Addu'ar Allah yakara daukaka wannan gidauniyar da kuma Kiran da acigaba kokarin akan irin Waɗannan aiyukan ahairai ga al'umma.

Shiman shuagaban kula da alluran lokaci zuwa lokaci Kuma shugaban Kungiyar Ma'aikatan Lafiya A na karamar hukumar Kankara Alhaji Aliyu Ibrahim Ketare ya Jaddada koyon baya ga kudurorin wannan gidauniyar aduk lokacin data ke Bukatar Wani Daya shafi fannin Kiwon Lafiya.

Address

Abuja

Telephone

+2347032340606

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kankara Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kankara Post:

Share